Sashe 6
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asiya ta kalli dakalin bayan ta fito. Yana zaune yana danna waya hasken fitilar kofar gidan ta haske masa fuska. In banda Allah wa zai maka Haka. Asiya ta darsa a zuciyar ta. Tasan ko kusa da ajin wannan gayen bata zo ba.
Ta taka a hankali ta isa gurin ta rusuna sannu da zuwa. Ta furta tana Kallon fuskarshi dan samun tabbacin ko shidinne..
Ya Kalle ta "Tashi mana ammmm Sadiya ko?" Tace Asiya dai Sadiya yayata ce. Yace sorry tashi Asiyatu. " Yanzu kam ta tabbatar shine. Ta zauna da yar tazara tsakanin su. Ya kalleta "Asiya ya jikin Baba ina fata yana samun sauki?" Tace so sai ma kuwa musamman jiya zuwa yau tamkar ka zo masa da waraka Muna ta yi wa Allah godiya.
Ya yi murmushi ashe tana da magana haka. Ya darsa a zuciyar sa. Sannan yace, "To Malam Asiya ya ki ka ga angon na ki?" Ta dan yi murmushi sannan ta sunkuyar da kai, tace me kake son infada? Yace Duk abinda ya zo bakin ki. " Ta danyi jim wani jin kai wanda bata san tana da shi ba ya motsa ta saci Kallon shi ta ga ita yake kallo, tace masha Allah barakallah.
Ya yi murmushi ya ga wani hali guda daya da yake so, yana son mace mai jin kanta cewa ita mace ce, yarinyar in ta samu kula zata yi yadda yake so. A zuciyar sa yace Bari ya sake latsata.
Ya dan yi gyaran murya. "Na yi mamaki fa wai ya akayi kika amince da ni haka? Da ga ganina fa baki sanni ba."
Ta danyi jim tana nazarin me zata fada, can tace Duk abinda na roki Allah a kai yana amsa min. Kullum Babana yana cewa "Allah ka kawo wa Asiya da Sadiya miji wanda zai kula da su ko bayan raina. Kasan ina girmama kalaman Babana jin haka sai nima na dora da adduo'in ina rokon Allah ya cika burin Babana ya kawo min mijin wanda yake zabin sa shi. To kana ganin cewa ba kai ne amsar addu a ta ba? Ya yi murmushi Ni ne gaskiya domin ba zance ga dalilin da yasa na yi miki maganar aure ba, Allah ne ya aiko ni, to kuma kina so na?" Tace Ni ban san so ba, amma zaka iya yimin bayani yadda ya ke.
Yace shike nan zan koya miki "amma sai na cire son wata a zuciyata." ya tsura mata ido. Itama ta kalle shi sannan ta sunkuyar da kai. Tace" To. " Abba ya yi sallama ya aje flas din awara da fiya wata a Leda. ya gaishe da shi ya amsa tare da tambayar kai ne Abba? Abba yace,"Nine. Halifa ya ce to Malam Abba maida wannan abin gida naci dazu." Ta kalleshi. baza ka kara ba?
Ya girgiza kai, tace shikenan Abba wuce da shi amma ka aje masa ruwan. Ta ciro daga Leda ta mika mishi, wani abu da yake ji tun da ya shaki wannan hodar ya kuma taso masa, ya danja tsaki sannan ya ce" Ki barshi . " lokaci guda kuma ya mike tsaye, ina ga zantafi ina jin kamar bana jin dadi."
Gaban Asiya ya fadi. Allah dai yasa ba ni ce na bata maka rai ba. Ta fada cikin damuwa. Yace ko kadan ya cije game da sabon yanayin yace "Amarya bakya laifi ko kin kashe dan masu gida, haka Hausawa suke fadi ko?" Asiya ta marairaice murya tace Yaya ban iya hira ba ko? Ta. mike ita ma, ka yi hakuri ban taba zance bane amma zaka koya min? Yace "Ai zancen mu bashi da tsawo ya kamata daga yau ma a dena wanna awarar a soma gyaran jiki ko?" Ta ce to duk yadda ka ce. Ya soma tafiya tare da fadin dan takamin mana."
Suka jera a hankali suke tafiyar yace Wai kuwa kina samun nawa a rana wannan awarar? Tace "Gaskiya muna samu, har dubu biyu fa wata ran muna ci a kwano daya, kai ko anyi kwantai fa muna samun abinda Baba zai ci mu kuma sai muci awarar ka san ba kowane abinci yake ci ba. Wataran kuma sai Maman Annur Sadiyarmu tana zuwa da abincin da zai iya ci daga gidan aikin ta sai musaka kudin sai masa abinci a bankinmu na kudin maganinsa. Yace Allah Sarki Ubangiji ya baku lada, ku kuke ta fama da gidan da kudin jinyarsa, ba masu taimaka wa ne a unguwar? Tace "Sun yi fa, yanzun ne kowa yana fama da kanshi, kuma gaskiya ni nafi son mu yi sana a da mu tsaya neman taimakon." Yace Haka ne yanzu kuma gashi zan dauke ki wa zai ke yin awarar? "
Asiya tace Abba zai ci gaba ko don kula da Baba, ta fada a rauna ne, domin sai taji wani yanayi na kewar rabuwa da ahalin ta. Daidai lokacin sun Iso shagon saida kayan masarufi ya ce ina zuwa, ya shiga, tana bakin shagon daya daga cikin masu saida kayan yace "
Asiya waken awara kwano nawa? " Tace ba siya na zo ba yanzu. Yace "Asiya Wai ance za ki yi aure da gaske ne?" Tace injiwa? Wani daga ciki ya am she da fadin gaske ne mana, har lefe an kawo. Wanda ya yi tambayar yace harda su lefe abin azimun amma waye wannan haka zai yi jihadi?"
Sai lokacin Halifa ya sa baki don tunda suke magana bai ce kala ba yana dai ta fadin a miko masa wannan nawa wancan. Yace Ba musulma bace dama? Suka ce Musulma ce yace me ya kawo batun jihadi? Wanda ya furta kalma yace to Megida duk yan matan garin nan ga sunan kosassu wannan kalleta fa kamar ka hureta ta fadi, anya ma ta isa aure? Halifa yace " Ina dai tana da halin kwarai?" har suna hada baki gurin cewa wannan kuma sai ince kaf unguwar nan da wuya asamu wadda tafi yarinyar hankali ga nutsuwa inda wata ce muna fara mata wannan wasan kasan da yanzu ta zage mu.
Halifa yace "wannan ai ba wasa bane, kuma ni ne wanda zai yi jihadi da ka ke magana, ni ne mijin Asiya sai ka duba ka gani dame ka fini kai da kake kushe ta?"
Mamaki ya ishe su, duk harda masu siyayyar suka kalleshi babu wanda ya kara magana cikin su sai wani da shima ya zo siyayya yace Allah ya sanya alkairi.
Kayan shayi da sabulan wanki da omo su makilin su ya siya da bread leda biyu ya biya su ya dakko. Asiya wadda taji duk ta muzanta a gaban saurayin ta an ci mata fuska kuma tanaji duk jikinta a sanyaye ta kalli fuskar Halifa. Tace kaji me mutane suke fada game da ni ko? Kamar bai ji me tace ba ya mika mata ledojin "Amshi wannan maza kije gida zan kira ki". Tace ai ba waya a gidan mu. Ya ciro wayoyin sa guda biyu ya mika mata babbar ki rike ta da kyau akwai muhimman abubuwa na aciki, zan kira ki. Duk wanda ya kira ki daga ki ce a neme ni ta daya layin. Tace To. Mun gode Allah ya jikan mahaifa ya kara budi. Cikin jin dadi ya ce "Ameen."
Ya nufi can inda ya yi fakin ta kwashi kaya Niki niki ta nufi gida.
Kafin Halifa ya kai gurin mota ya soma amai da kyar ya ke jan motar, yana ta amai. Yana shiga gida ya aje motar ya fito. Kanshi ya sara da ciwo ya nufi dakin shi, jiri na dibar shi. Yana kokarin ya bude kofa sai ya fadi a gurin yana maida numfashi. Yana son ya ciro Wayar shi daga aljihu Hafsi tana isowa gurin kamar yadda Anty ta turo ta ta duba mata ko shine dan taji shigo war mota.
*** ***
Bilkisu ta kalli mahaifiyar ta tace na gama jan Ya Wadudu kafa dubu kuma ba wanda na kuskure ban hada da sunan shi ba, yanzu saura sadakar kosan da zanyi da safe ko?
Mahaifiyar tace e "Ai insha Allah gobe da kafarshi zai shigo gidan nan yana baki hakuri har sai kin ja masa aji." Bilkisu tace humm ya dai zo din Umma ko ban ja masa yanzu ba muna komawa daidai sai ya gane Allah daya ne, dan zan rama abinda ya yi min. Umma ta sa dariya "Sun isa su sani inji kunya Asa bikin shekara guda sai da lokacin ya zo ya fasa, aiko da na kai shi Human rayit su bi miki hakkin ki na bata miki lokacin da ya yi sannan ya hana ki kula kowa, ta ina zaki fara yanzu shekarun ki a shirin da bakwai fa dan ma muna zabge uku muna cewa ashiru da hudu ki ke. " Bilkisu tace ai Halifa ma ba zai iya rabuwa da niba, na fa san irin son da ya ke min, duk barazana ce.
*** ***
Hafsi ta juya tana kuka, da ihu ga Uncle Halifa ya fadi. Da gudu suka fito Hajiya Talatu da Anty shigowar Dady kenan ya dakko mota sai Asibitin.
Likitan ya gama gwaje sannan ya sa a bashi taimakon gaggawa sai da aka gama tsaf yana kwance an sa masa ruwa. Ya dubi su Anty me ya ci na karshe? Duk suka yi Jim Anty tace sai dai kuma shine zai fada tunda daga waje ya ke. Dady ya kalli Likitan menene a cikin abinda ya ci?...
*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[5/24, 10:05] Ummi Tandama😇: Page 5
Likita yace "dole aƙwai abinda ya ci ko ya shaƙa ko kuma ya jima bai ci komai ba kuma yana da ulser. Halifa dake jinsu sama-sama har dai bacci ya yi gaba da shi.
Ta taka a hankali ta isa gurin ta rusuna sannu da zuwa. Ta furta tana Kallon fuskarshi dan samun tabbacin ko shidinne..
Ya Kalle ta "Tashi mana ammmm Sadiya ko?" Tace Asiya dai Sadiya yayata ce. Yace sorry tashi Asiyatu. " Yanzu kam ta tabbatar shine. Ta zauna da yar tazara tsakanin su. Ya kalleta "Asiya ya jikin Baba ina fata yana samun sauki?" Tace so sai ma kuwa musamman jiya zuwa yau tamkar ka zo masa da waraka Muna ta yi wa Allah godiya.
Ya yi murmushi ashe tana da magana haka. Ya darsa a zuciyar sa. Sannan yace, "To Malam Asiya ya ki ka ga angon na ki?" Ta dan yi murmushi sannan ta sunkuyar da kai, tace me kake son infada? Yace Duk abinda ya zo bakin ki. " Ta danyi jim wani jin kai wanda bata san tana da shi ba ya motsa ta saci Kallon shi ta ga ita yake kallo, tace masha Allah barakallah.
Ya yi murmushi ya ga wani hali guda daya da yake so, yana son mace mai jin kanta cewa ita mace ce, yarinyar in ta samu kula zata yi yadda yake so. A zuciyar sa yace Bari ya sake latsata.
Ya dan yi gyaran murya. "Na yi mamaki fa wai ya akayi kika amince da ni haka? Da ga ganina fa baki sanni ba."
Ta danyi jim tana nazarin me zata fada, can tace Duk abinda na roki Allah a kai yana amsa min. Kullum Babana yana cewa "Allah ka kawo wa Asiya da Sadiya miji wanda zai kula da su ko bayan raina. Kasan ina girmama kalaman Babana jin haka sai nima na dora da adduo'in ina rokon Allah ya cika burin Babana ya kawo min mijin wanda yake zabin sa shi. To kana ganin cewa ba kai ne amsar addu a ta ba? Ya yi murmushi Ni ne gaskiya domin ba zance ga dalilin da yasa na yi miki maganar aure ba, Allah ne ya aiko ni, to kuma kina so na?" Tace Ni ban san so ba, amma zaka iya yimin bayani yadda ya ke.
Yace shike nan zan koya miki "amma sai na cire son wata a zuciyata." ya tsura mata ido. Itama ta kalle shi sannan ta sunkuyar da kai. Tace" To. " Abba ya yi sallama ya aje flas din awara da fiya wata a Leda. ya gaishe da shi ya amsa tare da tambayar kai ne Abba? Abba yace,"Nine. Halifa ya ce to Malam Abba maida wannan abin gida naci dazu." Ta kalleshi. baza ka kara ba?
Ya girgiza kai, tace shikenan Abba wuce da shi amma ka aje masa ruwan. Ta ciro daga Leda ta mika mishi, wani abu da yake ji tun da ya shaki wannan hodar ya kuma taso masa, ya danja tsaki sannan ya ce" Ki barshi . " lokaci guda kuma ya mike tsaye, ina ga zantafi ina jin kamar bana jin dadi."
Gaban Asiya ya fadi. Allah dai yasa ba ni ce na bata maka rai ba. Ta fada cikin damuwa. Yace ko kadan ya cije game da sabon yanayin yace "Amarya bakya laifi ko kin kashe dan masu gida, haka Hausawa suke fadi ko?" Asiya ta marairaice murya tace Yaya ban iya hira ba ko? Ta. mike ita ma, ka yi hakuri ban taba zance bane amma zaka koya min? Yace "Ai zancen mu bashi da tsawo ya kamata daga yau ma a dena wanna awarar a soma gyaran jiki ko?" Ta ce to duk yadda ka ce. Ya soma tafiya tare da fadin dan takamin mana."
Suka jera a hankali suke tafiyar yace Wai kuwa kina samun nawa a rana wannan awarar? Tace "Gaskiya muna samu, har dubu biyu fa wata ran muna ci a kwano daya, kai ko anyi kwantai fa muna samun abinda Baba zai ci mu kuma sai muci awarar ka san ba kowane abinci yake ci ba. Wataran kuma sai Maman Annur Sadiyarmu tana zuwa da abincin da zai iya ci daga gidan aikin ta sai musaka kudin sai masa abinci a bankinmu na kudin maganinsa. Yace Allah Sarki Ubangiji ya baku lada, ku kuke ta fama da gidan da kudin jinyarsa, ba masu taimaka wa ne a unguwar? Tace "Sun yi fa, yanzun ne kowa yana fama da kanshi, kuma gaskiya ni nafi son mu yi sana a da mu tsaya neman taimakon." Yace Haka ne yanzu kuma gashi zan dauke ki wa zai ke yin awarar? "
Asiya tace Abba zai ci gaba ko don kula da Baba, ta fada a rauna ne, domin sai taji wani yanayi na kewar rabuwa da ahalin ta. Daidai lokacin sun Iso shagon saida kayan masarufi ya ce ina zuwa, ya shiga, tana bakin shagon daya daga cikin masu saida kayan yace "
Asiya waken awara kwano nawa? " Tace ba siya na zo ba yanzu. Yace "Asiya Wai ance za ki yi aure da gaske ne?" Tace injiwa? Wani daga ciki ya am she da fadin gaske ne mana, har lefe an kawo. Wanda ya yi tambayar yace harda su lefe abin azimun amma waye wannan haka zai yi jihadi?"
Sai lokacin Halifa ya sa baki don tunda suke magana bai ce kala ba yana dai ta fadin a miko masa wannan nawa wancan. Yace Ba musulma bace dama? Suka ce Musulma ce yace me ya kawo batun jihadi? Wanda ya furta kalma yace to Megida duk yan matan garin nan ga sunan kosassu wannan kalleta fa kamar ka hureta ta fadi, anya ma ta isa aure? Halifa yace " Ina dai tana da halin kwarai?" har suna hada baki gurin cewa wannan kuma sai ince kaf unguwar nan da wuya asamu wadda tafi yarinyar hankali ga nutsuwa inda wata ce muna fara mata wannan wasan kasan da yanzu ta zage mu.
Halifa yace "wannan ai ba wasa bane, kuma ni ne wanda zai yi jihadi da ka ke magana, ni ne mijin Asiya sai ka duba ka gani dame ka fini kai da kake kushe ta?"
Mamaki ya ishe su, duk harda masu siyayyar suka kalleshi babu wanda ya kara magana cikin su sai wani da shima ya zo siyayya yace Allah ya sanya alkairi.
Kayan shayi da sabulan wanki da omo su makilin su ya siya da bread leda biyu ya biya su ya dakko. Asiya wadda taji duk ta muzanta a gaban saurayin ta an ci mata fuska kuma tanaji duk jikinta a sanyaye ta kalli fuskar Halifa. Tace kaji me mutane suke fada game da ni ko? Kamar bai ji me tace ba ya mika mata ledojin "Amshi wannan maza kije gida zan kira ki". Tace ai ba waya a gidan mu. Ya ciro wayoyin sa guda biyu ya mika mata babbar ki rike ta da kyau akwai muhimman abubuwa na aciki, zan kira ki. Duk wanda ya kira ki daga ki ce a neme ni ta daya layin. Tace To. Mun gode Allah ya jikan mahaifa ya kara budi. Cikin jin dadi ya ce "Ameen."
Ya nufi can inda ya yi fakin ta kwashi kaya Niki niki ta nufi gida.
Kafin Halifa ya kai gurin mota ya soma amai da kyar ya ke jan motar, yana ta amai. Yana shiga gida ya aje motar ya fito. Kanshi ya sara da ciwo ya nufi dakin shi, jiri na dibar shi. Yana kokarin ya bude kofa sai ya fadi a gurin yana maida numfashi. Yana son ya ciro Wayar shi daga aljihu Hafsi tana isowa gurin kamar yadda Anty ta turo ta ta duba mata ko shine dan taji shigo war mota.
*** ***
Bilkisu ta kalli mahaifiyar ta tace na gama jan Ya Wadudu kafa dubu kuma ba wanda na kuskure ban hada da sunan shi ba, yanzu saura sadakar kosan da zanyi da safe ko?
Mahaifiyar tace e "Ai insha Allah gobe da kafarshi zai shigo gidan nan yana baki hakuri har sai kin ja masa aji." Bilkisu tace humm ya dai zo din Umma ko ban ja masa yanzu ba muna komawa daidai sai ya gane Allah daya ne, dan zan rama abinda ya yi min. Umma ta sa dariya "Sun isa su sani inji kunya Asa bikin shekara guda sai da lokacin ya zo ya fasa, aiko da na kai shi Human rayit su bi miki hakkin ki na bata miki lokacin da ya yi sannan ya hana ki kula kowa, ta ina zaki fara yanzu shekarun ki a shirin da bakwai fa dan ma muna zabge uku muna cewa ashiru da hudu ki ke. " Bilkisu tace ai Halifa ma ba zai iya rabuwa da niba, na fa san irin son da ya ke min, duk barazana ce.
*** ***
Hafsi ta juya tana kuka, da ihu ga Uncle Halifa ya fadi. Da gudu suka fito Hajiya Talatu da Anty shigowar Dady kenan ya dakko mota sai Asibitin.
Likitan ya gama gwaje sannan ya sa a bashi taimakon gaggawa sai da aka gama tsaf yana kwance an sa masa ruwa. Ya dubi su Anty me ya ci na karshe? Duk suka yi Jim Anty tace sai dai kuma shine zai fada tunda daga waje ya ke. Dady ya kalli Likitan menene a cikin abinda ya ci?...
*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[5/24, 10:05] Ummi Tandama😇: Page 5
Likita yace "dole aƙwai abinda ya ci ko ya shaƙa ko kuma ya jima bai ci komai ba kuma yana da ulser. Halifa dake jinsu sama-sama har dai bacci ya yi gaba da shi.