Sashe 50
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya yi murmushin takaici, yace Dady ka share min tantamata da kuma mamakina akan abubuwa da Anty ta yi min ko take kan yi min zan tafi amma ka sani nima ina goyon bayan ka dawo da matarka nan kuma suma yaranta zan dauki nauyin karatun su kamar dai na yan uwansu.
Sannan nima zan kira irin zaman nan nan da lokaci kadan. Anty tace "Halifa zo kaji karfa ya hada mu duk abin da yake fada son zuciyar sa ce kawai.
Halifa yana tuki yana tuna zantukan Dady ba shakka bai yi kuskuren ba wa Dady gida ba, duk da tarihin da Dady ya bashi ya dame shi amma fa babu kamar waccan kalma da Anty ta furta ta cewa gara ace ga Dady can an kama shi da wata yana zina da ace ya kara aure, duk mata haka suke? Wata rana Asiya zata iya fada masa haka dama yanzu ma ta nuna kishin ta mai karfi. Cikin wannan tunanin ya iso gida, Asiya tana kichin ta tasa Fati suna yin miyar nan margi special. Bata san ya shigo ba sai da suka gama ta nufi daki dan ta yi wanka sai kawai ta ga mutum kwance. Da sauri ta nufe shi ta zauna bakin gado ta kamo hannunshi ta saka a cikin nata tana tambayar shi, Yaya lafiya dai? Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya maida kallon shi gare ta yana tunanin abinda zai faru gaba.
Tsoro ya kama Asiya tace Yaya kamin magana baka da lafiya ne? Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya tashi zaune, ya "Asiya zan tambaye ki wani abu." Asiya ta danji dim domin duk lokacin da zai yi magana yace Asiya ba shakka magana ce mai muhimmanci.
Cike da tsoro da kasala tace to Yaya ina jinka. Yace Zan baki zabi daya a cikin biyu. Gabanta ya fadi ba dai zai ce ta tafi gida ba, ko maganar saki. "Kina ji?" Ya katse ta. In inajinka Yaya ta fada da in'ina, Yace Nan gaba in Allah ya amince ina son kara aure,in kuma ba haka ba to zaki lamun ce min in nemi mata banza a waje kinga ba ruwanki da kawo miki kishiya."
Asiya ta mike tsaye da sauri tana fadin Au'zubillahi minna shshaidani rajim. Allah karka kama shi da wani laifi mai kama da wannan. Allah kar ka sa mala'iku su amsa wanna magana.Ta kalle shi, Yaya daga ina ka ke? Taje ta kama fuskarshi ta kai hancin ta gurin bakinshi ta shaka. Tace Yaya duk da bansan wari kayan maye ba banji alamun kasha wani abu ba, nasan baka sha kuma ba su ka shaba. Menene ya kawo wannan tunanin a zuciyar ka? Me zai sa ka ce zaka nemi mata a waje. Ta fashe da kuka, ta durkusa a gaban shi Yaya wallahi na yarda ka sake ni ka auri mata hudu in baka bukata ta, da ace ga uban dana yana bin matan banza gara a ce ka auri mata hudu. In har maganar da na yi maka ce dana ce bana son ka kara aure ta kawo wannan tunanin Yaya ka yafe min wallahi bazan sake ba. Ka yi auren ka ko yanzu ka ke so Allah ne ya baka dama kar ka damu da kishina. Ta fashe da sabon kuka. Halifa ya tashi cike da tausayin Asiya ya kamota ya rungumeta yace ki daina kuka wani abu ne na gani ya rudani dan Allah ki yafe min Baby. Asiya tace Yaya Allah ya yafe maka da ka ayyana kan ka da aikata zina,dan Allah kar ka sake, Ina son ka min alkawarin yadda baka aikata zina ba kana samartaka yanzu ma baza ka yi ba. Yace na miki alkawari Baby.
Suka zauna tace Yaya ina ga dai da zarar jini ya dauke min zan dawo maka rashin samun kulawata sosai ne ya saka ka soma saka da mugun zare ko?
Yace " Anty ce ta firgitani naga cewa idan har Anty da girmanta a matsayin ta na uwa kuma kaka zata yi fatan da Dady ya yi aure gara a kamashi da mace to ke kuma da kike karama sai Yaya kenan? Asiya ta zuba ido cike da mamaki tana kallon Halifa kamar shine ya fada, tace amma kaji da kyau kuwa? Halifa yace Ba ni kadai bane bare ince kunne na ya yi tsatsa. Asiya tace Allah ya kyauta abin dai ba dadin ji.
Ya bata labarin duk abinda ya faru. Ta sha mamakin Dady ya yi aure ya boye ma matarshi tsawon shekaru. Ga Maman Nihal ita ma Bros ya boye ta. Ta kalli Halifa Yaya Dan Allah zan nemi wata alfarma in zaka yi aure wallahi ba zan taba hanawa ba, kawai ka fada min karka damu da kishi na, kar ka boye mace saboda ni. Ta kama hannuwan shi ta matse cikin nata. Ni da kai wallahi abu daya ne. Ya sunkuyar da kai cikin rashin Walwala Baby sai dai kar a kuma ni ma dai na boye mace kuma har ta haihu. Asiya ta zabura ta mike tana fadin Innalillahi wa Inna ilaihirraji un. Tun wane lokacin ka yi haka? Ya Kalli yadda ta firgita ya kamo hannun ta yace ke ce ai wadda na boye, ya saki dariya yanzu wa yasan muna tare? Ta sauke ajiyar zuciya Yaya ka tsorata ni walllahi dan Allah kar ka boye min komai. Ya kamota ya zaunar da ita a cinyar sa. Asiya wallahi na rantse miki da Allah a yanzu gani nake bani da wani wanda ya kai ki zama jini na, ke ce komai nawa, na baki amanar kaina Asiya wallahi da gaske nake yi, ki sani komai zan yi ki hanani zan hanu amma banda abinda ya shiga hurumin Allah.
Asiya ta rungume shi, nima haka Yaya kuma insha Allah bazaka taba yin danasanin bani amanar kanka ba.
Sulaiman ya taso yaro da yamma zuwa gaban Inna, ta tabbatar masa da cewa shine ya kawo takardar a gaban Inna ya tambayi yaron yaron yace 'Ni dai wasu mata ne suka bani suka ce ince inji ko wa ma nace da nazo na manta sunan har suka bani dari biyar. Sulaiman yace To kinji dai Inna da kunnan ki, wallah sharri ne kawai, Inna tace kayya to yanzu ina ma Asiyar take,ta fada cikin yanayin tausayi. Sulaiman yace Allah zai dawo da ita lafiya kuma wallahi mijinta bai zauna ba, yana can yana neman matar sa.
Sulaiman ya kira Halifa ya fada masa halin da a ke ciki Inna ta fahimta fata dai Allah ya bayyana Asiya. Halifa ya ji dadi kuma ya yi godiya. Yace dan Allah zai neme shi akan ya kawo Inna akwai zama da za ayi Sulaiman yace Insha Allahu ba damuwa.
Kafin Asiya ta yi arba'in sai da ta tabbatar ta koyi duk wani salon girki da Fati ke yi,ta kau da kai daga duk wani kini bibi da Fati ke yi idan taga Halifa.
Ta kuma sa ta yawo da hijabi a gidan da ta kula takan fizgi hankalin Halifa in tana kai kawo.
Bangare Hajjo ma Asiya ta ko yi wankan yaro dan haka bata da matsala da wannan.
Ranar da zata cika arba'in ta sa su Hajjo suka zo mata da me lalle aka zuba shi ta yi mata kitso gurin mai kitso ta sai wasu magunguna duk da dai ta yi amfani da abubuwan da ta samu a soshiyal midiya na gyaran jiki ga masu jego. Da yamma ta zuba wanka ta yi kyau kamar amarya. Halifa ya yi ta kallon ta yana mamakin bayan fitar shi duk ta yi wannan gyaran kasa cin abincin ya yi dan doki, ya shiga nuna mata zalamar shi . Da safe ya tashi cikin yanayi mai dadi da farin ciki ya laluba gefe bata nan. Kichin ya same ta tana hada abin kari. Yace zomuje ki bari su Fati su yi. Ta kalle shi, ai na sallami su Fati tun jiya. Gaban shi ya fadi, cikin in'ina yace "To me suka yi miki? " Ta yi murmushi babu komai, aikin su ya kare tunda na yi arba'in. Ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin ok na fahimta. Amma ai baza ki iya kula da gidan nan ba,ga yaro tace Zan gwada in na kasa sai mu samu mafita.
Sai dai yadda Halifa ya yi ne ya sa taji kamar akwai wani abu. Ya fita da sauri bata bi bayan shi ba sai da ta dauki tiren abin kari ta fita. Baya falo kamar yadda ta zata dan haka sai ta gama hada komai sannan ta nufi dakin, karaf ya aje wayarsa da sauri bayan ta murda kofar ta shigo, ya kama fadin kin kin gama hada break fast din ne da wanka zan yi, Asiya ta yi saurin kauda shakkun ta tace yanzu muje in maka wanka sai ka zo mu karya din ko? Yace muje dai mu fara karyawa bari in yi brush. Ya kuma daukar wayar sa ya saka aljihun jallabiyar sa. Murmushin takaici Asiya ta yi sannan tace ina jiran ka a can. Ta kalli danta yana bacci a gadon sa sannan ta wuce.
*Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[12/4, 12:12] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt
Inna bata gamsu da abinda Sulaiman ya fada ba,dan haka ta taka da kanta ta je har gidan su yaron ta same shi ta fadawa uwarsa komai, tace ita tana son yaro ya fadi gaskiya game da abinda ya sani na aiko shi da aka yi,kamar yadda ya fada haka ya maimaita Inna tace wa uwar dan Allah su lallaba mata shi ko zai fadi gaskiya. Ta kama hanya ta tafi.
Yaro kuwa ya yi ta rantsuwa akan cewar iyakacin Gaskiyar shi kenan dan haka suka shedawa Inna halin da ake ciki Inna dai zuciyarta ta kasa yarda amma bata da wani zabin ko tunanin face ita dai aga ƴarta.
Sannan nima zan kira irin zaman nan nan da lokaci kadan. Anty tace "Halifa zo kaji karfa ya hada mu duk abin da yake fada son zuciyar sa ce kawai.
Halifa yana tuki yana tuna zantukan Dady ba shakka bai yi kuskuren ba wa Dady gida ba, duk da tarihin da Dady ya bashi ya dame shi amma fa babu kamar waccan kalma da Anty ta furta ta cewa gara ace ga Dady can an kama shi da wata yana zina da ace ya kara aure, duk mata haka suke? Wata rana Asiya zata iya fada masa haka dama yanzu ma ta nuna kishin ta mai karfi. Cikin wannan tunanin ya iso gida, Asiya tana kichin ta tasa Fati suna yin miyar nan margi special. Bata san ya shigo ba sai da suka gama ta nufi daki dan ta yi wanka sai kawai ta ga mutum kwance. Da sauri ta nufe shi ta zauna bakin gado ta kamo hannunshi ta saka a cikin nata tana tambayar shi, Yaya lafiya dai? Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya maida kallon shi gare ta yana tunanin abinda zai faru gaba.
Tsoro ya kama Asiya tace Yaya kamin magana baka da lafiya ne? Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya tashi zaune, ya "Asiya zan tambaye ki wani abu." Asiya ta danji dim domin duk lokacin da zai yi magana yace Asiya ba shakka magana ce mai muhimmanci.
Cike da tsoro da kasala tace to Yaya ina jinka. Yace Zan baki zabi daya a cikin biyu. Gabanta ya fadi ba dai zai ce ta tafi gida ba, ko maganar saki. "Kina ji?" Ya katse ta. In inajinka Yaya ta fada da in'ina, Yace Nan gaba in Allah ya amince ina son kara aure,in kuma ba haka ba to zaki lamun ce min in nemi mata banza a waje kinga ba ruwanki da kawo miki kishiya."
Asiya ta mike tsaye da sauri tana fadin Au'zubillahi minna shshaidani rajim. Allah karka kama shi da wani laifi mai kama da wannan. Allah kar ka sa mala'iku su amsa wanna magana.Ta kalle shi, Yaya daga ina ka ke? Taje ta kama fuskarshi ta kai hancin ta gurin bakinshi ta shaka. Tace Yaya duk da bansan wari kayan maye ba banji alamun kasha wani abu ba, nasan baka sha kuma ba su ka shaba. Menene ya kawo wannan tunanin a zuciyar ka? Me zai sa ka ce zaka nemi mata a waje. Ta fashe da kuka, ta durkusa a gaban shi Yaya wallahi na yarda ka sake ni ka auri mata hudu in baka bukata ta, da ace ga uban dana yana bin matan banza gara a ce ka auri mata hudu. In har maganar da na yi maka ce dana ce bana son ka kara aure ta kawo wannan tunanin Yaya ka yafe min wallahi bazan sake ba. Ka yi auren ka ko yanzu ka ke so Allah ne ya baka dama kar ka damu da kishina. Ta fashe da sabon kuka. Halifa ya tashi cike da tausayin Asiya ya kamota ya rungumeta yace ki daina kuka wani abu ne na gani ya rudani dan Allah ki yafe min Baby. Asiya tace Yaya Allah ya yafe maka da ka ayyana kan ka da aikata zina,dan Allah kar ka sake, Ina son ka min alkawarin yadda baka aikata zina ba kana samartaka yanzu ma baza ka yi ba. Yace na miki alkawari Baby.
Suka zauna tace Yaya ina ga dai da zarar jini ya dauke min zan dawo maka rashin samun kulawata sosai ne ya saka ka soma saka da mugun zare ko?
Yace " Anty ce ta firgitani naga cewa idan har Anty da girmanta a matsayin ta na uwa kuma kaka zata yi fatan da Dady ya yi aure gara a kamashi da mace to ke kuma da kike karama sai Yaya kenan? Asiya ta zuba ido cike da mamaki tana kallon Halifa kamar shine ya fada, tace amma kaji da kyau kuwa? Halifa yace Ba ni kadai bane bare ince kunne na ya yi tsatsa. Asiya tace Allah ya kyauta abin dai ba dadin ji.
Ya bata labarin duk abinda ya faru. Ta sha mamakin Dady ya yi aure ya boye ma matarshi tsawon shekaru. Ga Maman Nihal ita ma Bros ya boye ta. Ta kalli Halifa Yaya Dan Allah zan nemi wata alfarma in zaka yi aure wallahi ba zan taba hanawa ba, kawai ka fada min karka damu da kishi na, kar ka boye mace saboda ni. Ta kama hannuwan shi ta matse cikin nata. Ni da kai wallahi abu daya ne. Ya sunkuyar da kai cikin rashin Walwala Baby sai dai kar a kuma ni ma dai na boye mace kuma har ta haihu. Asiya ta zabura ta mike tana fadin Innalillahi wa Inna ilaihirraji un. Tun wane lokacin ka yi haka? Ya Kalli yadda ta firgita ya kamo hannun ta yace ke ce ai wadda na boye, ya saki dariya yanzu wa yasan muna tare? Ta sauke ajiyar zuciya Yaya ka tsorata ni walllahi dan Allah kar ka boye min komai. Ya kamota ya zaunar da ita a cinyar sa. Asiya wallahi na rantse miki da Allah a yanzu gani nake bani da wani wanda ya kai ki zama jini na, ke ce komai nawa, na baki amanar kaina Asiya wallahi da gaske nake yi, ki sani komai zan yi ki hanani zan hanu amma banda abinda ya shiga hurumin Allah.
Asiya ta rungume shi, nima haka Yaya kuma insha Allah bazaka taba yin danasanin bani amanar kanka ba.
Sulaiman ya taso yaro da yamma zuwa gaban Inna, ta tabbatar masa da cewa shine ya kawo takardar a gaban Inna ya tambayi yaron yaron yace 'Ni dai wasu mata ne suka bani suka ce ince inji ko wa ma nace da nazo na manta sunan har suka bani dari biyar. Sulaiman yace To kinji dai Inna da kunnan ki, wallah sharri ne kawai, Inna tace kayya to yanzu ina ma Asiyar take,ta fada cikin yanayin tausayi. Sulaiman yace Allah zai dawo da ita lafiya kuma wallahi mijinta bai zauna ba, yana can yana neman matar sa.
Sulaiman ya kira Halifa ya fada masa halin da a ke ciki Inna ta fahimta fata dai Allah ya bayyana Asiya. Halifa ya ji dadi kuma ya yi godiya. Yace dan Allah zai neme shi akan ya kawo Inna akwai zama da za ayi Sulaiman yace Insha Allahu ba damuwa.
Kafin Asiya ta yi arba'in sai da ta tabbatar ta koyi duk wani salon girki da Fati ke yi,ta kau da kai daga duk wani kini bibi da Fati ke yi idan taga Halifa.
Ta kuma sa ta yawo da hijabi a gidan da ta kula takan fizgi hankalin Halifa in tana kai kawo.
Bangare Hajjo ma Asiya ta ko yi wankan yaro dan haka bata da matsala da wannan.
Ranar da zata cika arba'in ta sa su Hajjo suka zo mata da me lalle aka zuba shi ta yi mata kitso gurin mai kitso ta sai wasu magunguna duk da dai ta yi amfani da abubuwan da ta samu a soshiyal midiya na gyaran jiki ga masu jego. Da yamma ta zuba wanka ta yi kyau kamar amarya. Halifa ya yi ta kallon ta yana mamakin bayan fitar shi duk ta yi wannan gyaran kasa cin abincin ya yi dan doki, ya shiga nuna mata zalamar shi . Da safe ya tashi cikin yanayi mai dadi da farin ciki ya laluba gefe bata nan. Kichin ya same ta tana hada abin kari. Yace zomuje ki bari su Fati su yi. Ta kalle shi, ai na sallami su Fati tun jiya. Gaban shi ya fadi, cikin in'ina yace "To me suka yi miki? " Ta yi murmushi babu komai, aikin su ya kare tunda na yi arba'in. Ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin ok na fahimta. Amma ai baza ki iya kula da gidan nan ba,ga yaro tace Zan gwada in na kasa sai mu samu mafita.
Sai dai yadda Halifa ya yi ne ya sa taji kamar akwai wani abu. Ya fita da sauri bata bi bayan shi ba sai da ta dauki tiren abin kari ta fita. Baya falo kamar yadda ta zata dan haka sai ta gama hada komai sannan ta nufi dakin, karaf ya aje wayarsa da sauri bayan ta murda kofar ta shigo, ya kama fadin kin kin gama hada break fast din ne da wanka zan yi, Asiya ta yi saurin kauda shakkun ta tace yanzu muje in maka wanka sai ka zo mu karya din ko? Yace muje dai mu fara karyawa bari in yi brush. Ya kuma daukar wayar sa ya saka aljihun jallabiyar sa. Murmushin takaici Asiya ta yi sannan tace ina jiran ka a can. Ta kalli danta yana bacci a gadon sa sannan ta wuce.
*Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[12/4, 12:12] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt
Inna bata gamsu da abinda Sulaiman ya fada ba,dan haka ta taka da kanta ta je har gidan su yaron ta same shi ta fadawa uwarsa komai, tace ita tana son yaro ya fadi gaskiya game da abinda ya sani na aiko shi da aka yi,kamar yadda ya fada haka ya maimaita Inna tace wa uwar dan Allah su lallaba mata shi ko zai fadi gaskiya. Ta kama hanya ta tafi.
Yaro kuwa ya yi ta rantsuwa akan cewar iyakacin Gaskiyar shi kenan dan haka suka shedawa Inna halin da ake ciki Inna dai zuciyarta ta kasa yarda amma bata da wani zabin ko tunanin face ita dai aga ƴarta.