Sashe 4
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A mota Halifa ya sanar da Dady Mijin Anty komai. Dady yace ai kaima da baka tsaya biyewa Antynka kuka yi wani gwaji ba, sai dai tunda mai aukuwa ta auku sai muce Allah ya sa hakan ya zama alkairi. Baffa yace ai maza ke kai kaya na fada masa dazu. fatanmu dai wannan din ya zama alkairi sannan tunda yace Fage ne ina da wani aboki na da mukayi harkar goro da shi a kurmi iyayen su sune suka kafa unguwar na tabbatar zan samu cikakken bayani game da yarinya da kuma iyayenta. Mijin Anty yace yawwa nima dai ina son a samu dan wani bayani game da yarinyar duk da nasan Halifa baya abu da ka. Ko tak Halifa bai furta ba
A kofar gida suka samu Sulaiman domin Halifa ya sanar dashi da suka taso.
An saka shimafida a soro inda mahaifin su Asiya ya dogaro ya fito ya zauna, ya tarbi baki cikin fara a da murna duk da yana cikin yanayin rashin lafiya mai tasanani, ya umarci Sulaiman ya sanar da mahaifin sa da daya makocin na su cewa bakin sun iso domin tun Daren jiya ya tura mahaifiyar su Asiya ta sanar da makotan zuwan bakin, bayan ya samu labari daga bakin Sulaiman.
Kamar arashi sai gashi ashe Abban su Sulaiman shine abokin Baffan su Halifa da yake maganar zai nema, dan haka Baffa ya ce shike nan kaya ya tsinke a gindin kaba ai muna tahowa yanzu a hanya nake tadin ka.
Baban su Sulaiman yace "Yace ashe ni abin duk nawa ne, dama shi Halifa nasan shi duk da bansan iyayenshi ba yaron kirkine abokin dan waje na ne, ko azumin da ya wuce ya kawo min kayan shayi. Ita kuwa yarinyar kamar diyata haka take."
Baffa yace Allah sarki, hakika Halifa dana ne wanda dan uwana Alhaji Umaru ya haifamin ai sunan mahaifinsa yaci, domin kwana uku da rasuwar mahaifinsa aka haife shi, kafin a yaye shi kuma uwar ta rasu sai rukonsa ya koma hannun wannan bawan Allahn ya nuna Mijin Anty ya ci gaba da fadin shi wannan ya auri Yayar Halifa ko wata biyu ba su yi ba, ita kuma Uwa suka hada da Halifa su shida ne Ubansu ya mutu ya bari rabon Halifa sai Uwarsu ta auri Dan uwana Alhaji Umaru shine aka samu Halifa to kunji yadda muke da Halifa. Wannan ne Ubanshi duniya bashi da sama dashi, amma yana da yan uwa su shi da suke uba daya amanar da ya rika yasa ko dukiyar Halifa da aka raba gado gaba daya muka basu, kuma har yau bamu taba jin wani korafi daga Halifa ba. Yaro kuma gashi yanzu ya zama mutum.
Mijin Anty ya yi gyara murya, yace "Gaskiya dai Halifa dana ne, domin ko Adamu dan nawa bani da shakuwa da shi kamar Halifa, duk inda ka ke neman Yaro dan albarka Halifa ya kai. Fatanmu Allah ya sa a kulla alkairi.
Baban su Asiya ya ji dadi kuma ya tabbatar musu ya ba Halifa auren Asiya ya kara da cewa ko bai kai rana ita yau da rai ba yana rokon karsu daga auren daga wannan ranar su tabbatar sun ba Halifa matar sa. Nan dai suka yi adduo'i aka shafa bayan sun bada kudi dubu dari biyu harda sadaki.
Halifa da Sulaiman suna zaune a dakalin kofar gidan su, suna kara tattaunawa game da batun daurin aure har suka yi yar gardama kan batun fati Halifa yace na saka su maido muku kudin ku, dama waccan yarinyar ce ta matsa. Sulaiman yace "To wannan ai bakaji ra ayin ta ba. " Halifa ya ce na yi hasashe a kanta bata bukata amma ka fada mata zanzo anjima da dare, inna zo na tambaye ta lokacin in tana so zan mata. Sulaiman yace to ai shike nan. Suka fito inda suka raka su har mota.
Anty tana idar da salla ta kira layin Malami na farko danjin sakamakon bincike. Ko gaisawa basu yi ba tace Malam yaya? Yace "Kedai ban taba ganin mai wutar ciki irinki ba, to gaskiya sunan da kika bada na Sadiya babu wata alaka ta aure sai dai kuma ga auren nan yana tunkarar sa wanda ba wani abu dai zai dakatar da shi."
Tace ka bincikami taurarin wadda zai aura din da kuma yadda auren zai kasance.
Yace na yi yunkurin haka amma ban iya gane komi ba, kila da a kwai sunan yarinya sai mu fahimta sunan da kika bada kuwa in har itace to sam tauraron su bai zo daya ba, kuma arzikin sa zai karye,abinci sai ya gagare shi. Sai dai ita kamar yadda na fada miki ba muga aure a kanta ba.
A gigice ta kira sauran malaman suma dai kusan bayanin daya ne sunga aurensa amma ba su ga na yarinyar ba.
Dole ta tafi gidan Hajiya Kaka dan ta watsa wuri ta yi bincike a gaban ta kuma ta dakatar mata da auren.
Tana shirin fita Mijinta yana shigo wa yace ina kuma zaki yanzu? Ta bishi da kallo daga ina kake kuma yau she ka fita? Yace " Kina can kina baccin asara na fita.,kuma daga gidan surukan Halifa muke mutanan kirki sun bashi yarinyar. "
Tace to be karba ba, nifa ba zan yarda da auren yar matsiyata ba kuma kilama baƙi ne tunda naji an ce Fage ce unguwar ta su.
Dady Yace wallahi ba matsiyata bane, yana da kyau ki gane arziki daban da kudi, sannan maganar baƙi a kano ke ki fada min tushen ku,? Ajiye batun wannan ma har akwai wani mutum a duniya wanda ba bako ba, wadanda a kayi duniyar domin su ina suke yanzu ke da har abada bazaki canza ba, ina son ki sani zaki iya duk abinda kike so, amma abinda Allah ya yi shine kadai wanda zai wanzu. " Ya wuce ya barta tsaye cike da mamakin Dady, kenan shima aikin da ta yi akan sa ya yi kasa, lallai a kwai bukatar sabunta aiki domin yana da ga cikin wanda za su bata matsala.
Hajiya Talatu da Ma u suka yi sallama Har cikin falo ba a amsaba da alamu basa nan. Ta zauna kan kujera tace da Ma u aje jakar kema ki ki zauna kila ta tafi shegen yawon malamnta yaran kuma kila suna makaranta. Tana zama Hafsi na shigowa falon tace "Oyoyo Hajiya ku ne da yamma haka, ta dubi Ma u Sis harda ke yaushe rabona dake tun bikin Bros Adamu." Ma u cikin murna tace shine ai nace nima sai nazo bikin Halifa. Hafsi tace "Ai dama bikin Uncle Halifan kuka zo sai rana ita yau fa? " Hajiya Talatu tace To zamu zo sayayya muka hada tafiyar ma yi zuwa biyu, kuma banda abinki suwaye abokan sharawar, kinga Hafsa je ni ki kawo mana abinci mun kwaso yunwa da kishi. Hafsa tace "Aiko sai dai a dafa muku taliya dan dazu yarannan suka cinye ragowar abincin rana da za su islamiya. Ta dubi Ma u zomuje mu dafa."
Hajiya Talatu tace taliya ba wata tsiya ba sai an mata gayya kije ki dafa mana Ma u tasha gajiyar mota daga Zariya zuwa kano lafiya ba ne.
Hafsi ta wuce tana kunkunan cewa nifa shiyasa na tsani matar nan wallahi ta zo gidan ku ta kama yi maka iko, masu shagen kwadayi.
Ita kuwa Hajiya Talatu ta kalli Ma u, tace tun yanzu zaki fara baza kafasitin ki a gidan nan domin ke ce zaki auri Halifa kuma shine gidan. Kinsan fa wannan gidan daya daga cikin gidajansa ne suke zaune, Haka gidan da Adam danta ya sa matarsa kafin ta sa ya sake ta. Haka kudin Halifa Adam ke juyawa a kasuwar kwari sannan shi kanshi Dadyn na su store dinshi na singa ai dukiyar Halifan ce gidajansa ance sunfi a shirin na haya domin komai da ki ke gani nashi ne. wannan ce amsar tambayar ki ta rannan, shine dalilin da yasa nake son ki auri Halifa, kuma shine dalilin da yasa ita Habiba take son sai wadda ta ga dama zata aura wa Halifa. A haka ma ta boye min wasu abubuwa fa.
Ma u ta mike ta yi rawa tace "Allah ya nuna min in auri Halifa duk sai na yi maganin kowa wallahi. " Sai sun tashi a gidan nan.
Hajiya Talatu tace abinda ya sa muka zo gidan nan da wuri saboda ki aiwatar da abubuwan da Malam na shuri ya bada, kuma ki natsu ki yi su cikin hankali kar a samu kuskure, sannan ki hada da kirsa.
Hafsi ta kira Anty a waya yafi sau Talatin amma bata daga ba, dan haka ta dafo musu farar taliya da mai da yaji. Hajiya Talatu ta ce "Lallai Hafsi mu zaki ba mai da yaji kamar yan iska?" Hafsi tace ba kayan miya ne ta wuce warta dakinta sai lokacin Anty ta kira, tana dagawa ta soma yi mata fada. "Kiran uban me ki ke min ne?!! Kinsan a tashin hankalin da nake ciki kuwa ance min masifa zata sauka min a gida ina nan ina ta fadi ta shin ganin na samu mafita ke kuma kin ishe ni da kira.
Hafsi tace " To ai masifar har ta sauka ina ta kira kin kasa daga wayata." Innalillahi wuta ce ko mutuwa aka yi? Hafsi tace kawarki ce Hajiya Talatu da Yarta Ma u suka iso da katuwar akwatin su wai sun zo bikin Halifa. " Anty ta kasa magana dan mamaki wato dama Talatu ce masifar da Hajiya Kaka mai wuri ta fara gani tana watsa wurin ta na bincike. Hafsi ta katse mata tunani da cewa kin taho ne.? ' Humm na taho lalai tauraruwa mai wutsiya ganinki ba alkairi ba....
*ƘARSHEN FREE PAGES*
*Zaɓi biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[5/24, 10:05] Ummi Tandama😇: Fage 4
A kofar gida suka samu Sulaiman domin Halifa ya sanar dashi da suka taso.
An saka shimafida a soro inda mahaifin su Asiya ya dogaro ya fito ya zauna, ya tarbi baki cikin fara a da murna duk da yana cikin yanayin rashin lafiya mai tasanani, ya umarci Sulaiman ya sanar da mahaifin sa da daya makocin na su cewa bakin sun iso domin tun Daren jiya ya tura mahaifiyar su Asiya ta sanar da makotan zuwan bakin, bayan ya samu labari daga bakin Sulaiman.
Kamar arashi sai gashi ashe Abban su Sulaiman shine abokin Baffan su Halifa da yake maganar zai nema, dan haka Baffa ya ce shike nan kaya ya tsinke a gindin kaba ai muna tahowa yanzu a hanya nake tadin ka.
Baban su Sulaiman yace "Yace ashe ni abin duk nawa ne, dama shi Halifa nasan shi duk da bansan iyayenshi ba yaron kirkine abokin dan waje na ne, ko azumin da ya wuce ya kawo min kayan shayi. Ita kuwa yarinyar kamar diyata haka take."
Baffa yace Allah sarki, hakika Halifa dana ne wanda dan uwana Alhaji Umaru ya haifamin ai sunan mahaifinsa yaci, domin kwana uku da rasuwar mahaifinsa aka haife shi, kafin a yaye shi kuma uwar ta rasu sai rukonsa ya koma hannun wannan bawan Allahn ya nuna Mijin Anty ya ci gaba da fadin shi wannan ya auri Yayar Halifa ko wata biyu ba su yi ba, ita kuma Uwa suka hada da Halifa su shida ne Ubansu ya mutu ya bari rabon Halifa sai Uwarsu ta auri Dan uwana Alhaji Umaru shine aka samu Halifa to kunji yadda muke da Halifa. Wannan ne Ubanshi duniya bashi da sama dashi, amma yana da yan uwa su shi da suke uba daya amanar da ya rika yasa ko dukiyar Halifa da aka raba gado gaba daya muka basu, kuma har yau bamu taba jin wani korafi daga Halifa ba. Yaro kuma gashi yanzu ya zama mutum.
Mijin Anty ya yi gyara murya, yace "Gaskiya dai Halifa dana ne, domin ko Adamu dan nawa bani da shakuwa da shi kamar Halifa, duk inda ka ke neman Yaro dan albarka Halifa ya kai. Fatanmu Allah ya sa a kulla alkairi.
Baban su Asiya ya ji dadi kuma ya tabbatar musu ya ba Halifa auren Asiya ya kara da cewa ko bai kai rana ita yau da rai ba yana rokon karsu daga auren daga wannan ranar su tabbatar sun ba Halifa matar sa. Nan dai suka yi adduo'i aka shafa bayan sun bada kudi dubu dari biyu harda sadaki.
Halifa da Sulaiman suna zaune a dakalin kofar gidan su, suna kara tattaunawa game da batun daurin aure har suka yi yar gardama kan batun fati Halifa yace na saka su maido muku kudin ku, dama waccan yarinyar ce ta matsa. Sulaiman yace "To wannan ai bakaji ra ayin ta ba. " Halifa ya ce na yi hasashe a kanta bata bukata amma ka fada mata zanzo anjima da dare, inna zo na tambaye ta lokacin in tana so zan mata. Sulaiman yace to ai shike nan. Suka fito inda suka raka su har mota.
Anty tana idar da salla ta kira layin Malami na farko danjin sakamakon bincike. Ko gaisawa basu yi ba tace Malam yaya? Yace "Kedai ban taba ganin mai wutar ciki irinki ba, to gaskiya sunan da kika bada na Sadiya babu wata alaka ta aure sai dai kuma ga auren nan yana tunkarar sa wanda ba wani abu dai zai dakatar da shi."
Tace ka bincikami taurarin wadda zai aura din da kuma yadda auren zai kasance.
Yace na yi yunkurin haka amma ban iya gane komi ba, kila da a kwai sunan yarinya sai mu fahimta sunan da kika bada kuwa in har itace to sam tauraron su bai zo daya ba, kuma arzikin sa zai karye,abinci sai ya gagare shi. Sai dai ita kamar yadda na fada miki ba muga aure a kanta ba.
A gigice ta kira sauran malaman suma dai kusan bayanin daya ne sunga aurensa amma ba su ga na yarinyar ba.
Dole ta tafi gidan Hajiya Kaka dan ta watsa wuri ta yi bincike a gaban ta kuma ta dakatar mata da auren.
Tana shirin fita Mijinta yana shigo wa yace ina kuma zaki yanzu? Ta bishi da kallo daga ina kake kuma yau she ka fita? Yace " Kina can kina baccin asara na fita.,kuma daga gidan surukan Halifa muke mutanan kirki sun bashi yarinyar. "
Tace to be karba ba, nifa ba zan yarda da auren yar matsiyata ba kuma kilama baƙi ne tunda naji an ce Fage ce unguwar ta su.
Dady Yace wallahi ba matsiyata bane, yana da kyau ki gane arziki daban da kudi, sannan maganar baƙi a kano ke ki fada min tushen ku,? Ajiye batun wannan ma har akwai wani mutum a duniya wanda ba bako ba, wadanda a kayi duniyar domin su ina suke yanzu ke da har abada bazaki canza ba, ina son ki sani zaki iya duk abinda kike so, amma abinda Allah ya yi shine kadai wanda zai wanzu. " Ya wuce ya barta tsaye cike da mamakin Dady, kenan shima aikin da ta yi akan sa ya yi kasa, lallai a kwai bukatar sabunta aiki domin yana da ga cikin wanda za su bata matsala.
Hajiya Talatu da Ma u suka yi sallama Har cikin falo ba a amsaba da alamu basa nan. Ta zauna kan kujera tace da Ma u aje jakar kema ki ki zauna kila ta tafi shegen yawon malamnta yaran kuma kila suna makaranta. Tana zama Hafsi na shigowa falon tace "Oyoyo Hajiya ku ne da yamma haka, ta dubi Ma u Sis harda ke yaushe rabona dake tun bikin Bros Adamu." Ma u cikin murna tace shine ai nace nima sai nazo bikin Halifa. Hafsi tace "Ai dama bikin Uncle Halifan kuka zo sai rana ita yau fa? " Hajiya Talatu tace To zamu zo sayayya muka hada tafiyar ma yi zuwa biyu, kuma banda abinki suwaye abokan sharawar, kinga Hafsa je ni ki kawo mana abinci mun kwaso yunwa da kishi. Hafsa tace "Aiko sai dai a dafa muku taliya dan dazu yarannan suka cinye ragowar abincin rana da za su islamiya. Ta dubi Ma u zomuje mu dafa."
Hajiya Talatu tace taliya ba wata tsiya ba sai an mata gayya kije ki dafa mana Ma u tasha gajiyar mota daga Zariya zuwa kano lafiya ba ne.
Hafsi ta wuce tana kunkunan cewa nifa shiyasa na tsani matar nan wallahi ta zo gidan ku ta kama yi maka iko, masu shagen kwadayi.
Ita kuwa Hajiya Talatu ta kalli Ma u, tace tun yanzu zaki fara baza kafasitin ki a gidan nan domin ke ce zaki auri Halifa kuma shine gidan. Kinsan fa wannan gidan daya daga cikin gidajansa ne suke zaune, Haka gidan da Adam danta ya sa matarsa kafin ta sa ya sake ta. Haka kudin Halifa Adam ke juyawa a kasuwar kwari sannan shi kanshi Dadyn na su store dinshi na singa ai dukiyar Halifan ce gidajansa ance sunfi a shirin na haya domin komai da ki ke gani nashi ne. wannan ce amsar tambayar ki ta rannan, shine dalilin da yasa nake son ki auri Halifa, kuma shine dalilin da yasa ita Habiba take son sai wadda ta ga dama zata aura wa Halifa. A haka ma ta boye min wasu abubuwa fa.
Ma u ta mike ta yi rawa tace "Allah ya nuna min in auri Halifa duk sai na yi maganin kowa wallahi. " Sai sun tashi a gidan nan.
Hajiya Talatu tace abinda ya sa muka zo gidan nan da wuri saboda ki aiwatar da abubuwan da Malam na shuri ya bada, kuma ki natsu ki yi su cikin hankali kar a samu kuskure, sannan ki hada da kirsa.
Hafsi ta kira Anty a waya yafi sau Talatin amma bata daga ba, dan haka ta dafo musu farar taliya da mai da yaji. Hajiya Talatu ta ce "Lallai Hafsi mu zaki ba mai da yaji kamar yan iska?" Hafsi tace ba kayan miya ne ta wuce warta dakinta sai lokacin Anty ta kira, tana dagawa ta soma yi mata fada. "Kiran uban me ki ke min ne?!! Kinsan a tashin hankalin da nake ciki kuwa ance min masifa zata sauka min a gida ina nan ina ta fadi ta shin ganin na samu mafita ke kuma kin ishe ni da kira.
Hafsi tace " To ai masifar har ta sauka ina ta kira kin kasa daga wayata." Innalillahi wuta ce ko mutuwa aka yi? Hafsi tace kawarki ce Hajiya Talatu da Yarta Ma u suka iso da katuwar akwatin su wai sun zo bikin Halifa. " Anty ta kasa magana dan mamaki wato dama Talatu ce masifar da Hajiya Kaka mai wuri ta fara gani tana watsa wurin ta na bincike. Hafsi ta katse mata tunani da cewa kin taho ne.? ' Humm na taho lalai tauraruwa mai wutsiya ganinki ba alkairi ba....
*ƘARSHEN FREE PAGES*
*Zaɓi biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[5/24, 10:05] Ummi Tandama😇: Fage 4