Sashe 60
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Lokacin karfe tara sun ta shi aiki tuni amma ba su tafi ba. Muna zuwa ya fara min faɗa bana neman shi kaza kaza na bashi hakuri domin gaskiya dai ban saba da su ba, amma mukan hadu a gida lokacin duk da za ayi wani shi ani Ina zuwa, da Ina karami ne Anty bata cika kai ni ba. Amma dana girma Dady ne yake fada min in bi yan uwana mu yi zumunci.
Sai sha biyu suka fito ya sauke ni a gida yace da sassafe in same sh office nace to.
Shine ranar da na kai sha buyun da take magana sai wani irin kallo take yi min dana dawo na shiga wanka dan ina ta jin kyan kyamin jikina tunda an sakani a sell Gurin ƴan sanda kafin muje Bamfai. Ga gajiya na ki fada mata ne dan bana son ta tada hankalinta Babu abin da ke daga min hankali sama da in ga Asiya a damuwa. Dan ina ganin yanzu ita ce komai nawa kuma na fada mata hakan gata nan Tana jina.
Abinda ya bani mamaki muna dawo wa daga Bomfai Washe garin ranar ni da lauyana wai kawai sai na ganta a dan sahu bayan Asibiti tace min zata je kuma ba hanyar bane. Har mun wuce sai na juya nace masa kamar naga wani da nake son haduwa da shi a Keke Napep Na yi haka ne kawai dan ta ga mota ta. Cikin sa a ta ganni ta sa mai keke ya bini. Na sauke lauya na a kasuwa ya dauki motar sa dama nan ya barta muka hau tawa. Ina zaune a motar ina mamaki kenan yarinyar nan bibiyata take yi tana zargina. To halin da nake ciki bana bukatar wani tashin hankali a gida domin mutumin da na buga har lokacin baya gane kowa duk da ya farka.
Sannan nima na shigar da ƙara akan abinda ya yi wa yaran nan bani da ishshen lokacin da zan zauna ko abinci in ci, kasuwa ma bana samun zama sam daga gurin yansanda zuwa Asibiti kuma ni na bada jini da aka yi wa Abba aiki amma matar nan tana ta zargina har da cewa ina tona asirinta a gurin matan da nake nema . Ta tashi dan hauka ta tafi gidan su Fati me aikin ta dan wulakanta kai da zubar da aji . Hajjo ta kira ni ta faɗa min har lambar da ta sa aka turo mata duk babu abinda ban sani ba. Na shanye to wai kuma jiya na shigo gida Ina waya zan kira Barista ka wai kiran ya tafi ashe wayar Bilkisu na kira yarinyar da zan aura a da, gudun kar ya zama kamar na wulaƙanta ta sai na tsaya muna gaisawa sannan na shigo gida da kwarin ta kai tsaye tunda nasan bata nan kuma Ina da kwarin gwiwar cewa yanzu suna tare da Inna taji komai dan haka na shigo Ina wayata kai tsaye, ganinta zaune yasa naji na dan kadu domin dama ga halin da nake ciki game da ita kuma gashi taji ina waya. Yadda na tsargu shine ya bata damar fada min magana wai ina kai mata Hotel. Raina ya sake ɓaci sakamakon tuna batun cikin fushi yace aure baya yi wuwa da zargi dan haka na fada mata wallahi ta fara dusashewa daga raina ta zabi abinda take so wallahi zan mata in gaba ɗaya take son sakinta zan bata, sai inje in yi sharholiya ta yadda nake so,.
Ya mike bayan ya kai ƙarshen bayanin shi, Inna wadda duk jikinta ya yi sanyi tace to aiba tafiya zaka yi ba,, ka tsaya a warware maganar . Sulaiman ya ce Inna kiyi hakuri zamu dawo wallahi dama da kyar na sha kansa ya zo. Shima ya fice. Asiya wadda kunya da bakin ciki suka hana ta dago kai sai da ta tabbata Halifa ya fice. Ta mike tsaye tana fadin Innalillahi wa inna ilaihirraji un.
Inna wallahi nayi kuskure na zargi yaya Halifa cike da jahilci. Inna tace Nan fa shine ya tsaya mana kare wa ma wannan gidan shi ya saya mana yace mu bar unguwar saboda abinda aka yi wa Abba. Ya kawo kayan abinci ya jibge mana hatta Sadiya yace ta daina zuwa aikin nan dan kuɗin makarantar yara zai biya musu dan dai matar da ta ke yi wa aikin taje Umara ne amma da ta dawo zata daina zuwa.
Sadiya tace to wai ke Asiya duk wa ya zuga ki kika dinga wannan shirme babu lissafi? Dan gaskiya da ba haka ki ke ba, wallahi gaba ɗaya duk kin sa kunya ta rife ni, na kasa magana. Asiya tace sharrin zuciya ne wallahi sai ta yi ta raya min ni kuma inta hasashe cewa fa ga shi can kuma bugu da kari Fati me aikina da ta fada min cewa yace na gudo ne. Asiya tace aikin banza kila ma jinku ta yi ba kince a gidan sauke yini ba? A kwai wanda ya kai masu aiki gulma da bin diddigin masu gida ne aka fada miki? Gidan aikina gashi nan ina gani a gurin sauran masu aikin har labe suna yi. Asiya tace Ita wannan shegiyar zata iya aikata wa . Inna tace Ni na ma rasa ta inda za bullo wa lamarin shi yana nan yana kare miki mutunci iyaye da kanin ki ya kuma kasa faɗa miki dan kar hakalin ki ya ta shi ke kuma kina can ki nai masa cin zarafi.
Asiya tace to wai ni ku fada min ta inada zan fara. Sadiya tace ki kira shi a waya ki ba Inna ta bashi haƙuri ko kuwa? Asiya tace dan yi shiru bari in gwada bashi hakurin ni da kai na mugani.
Asiya ta firgita da ganin yadda ta yi masa kira goma sha biyu bai ɗaga ba. Tace lamari fa ya baci ta kira Sulaiman yace ai ko ɗazu kafin na fito har ya tafi kuma nima bai daga kirana ba. Yace Asiya kema baki kyauta ba abin fa da ciwo ya zama iyalinka kuma basu yarda da kai ba. Asiya tace Na yarda Yaya Sulaiman na yi laifi hakuri zan bashi. Yace ki masa Message sai ki jira zuwa gobe ya huce. Bata da zaɓin da ya wuce hakan.
Sai dai wasa wasa yau sati daya ba wani ci gaba ta masa sako ya fi dari amma ba amsa kira kuwa da ya gaji ya saka layin a DNA.
Har kasuwa Sulaiman ya je yaran shagon suka ce ya yi tafiya.
Hakurin Asiya ya kare ga fargaba kar fa Halifa yace zai sake ta.
Ta shiga yi wa Inna kuka har ta ba Inna haushi Tace zata saba mata in dai bata nutsu ba wani yace ta yi laifin tunda ta san halinsa. Sadiya dai sai lallashi Su tufka wannan shawara su kwance.
Daga karshe ta sake kiran Anty K mashi bata boye mata komai ba. K mashi tace “Abinda ya faru dai ya riga ya faru, yanzu shawara daya ce waye kika sani guda daya wanda ba zai musa maganar sa ba? Asiya tace sai dai Baffan shi, K mashi tace to ki sanar da Inna cewa zaki je gurin Baffa din domin ya bashi hakuri ita rayuwa akwai yanayin da baka tsayawa ga mace musamman miji ya
diga miki alama ta cewa kin fara fita ransa har kuma ya maimaita hakan a gaban mahaifiyar ki. To ki aje wani batun wani aji ki sunkuyar da kai .
Asiya tace “Yanzu ma kuwa zan tashi in kama hanya . Ta sanar da Inna komai Inna tace Ni da zaki bi tawa ki jira shi ya huce ya kawo kanshi hakan akwai daraja kuwa? Asiya tace “Inna Ni nasan halin kaya na, Yaya da ki ke gani sai ya shafe labarina daga yadda ya bar wadda suka dade suna soyayya ya aure ni ya ishe ni misali.
Inna tace To ku tafi tare da Sadiya. Kuma dan Allah kar ki kuma tafiya ba da izini na ba.
Asiya tace kar ki damu Inna bazan sake yin wannan kuskuren ba.
Asiya da Sadiya suna zaune a gaban Baffa ta sanar da shi ko ita din wacece dan ba zai gane ta ba Baffa ya sha Mamaki wai dama an ganta . Tace ita dama gidansa ta tafi, ta zayyana wa Baffa komai . Baffa ya yi mata faɗa sosai sannan ya dauki waya ya kira Halifa yace Yace duk inda yake ya zo yanzun nan yana neman sa.
Halifa bai kawo Asiya cikin dalilin kiran ba, domin ai ba su san anganta ba. Sai dai abin mamaki yana shiga Falon Baffa sai ya ya ga Asiya zaune ita da Sadiya shi kuma yana rungume da jariri yana ta yi musu nasiha.
Sai sha biyu suka fito ya sauke ni a gida yace da sassafe in same sh office nace to.
Shine ranar da na kai sha buyun da take magana sai wani irin kallo take yi min dana dawo na shiga wanka dan ina ta jin kyan kyamin jikina tunda an sakani a sell Gurin ƴan sanda kafin muje Bamfai. Ga gajiya na ki fada mata ne dan bana son ta tada hankalinta Babu abin da ke daga min hankali sama da in ga Asiya a damuwa. Dan ina ganin yanzu ita ce komai nawa kuma na fada mata hakan gata nan Tana jina.
Abinda ya bani mamaki muna dawo wa daga Bomfai Washe garin ranar ni da lauyana wai kawai sai na ganta a dan sahu bayan Asibiti tace min zata je kuma ba hanyar bane. Har mun wuce sai na juya nace masa kamar naga wani da nake son haduwa da shi a Keke Napep Na yi haka ne kawai dan ta ga mota ta. Cikin sa a ta ganni ta sa mai keke ya bini. Na sauke lauya na a kasuwa ya dauki motar sa dama nan ya barta muka hau tawa. Ina zaune a motar ina mamaki kenan yarinyar nan bibiyata take yi tana zargina. To halin da nake ciki bana bukatar wani tashin hankali a gida domin mutumin da na buga har lokacin baya gane kowa duk da ya farka.
Sannan nima na shigar da ƙara akan abinda ya yi wa yaran nan bani da ishshen lokacin da zan zauna ko abinci in ci, kasuwa ma bana samun zama sam daga gurin yansanda zuwa Asibiti kuma ni na bada jini da aka yi wa Abba aiki amma matar nan tana ta zargina har da cewa ina tona asirinta a gurin matan da nake nema . Ta tashi dan hauka ta tafi gidan su Fati me aikin ta dan wulakanta kai da zubar da aji . Hajjo ta kira ni ta faɗa min har lambar da ta sa aka turo mata duk babu abinda ban sani ba. Na shanye to wai kuma jiya na shigo gida Ina waya zan kira Barista ka wai kiran ya tafi ashe wayar Bilkisu na kira yarinyar da zan aura a da, gudun kar ya zama kamar na wulaƙanta ta sai na tsaya muna gaisawa sannan na shigo gida da kwarin ta kai tsaye tunda nasan bata nan kuma Ina da kwarin gwiwar cewa yanzu suna tare da Inna taji komai dan haka na shigo Ina wayata kai tsaye, ganinta zaune yasa naji na dan kadu domin dama ga halin da nake ciki game da ita kuma gashi taji ina waya. Yadda na tsargu shine ya bata damar fada min magana wai ina kai mata Hotel. Raina ya sake ɓaci sakamakon tuna batun cikin fushi yace aure baya yi wuwa da zargi dan haka na fada mata wallahi ta fara dusashewa daga raina ta zabi abinda take so wallahi zan mata in gaba ɗaya take son sakinta zan bata, sai inje in yi sharholiya ta yadda nake so,.
Ya mike bayan ya kai ƙarshen bayanin shi, Inna wadda duk jikinta ya yi sanyi tace to aiba tafiya zaka yi ba,, ka tsaya a warware maganar . Sulaiman ya ce Inna kiyi hakuri zamu dawo wallahi dama da kyar na sha kansa ya zo. Shima ya fice. Asiya wadda kunya da bakin ciki suka hana ta dago kai sai da ta tabbata Halifa ya fice. Ta mike tsaye tana fadin Innalillahi wa inna ilaihirraji un.
Inna wallahi nayi kuskure na zargi yaya Halifa cike da jahilci. Inna tace Nan fa shine ya tsaya mana kare wa ma wannan gidan shi ya saya mana yace mu bar unguwar saboda abinda aka yi wa Abba. Ya kawo kayan abinci ya jibge mana hatta Sadiya yace ta daina zuwa aikin nan dan kuɗin makarantar yara zai biya musu dan dai matar da ta ke yi wa aikin taje Umara ne amma da ta dawo zata daina zuwa.
Sadiya tace to wai ke Asiya duk wa ya zuga ki kika dinga wannan shirme babu lissafi? Dan gaskiya da ba haka ki ke ba, wallahi gaba ɗaya duk kin sa kunya ta rife ni, na kasa magana. Asiya tace sharrin zuciya ne wallahi sai ta yi ta raya min ni kuma inta hasashe cewa fa ga shi can kuma bugu da kari Fati me aikina da ta fada min cewa yace na gudo ne. Asiya tace aikin banza kila ma jinku ta yi ba kince a gidan sauke yini ba? A kwai wanda ya kai masu aiki gulma da bin diddigin masu gida ne aka fada miki? Gidan aikina gashi nan ina gani a gurin sauran masu aikin har labe suna yi. Asiya tace Ita wannan shegiyar zata iya aikata wa . Inna tace Ni na ma rasa ta inda za bullo wa lamarin shi yana nan yana kare miki mutunci iyaye da kanin ki ya kuma kasa faɗa miki dan kar hakalin ki ya ta shi ke kuma kina can ki nai masa cin zarafi.
Asiya tace to wai ni ku fada min ta inada zan fara. Sadiya tace ki kira shi a waya ki ba Inna ta bashi haƙuri ko kuwa? Asiya tace dan yi shiru bari in gwada bashi hakurin ni da kai na mugani.
Asiya ta firgita da ganin yadda ta yi masa kira goma sha biyu bai ɗaga ba. Tace lamari fa ya baci ta kira Sulaiman yace ai ko ɗazu kafin na fito har ya tafi kuma nima bai daga kirana ba. Yace Asiya kema baki kyauta ba abin fa da ciwo ya zama iyalinka kuma basu yarda da kai ba. Asiya tace Na yarda Yaya Sulaiman na yi laifi hakuri zan bashi. Yace ki masa Message sai ki jira zuwa gobe ya huce. Bata da zaɓin da ya wuce hakan.
Sai dai wasa wasa yau sati daya ba wani ci gaba ta masa sako ya fi dari amma ba amsa kira kuwa da ya gaji ya saka layin a DNA.
Har kasuwa Sulaiman ya je yaran shagon suka ce ya yi tafiya.
Hakurin Asiya ya kare ga fargaba kar fa Halifa yace zai sake ta.
Ta shiga yi wa Inna kuka har ta ba Inna haushi Tace zata saba mata in dai bata nutsu ba wani yace ta yi laifin tunda ta san halinsa. Sadiya dai sai lallashi Su tufka wannan shawara su kwance.
Daga karshe ta sake kiran Anty K mashi bata boye mata komai ba. K mashi tace “Abinda ya faru dai ya riga ya faru, yanzu shawara daya ce waye kika sani guda daya wanda ba zai musa maganar sa ba? Asiya tace sai dai Baffan shi, K mashi tace to ki sanar da Inna cewa zaki je gurin Baffa din domin ya bashi hakuri ita rayuwa akwai yanayin da baka tsayawa ga mace musamman miji ya
diga miki alama ta cewa kin fara fita ransa har kuma ya maimaita hakan a gaban mahaifiyar ki. To ki aje wani batun wani aji ki sunkuyar da kai .
Asiya tace “Yanzu ma kuwa zan tashi in kama hanya . Ta sanar da Inna komai Inna tace Ni da zaki bi tawa ki jira shi ya huce ya kawo kanshi hakan akwai daraja kuwa? Asiya tace “Inna Ni nasan halin kaya na, Yaya da ki ke gani sai ya shafe labarina daga yadda ya bar wadda suka dade suna soyayya ya aure ni ya ishe ni misali.
Inna tace To ku tafi tare da Sadiya. Kuma dan Allah kar ki kuma tafiya ba da izini na ba.
Asiya tace kar ki damu Inna bazan sake yin wannan kuskuren ba.
Asiya da Sadiya suna zaune a gaban Baffa ta sanar da shi ko ita din wacece dan ba zai gane ta ba Baffa ya sha Mamaki wai dama an ganta . Tace ita dama gidansa ta tafi, ta zayyana wa Baffa komai . Baffa ya yi mata faɗa sosai sannan ya dauki waya ya kira Halifa yace Yace duk inda yake ya zo yanzun nan yana neman sa.
Halifa bai kawo Asiya cikin dalilin kiran ba, domin ai ba su san anganta ba. Sai dai abin mamaki yana shiga Falon Baffa sai ya ya ga Asiya zaune ita da Sadiya shi kuma yana rungume da jariri yana ta yi musu nasiha.