Sashe 40
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Halifa yace Zan fi son hakan saki take bukata zan bata. "Karka yi saurin yanke haka, ka fara kiran waliyyin nata sai muji yadda za a yi.
Halifa ya ja tsaki kan mace Bros bazan dauki rainin hankali ba, babu wanda zai mutu dan baya tare da wani. Yarinyar nan fa ta wani gefen alfarma na yi mata,amma wai har ita ta kai mutum!!
Adamu yace "Haka ne amma abi komai sannu.
Kamar yadda Hajiya Talatu tace,tana idar da sallar asubahi ta kama shiri ta kalli Anty wadda ta idar da sallar tana kwance tana ta saka da mugu zare. Tace "To Sahiba nifa zakara zai bani sa a, zan zarga wa kare na igiya in yi gidana bazan bari wancan bomb din ya tashii da ni ba,dan kuwa dole zai tashi.sai dai in har ki ka kiyaye abinda zan fada miki to ba shakka asiri ba zai
tonu ba, ke koda asirin nan ya tonu to zai tonu a kuraren lokacin da sai dai su yi da sun sani.
Anty tace Hakan ma in yafaru ni ce da godiya.
Hajiya Talatu ta yi kasa da murya tace 'Kamar yadda na fada miki,wannan takardar sakin in har su ba jahilai bane kotu za su nufa shi kuma bai san zance ba yaga sammaci a zuciya irin tasa da kike fada ba zai je ba,saidai ya tura lauya to ke kuma sai ki maza ki siye lauyan kiyi ta tsara masa abinda zai fada masa da kuma yadda zai yi a kotu.'
Anty tace Kash ga bikin zuwa amma babu zanin daurawa.
Bani da kudin da zan baiwa lauya kina dai kallon rigimar dana dakko ta kudin mutumin nan gashi saura dari da Talatin duk na Bawa malamai. Hajiya Talatu tace Sai a kuma tambayar sa ya karo wani abu,naga fa kamar wani wawa sai sanda kika samu kya bashi. Anty tace 'Tab wannan fa daga gani dan tijara ne, amma dai bari mu gani in har suka kai shi karar ko ina ne zan nemo kudin dan dai inga bayan su. Hajiya Talatu tace Da kinyi kyan kai,yanzu dai ki samo min kudin mota in sa kai. Anty tace ko kwabo,ke din da duk kudin da kike min kwange ,ina kudaden da kika yi ta amsha gurin malaman nan ki na cewa zaki yi musu Transfer banga kin tura komai ba."Zan tura musu a hanya,network ne jiyan nan,zanci musu kudi ne?" Haka dai suka rabu suna ta yi wa juna ba a,da cin fuska.
Tana isa gurin Get Halifa ya shigo daga masallaci. A tsorace ta kauce ta yi gefe. Ya ja dogon tsaki.
Asiya ta na zaune kan gadon Asibitn kuka take kuma ta ki ci ta ki sha,bakin cikinta an kai Halifa Kotu,sannan sun ki sauraron ta tana fada musu akwai alkawura da Halifa ya yi mata ciki harda alkawarin ba zai taba sakinta ba,dan haka ita bata yarda cewa shine yayi sakin ba. Sai likitan ya bada shawara cewa a kaita Dawanau,akwai alamun Depression a tare da ita.
Halifa ya shiga cikin gida ya sauya riga ya fita zuwa gidan Baffan shi bayan sun gaisa sai Halifa ya sanar da Baffan sa halin da ake ciki na kararsa da Asiya ta yi, sannan ya nemi shawarar Baffan sa game da shi hukuncin da ya yanke, na bada takarda a kai kotu. Ko kuma ya aika mata da ita gida.Baffa ya yi salati daga bisani ya ba Halifa shawara cewa ya koma gida,insha Allah zai taka har gurin Waliyyin yarinyar su yi magana. Da ciwon kai ya koma gida. Yana ta kai kawo ga takarda da biro tun jiya ya kasa rubuta saki, sai yana ganin kamar ya karya alkawuran daya daukar mata.
Wata zuciyar tana ta zuga shi akan ya sake ta kawai tunda ita har ta iya kai shi kotu.
Washegari
Hafsi ta kwankwasa dakin yace shigo ta turo kofar tare da fadin "Uncle ga break fast din ka." Tafi dashi banaci, daga yau karki kara kawo min abinci dan Allah !! Ya daka mata tsawa .A gigice Hafsi ta fita. Anty kam dama ta san haka ce zata faru,Ada ma lokacin da bai fara zuwa kasuwa ba in yana fushi ba zai ci abincin gidan ba, kafin tasa a raunata mata zuciyar sa. Tace yarinyar nan da za su koma zama iya fushi da bakar zuciyar nan ta Halifa ka dai zata koreta gidan su.
Hafsi tace lokacin da zan shiga naji yana ta maimaita cewa wai ni Asiya zata kai kotu. Menene me zafi har haka? Anty ta tashi tsaye tana fadin anzo gurin bani wayata ta soma neman wayarta cike da murna. Hajiya Talatu tana dagawa ko gaisuwa bare ta tambayi ko har ta isa gida,abinda kawai ta ce Sahiba sun kawo masa sammaci. Hajiya Talatu cike dariya tace Alhamdulillah. Komai ya zo kamar yadda muka tsara,da sauki, kije ki lallaɓa shi kiji komai dan mugano bakin zaren muna bukatar samun lauyan, ta yadda zamu saye shi ya yi mana aiki." Anty tace wai ba yanzu ba, dan kuwa a fusace yake da kowa'zai iya komai in ya hau dokin zuciyar nan tashi.
Zanbi a sannu in dinga samo labari ko ba ta gurin shi ba.
Baffa ya samu Abban su Sulaiman a bakin wapa inda suka yi mahada,sun tattauna game da matsalolin kafin suka tsaida shawara cewa Abban su Sulaiman zai samu Inna da yarinyar kuma duk yadda ake ciki zai sanar da Baffa.
Abban su Sulaiman ya Isa gidan su Asiya ya yi sallama, daga ciki Sadiya ta amsa dama ita da yaranta ne a ciki Inna tana Asibiti da Asiya Sadiya ta fada masa cewa suna Asibiti bayan ta gaishe shi, yace To amma Yaya baku fada ba ko ke ba sai ki shiga ki sanar da Umman su Sulaiman ba?Sadiya tace an fada musu Abba inaga dai sun shafa a ne basu sanar da kai ba. Ya tambayi Asibitin ta sanar da shi, ya yi addu'a ya ce yaje gobe da sassafe ko kuma bayan issha yau in ya samu sarari.
Sannu a hankali Halifa ya gama kwashe kayan shi ya kai su sabon gidan shi duk ba tare da kowa ya sani ba.
Abban su Sulaiman ya kira Baffan Halifa ya sanar da shi cewa ya yi hakuri yarinyar bata da lafiya tana Asibiti in ta samu sauki za su zauna. Shima da safe zaije ya ga jikin.
Ya samu Asiya tana zaune Inna tana ta godo da ita akan tasha kunu amma taki. Yace" Ki amsa mana ki sha magani ai sai da abinci." Inna tace ka ganta nan tunda mijin ya aiko mata da takarda gaba daya ta haukace, sai zantuka take yi wai wallahi bashi bane ya mata alkawarin bazai sake ta ba,wai sai abarta taje ta tambaye shi. Taki ci ta ki sha, sunce ma zamu je dawanau ayi mata gwajin kwakwalwa. Ga hawan jini sai ya sauka ya kuma hawa,Wallahi Malam ina yin dana sani akan wannan aure na gaggawa da aka yi huce haushi kawai ya yi amma sam Halifa baya kaunar yarinyar shida yan uwansa har fa cewa ya yi shi ciki ba nasa bane.
"Subahanallahi " Abban su Sulaiman ya fada, abin har ya yi tsamari haka? Ashe har ya aiko da saki,ni da na zo ne akan batun kotu waliyinsa ya fada min suna son a yi masalaha a gida."
Inna tace "Masalaha yanzu ne suke son masalaha tunda su masu dashi ne suna jin kunyar tsayawa a gaban alkali masalaha daya ce ya karbi cikin shi domin ba zai yiwu ya tarwatsa mata yau sannan ya tarwatsa mata kuma goben ta ba. Ta tashi da dan da bashi da uba,wa zai aureta, shi kanshi dan an tarwatsa masa rayuwa fa kenan.
Abba cikin rashin fahimta yace "Wai tsaya, kina nufin cewa ya yi ba dansa ba ne?" Haka yace a jikin takardar daya aiko mata ta saki har uku. Na ce ko daya ma ya yi mata dama ni ba bari zan yi ta koma ba cutar ta isa haka.
Abba ya yi shiru ya rasa abin cewa. Ya kawo dubu biyu ya basu yace "To ni zan tafi,insha Allahu zanje har can gurin Baffan na shi in ji."
Asiya ta dago ido tace Abba dan Allah ka ce su barni in koma gidan mijina wallah bai sake ni, sharri ne kawai, wallahi ko da zai sake ni ba irin kalaman da ke cikin takardar zai rubutaba na san Halifa kuma na san me zai aikata.
Abba yace "Allah ya baki lafiya lallai kam da matsala" Gara kuje a duba kan nata."
Asiya tace Abba dan Allah a maganganuna ina ne na yi maganar rashin hankali? Ya ce 'Babu Asiya " Tace to me yasa ake jifana da kalmar hauka? Shiya sa nake yin shiru.
Haka dai Abba ya tafi cike da jimami na halin da yarinyar ta tsinci kanta.
amma kanshi a daure,domin shi Baffa bai fada masa cewar anyi saki ba,hasali ma dai ya nuna masa sun kai kara ne akan a bata takardar ta.
Halifa ya gama shiri tsaf zai fita sai ga kiran bros yace masa lafiya yanzu na shigo gidan na samu ana rigima Anty Umma ta zo kwasar kayan dakin ka Anty ta hana kuma tana ta kiran wayar ka amma ba ka daga ba. Halifa yace na ga ni Bros kawai dai ban daga bane saboda bana son in fadawa Anty abinda yafi wanda na fada mata ran nan. Ni na tashi a gidan gaba daya na bawa Anty Umma kayan tafi Anty bukatar su. Da yake a hands-free Bros ya saka duk suna ji su Antyn. Lamarin ya girgiza Anty har ta fasa kuka yau ita Halifa zai guda sabodar matar sa,to wallahi in zata yi yawo tsirara sai ta raba shi da ita.
Bros ya ce Anty kar ki dauki wani alhakin mana.Ita kanta yanzu haka bata gidan amma kin dora alhakin a kanta maimakon ki yi tunanin ina ne ki ka masa ba daidai ba ya za ayi kuma a gyara!! ""Kai ka min shiru Halifa haihuwar sa ne kawai ban yi ba,kuma kafin ya auri wannan yarinyar lafiya lau muke kowa ya sani,dan haka bazan bar wannan ya tafi a banza ba. Ta nufi ciki tana kuka.
Halifa ya ja tsaki kan mace Bros bazan dauki rainin hankali ba, babu wanda zai mutu dan baya tare da wani. Yarinyar nan fa ta wani gefen alfarma na yi mata,amma wai har ita ta kai mutum!!
Adamu yace "Haka ne amma abi komai sannu.
Kamar yadda Hajiya Talatu tace,tana idar da sallar asubahi ta kama shiri ta kalli Anty wadda ta idar da sallar tana kwance tana ta saka da mugu zare. Tace "To Sahiba nifa zakara zai bani sa a, zan zarga wa kare na igiya in yi gidana bazan bari wancan bomb din ya tashii da ni ba,dan kuwa dole zai tashi.sai dai in har ki ka kiyaye abinda zan fada miki to ba shakka asiri ba zai
tonu ba, ke koda asirin nan ya tonu to zai tonu a kuraren lokacin da sai dai su yi da sun sani.
Anty tace Hakan ma in yafaru ni ce da godiya.
Hajiya Talatu ta yi kasa da murya tace 'Kamar yadda na fada miki,wannan takardar sakin in har su ba jahilai bane kotu za su nufa shi kuma bai san zance ba yaga sammaci a zuciya irin tasa da kike fada ba zai je ba,saidai ya tura lauya to ke kuma sai ki maza ki siye lauyan kiyi ta tsara masa abinda zai fada masa da kuma yadda zai yi a kotu.'
Anty tace Kash ga bikin zuwa amma babu zanin daurawa.
Bani da kudin da zan baiwa lauya kina dai kallon rigimar dana dakko ta kudin mutumin nan gashi saura dari da Talatin duk na Bawa malamai. Hajiya Talatu tace Sai a kuma tambayar sa ya karo wani abu,naga fa kamar wani wawa sai sanda kika samu kya bashi. Anty tace 'Tab wannan fa daga gani dan tijara ne, amma dai bari mu gani in har suka kai shi karar ko ina ne zan nemo kudin dan dai inga bayan su. Hajiya Talatu tace Da kinyi kyan kai,yanzu dai ki samo min kudin mota in sa kai. Anty tace ko kwabo,ke din da duk kudin da kike min kwange ,ina kudaden da kika yi ta amsha gurin malaman nan ki na cewa zaki yi musu Transfer banga kin tura komai ba."Zan tura musu a hanya,network ne jiyan nan,zanci musu kudi ne?" Haka dai suka rabu suna ta yi wa juna ba a,da cin fuska.
Tana isa gurin Get Halifa ya shigo daga masallaci. A tsorace ta kauce ta yi gefe. Ya ja dogon tsaki.
Asiya ta na zaune kan gadon Asibitn kuka take kuma ta ki ci ta ki sha,bakin cikinta an kai Halifa Kotu,sannan sun ki sauraron ta tana fada musu akwai alkawura da Halifa ya yi mata ciki harda alkawarin ba zai taba sakinta ba,dan haka ita bata yarda cewa shine yayi sakin ba. Sai likitan ya bada shawara cewa a kaita Dawanau,akwai alamun Depression a tare da ita.
Halifa ya shiga cikin gida ya sauya riga ya fita zuwa gidan Baffan shi bayan sun gaisa sai Halifa ya sanar da Baffan sa halin da ake ciki na kararsa da Asiya ta yi, sannan ya nemi shawarar Baffan sa game da shi hukuncin da ya yanke, na bada takarda a kai kotu. Ko kuma ya aika mata da ita gida.Baffa ya yi salati daga bisani ya ba Halifa shawara cewa ya koma gida,insha Allah zai taka har gurin Waliyyin yarinyar su yi magana. Da ciwon kai ya koma gida. Yana ta kai kawo ga takarda da biro tun jiya ya kasa rubuta saki, sai yana ganin kamar ya karya alkawuran daya daukar mata.
Wata zuciyar tana ta zuga shi akan ya sake ta kawai tunda ita har ta iya kai shi kotu.
Washegari
Hafsi ta kwankwasa dakin yace shigo ta turo kofar tare da fadin "Uncle ga break fast din ka." Tafi dashi banaci, daga yau karki kara kawo min abinci dan Allah !! Ya daka mata tsawa .A gigice Hafsi ta fita. Anty kam dama ta san haka ce zata faru,Ada ma lokacin da bai fara zuwa kasuwa ba in yana fushi ba zai ci abincin gidan ba, kafin tasa a raunata mata zuciyar sa. Tace yarinyar nan da za su koma zama iya fushi da bakar zuciyar nan ta Halifa ka dai zata koreta gidan su.
Hafsi tace lokacin da zan shiga naji yana ta maimaita cewa wai ni Asiya zata kai kotu. Menene me zafi har haka? Anty ta tashi tsaye tana fadin anzo gurin bani wayata ta soma neman wayarta cike da murna. Hajiya Talatu tana dagawa ko gaisuwa bare ta tambayi ko har ta isa gida,abinda kawai ta ce Sahiba sun kawo masa sammaci. Hajiya Talatu cike dariya tace Alhamdulillah. Komai ya zo kamar yadda muka tsara,da sauki, kije ki lallaɓa shi kiji komai dan mugano bakin zaren muna bukatar samun lauyan, ta yadda zamu saye shi ya yi mana aiki." Anty tace wai ba yanzu ba, dan kuwa a fusace yake da kowa'zai iya komai in ya hau dokin zuciyar nan tashi.
Zanbi a sannu in dinga samo labari ko ba ta gurin shi ba.
Baffa ya samu Abban su Sulaiman a bakin wapa inda suka yi mahada,sun tattauna game da matsalolin kafin suka tsaida shawara cewa Abban su Sulaiman zai samu Inna da yarinyar kuma duk yadda ake ciki zai sanar da Baffa.
Abban su Sulaiman ya Isa gidan su Asiya ya yi sallama, daga ciki Sadiya ta amsa dama ita da yaranta ne a ciki Inna tana Asibiti da Asiya Sadiya ta fada masa cewa suna Asibiti bayan ta gaishe shi, yace To amma Yaya baku fada ba ko ke ba sai ki shiga ki sanar da Umman su Sulaiman ba?Sadiya tace an fada musu Abba inaga dai sun shafa a ne basu sanar da kai ba. Ya tambayi Asibitin ta sanar da shi, ya yi addu'a ya ce yaje gobe da sassafe ko kuma bayan issha yau in ya samu sarari.
Sannu a hankali Halifa ya gama kwashe kayan shi ya kai su sabon gidan shi duk ba tare da kowa ya sani ba.
Abban su Sulaiman ya kira Baffan Halifa ya sanar da shi cewa ya yi hakuri yarinyar bata da lafiya tana Asibiti in ta samu sauki za su zauna. Shima da safe zaije ya ga jikin.
Ya samu Asiya tana zaune Inna tana ta godo da ita akan tasha kunu amma taki. Yace" Ki amsa mana ki sha magani ai sai da abinci." Inna tace ka ganta nan tunda mijin ya aiko mata da takarda gaba daya ta haukace, sai zantuka take yi wai wallahi bashi bane ya mata alkawarin bazai sake ta ba,wai sai abarta taje ta tambaye shi. Taki ci ta ki sha, sunce ma zamu je dawanau ayi mata gwajin kwakwalwa. Ga hawan jini sai ya sauka ya kuma hawa,Wallahi Malam ina yin dana sani akan wannan aure na gaggawa da aka yi huce haushi kawai ya yi amma sam Halifa baya kaunar yarinyar shida yan uwansa har fa cewa ya yi shi ciki ba nasa bane.
"Subahanallahi " Abban su Sulaiman ya fada, abin har ya yi tsamari haka? Ashe har ya aiko da saki,ni da na zo ne akan batun kotu waliyinsa ya fada min suna son a yi masalaha a gida."
Inna tace "Masalaha yanzu ne suke son masalaha tunda su masu dashi ne suna jin kunyar tsayawa a gaban alkali masalaha daya ce ya karbi cikin shi domin ba zai yiwu ya tarwatsa mata yau sannan ya tarwatsa mata kuma goben ta ba. Ta tashi da dan da bashi da uba,wa zai aureta, shi kanshi dan an tarwatsa masa rayuwa fa kenan.
Abba cikin rashin fahimta yace "Wai tsaya, kina nufin cewa ya yi ba dansa ba ne?" Haka yace a jikin takardar daya aiko mata ta saki har uku. Na ce ko daya ma ya yi mata dama ni ba bari zan yi ta koma ba cutar ta isa haka.
Abba ya yi shiru ya rasa abin cewa. Ya kawo dubu biyu ya basu yace "To ni zan tafi,insha Allahu zanje har can gurin Baffan na shi in ji."
Asiya ta dago ido tace Abba dan Allah ka ce su barni in koma gidan mijina wallah bai sake ni, sharri ne kawai, wallahi ko da zai sake ni ba irin kalaman da ke cikin takardar zai rubutaba na san Halifa kuma na san me zai aikata.
Abba yace "Allah ya baki lafiya lallai kam da matsala" Gara kuje a duba kan nata."
Asiya tace Abba dan Allah a maganganuna ina ne na yi maganar rashin hankali? Ya ce 'Babu Asiya " Tace to me yasa ake jifana da kalmar hauka? Shiya sa nake yin shiru.
Haka dai Abba ya tafi cike da jimami na halin da yarinyar ta tsinci kanta.
amma kanshi a daure,domin shi Baffa bai fada masa cewar anyi saki ba,hasali ma dai ya nuna masa sun kai kara ne akan a bata takardar ta.
Halifa ya gama shiri tsaf zai fita sai ga kiran bros yace masa lafiya yanzu na shigo gidan na samu ana rigima Anty Umma ta zo kwasar kayan dakin ka Anty ta hana kuma tana ta kiran wayar ka amma ba ka daga ba. Halifa yace na ga ni Bros kawai dai ban daga bane saboda bana son in fadawa Anty abinda yafi wanda na fada mata ran nan. Ni na tashi a gidan gaba daya na bawa Anty Umma kayan tafi Anty bukatar su. Da yake a hands-free Bros ya saka duk suna ji su Antyn. Lamarin ya girgiza Anty har ta fasa kuka yau ita Halifa zai guda sabodar matar sa,to wallahi in zata yi yawo tsirara sai ta raba shi da ita.
Bros ya ce Anty kar ki dauki wani alhakin mana.Ita kanta yanzu haka bata gidan amma kin dora alhakin a kanta maimakon ki yi tunanin ina ne ki ka masa ba daidai ba ya za ayi kuma a gyara!! ""Kai ka min shiru Halifa haihuwar sa ne kawai ban yi ba,kuma kafin ya auri wannan yarinyar lafiya lau muke kowa ya sani,dan haka bazan bar wannan ya tafi a banza ba. Ta nufi ciki tana kuka.