Sashe 35
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[8/28, 10:09] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w
Hajiya Talatu ce ta binciko cewar Asiya tana garin su, ta hanyar yin amfani da wata makociyar su Inna. Kuma ta bata aikin cewar duk lokacin da Asiya ta dawo ga lambar ta nan Dan Allah ta sanar da ita, domin ita tana aiki ne da Hukumar kare hakkin dan Adam sannan taga Videon Asiya yana yawo wanda ta san cewa sharri akai mata.
Makociya ta saki jiki tare da fadin tabbas sharri ne, domin Asiya yarinyar kirki ce zan sanar da Innar su kuma nasan in ta dawo zata sanar da ni.
Haka kuwa makociya ta shiga gidan cike da murnar taimakon su Inna ta sanar da Inna komai. Inna tace to gaskiya dai ni bana ma son sai muje muna wata shara a ko wani maida zance. Allah dai na barwa komai Asiya zata dawo amma bansan rana ba wallahi. Makociya ta yi ta kokarin wayar wa da Inna kai amma Inna tace Allah ya zaba abinda yake mafi alkairi.
Ko dan wannan tashin hankali na yan Biñdiga da suka soma kawo hari makotan kauyen nan Asiya dole ki koma gida tun da can komai ya lafa ko kuma ki zauna a kurna. Domin muma kaura zamu yi daga nan zamu tafi Kankiya Baba Tabawa take fadawa Asiya. Asiya tace "Nima na yi tunanin haka amma ji nake gaba daya an cire min Kano a raina sai dai inje dole." Tabawa tace Hakuri za ki yi saidai in zaki bimu hijirar sai mu tafi. Asiya tace haba dai, babu wani abu zuwa gobe sai in koma Kano.
Makociya ta sanar da Hajiya Talatu bayan dawowar Asiya da kwana biyu dan haka suka soma shirya abinda za su aiwatar.
Sulaiman Asiya ta sa Abba ya kira mata. Suka gaisa a soro. Tace kasan abinda ya sa na kira ka Yaya Sulaiman? Yace 'A' a. Tace Ina son inji ko kunyi magana da Abokin ka ne, bansan zaman da nake yi ba har yanzu gara ya bani takarda ta sannan in san matsayin dan ciki na. Ta kai karshen maganar da kuka.
Sulaiman ya ce Kiyi Hakuri wallahi Halifa nima bai daga wayata ba tunda aka shiga wannan kwamacalar yanzu ma ina zaton ya yi Blocking dina ne dan bana samun shi, kawai, ina son Kiyi hakuri zanje har kasuwar su in same shi zuwa kamar karfe biyu. Duk yadda ake ciki zan sanar da ke zuwa magariba.
Tace to Na gode ina son zuwa Asibiti ne amma sai naji inda muka kwana da zancen shi. Yace ba damuwa.
Kamar yadda Sulaiman ya alkawarta haka ya yi. Yaje saidai yaran shagon sun tabbatar masa da cewa Halifa baya kasar kusan wata daya kenan amma suna sa ran dawowar shi cikin satin nan. Ya bukaci lambar da zai same shi. Suka ce ai ba a samun shi sai dai in shine ya kira.
Haka Sulaiman ya sanar da Asiya lokacin da ya shiga gidan bayan magariba. Yace ki kara hakuri nima sai yanzu na huce dana fahimci ashe baya nan ne, kuma gaskiya ko can dama abotarmu bawai ta yi mugun karfin da duk inda zashi sai ya sanar da mu bane. Yana dai son mu ne gaskiya dan kafin mu nemeshi ya nememu ya yi mana alkairi kinga kenan baya nan Anty ta kawo wa Inna yansanda bana tunanin ya sani. Asiya ta sauke Ajiyar zuciya Sannan tace haka ka ke gani? Yace Gaskiya dai haka ne ma ance ya yi wata baya nan su kuma ai ba ayi wata ba. Sannan a iya sanina da Halifa Koda abinda ya faru da gaske ne ba zai sa a kama Inna ba. Asiya tace to Allah ya sa hakan ne. Sulaiman ya kawo kudi dubu goma ya ba Asiya ga wannan kije Asibitin inhar da wata damuwa ki sanar dani. Asiya zata ki amsa ya yi mata tsawa da cewa baya son haka. Ta amsa ta yi godiya. Inna ma ta yi masa godiya. Asiya ta na kwance tana tunani ko da ba gaskiya bane abinda Sulaiman ya fada ta ji sanyi da farin ciki. Allah ya sa su koma zaman su da mijinta tana sonshi sosai.
Asiya da Sadiyan su Maman Annur suka tafi Asibiti tun a gida suke ta shawara suje Asibitin Unguwa ne ko kuwa suje Murtala. Karshe dai suka tafi wani Asibitin kudi amma ba shi da tsada wata mata da suka hau kekenapep ta basu shawara tace ga kula sosai.Sun isa Asibitin nan suka fada mata cewar dubu ishirin ne zata biya har ta haihu, saidai hoton ciki ko magani su siya zata yi. Tace zata fara ba su dubu goma kafin ta haihu sai ta cika, suka ce babu damuwa.
An tabbatar mata ita da abinda ke cikin nata duk suna lafiya domin bugun zuciyar sa daidai, amma an bata takardar da zata yi hoto domin aga yanayi zaman sa. Sadiya ce ta bata kudin hoton domin anyi mata albashinta ba jimawa. Sunce cikin nata watan shi Hudu da sati uku kuma sun saka mata ranar
haihuwa.
Hajiya Talatu da Anty suka shiga duba katuna sun samu masu suna Asiya guda biyu saidai ba za su gane wacce ce ba saboda Anty bata san sunan Baban Asiya ba. Likitan yace ku duba shekarun mana, inhar baku gane nata shekarun ba sai ku bincika sunan Babanta. Sun samu Asiya daya shekaru Talatin dayar sha takwas, dan haka suka gano yar sha takwas din nan dai ita ce suka zo akan ta.
Hajiya Talatu itace ta sanar da Likitan abinda suke bukata suna son a zubda cikin Asiya suna son ya fadi abinda za su bashi.
Ya dan jima yana Nazari Sannan yace "To da farko dai ina mijinta domin bana son in shiga abinda zai bada matsala. Anty tace bata da miji sun rabu sakamakon kamata da ya yi tirmi da tabar ya da wani, to sai ta zo da wannan cikin tace nasa ne, nasan in anje kotun musulinci shi za a bawa cikin nan, ni kuma gaskiya bazan yarda a bashi ciki da ba nasa ba, shine kawai zamu raba gaddamar.
Likitan yace to ba damuwa miliyan daya zaki bani. Anty ta mike tsaye a gigice haba dai kai kuwa milinyan fa da yawa gaskiya yace to baki duba girman laifin da kike son a aikata wadda ta saba da Dokar likitanci akan wannan aikin naki sai a rufe asibitin tare da kwace lasisin Asibitina, ya dan yi shiru gaskiya nama fasa domin aikin yana da hadari sosai.
Hajiya Talatu tace "Kinji matsalar ki ke baki son fidda kudi kuma kina son ayi miki aikin kudi. " Anty tace ke bazaki gane bane, nifa ba nice me kudin ba Halifa ne me kudin rigar alfamar sa ce ke nuna ni ake min kallon kudi. Hajiya Talatu ta kyakyace da dariyar keta, sannan tace To sai ki ta shi mu tunda ba kudi. Anty ta danyi tsai tana tunanin inda zata samar da wannan kudin kai tsaye.
In kawo miki mai sayen ragowar kayan Lefen nan ku karasar da su har akwatunan ki biya bukatar gabanki. Anty ta danyi shiru tana tunanin Anya kuwa Halifa zai yafe mata ta saida masa kayan masu tsada ta hanyar karyar da su kuma ta yi amfani da kudin gurin zubar masa da ciki dan sa. Ta saki murmushin mugunta tare da fadin hakuri zai yi kawai. Ta kalli Talatu shikenan zanje in nemo rabi aiki yana kammala zan cika maka saura.
Asiya taga Anty da Hajiya Talatu sun biyo ta da gudu tana ta boyewa kuma a cikin Asibitin da taje awo. Ta labe a wani daki suna ta neman ta sai taga wani likita ya shigo yace karki damu zan boye ki biyoni. Bayan ta bishi ya boye ta sai kuma ta hango shi ta windor yana magana da su suna tuntsira dariya. Firgugit ta farka ta tashi zaune tana addu"a, tayi hamdala da ta ga mafarki ne, Asiya tana da girmama mafarki, bata yawan yin sa, amma kuma duk lokacin da zata yi shi sai ya zame mata kamar ishara ko nuni zuwa ga wani abu.
Suna karyawa da safe tace wa Maman Annur nifa ina zargin kamar Anty tana bibiyata domin na yi wani mafarki da ya bani tsoro abin ya shafi cikin jikina domin harda Asibitin da mukaje. ta bata labarin mafarkin. "Karki baiwa mafarki muhimmanci. Da Yawan mafarkai shedan ne ki kyautata zato kiyi addua khairan insha Allah.
Halifa ya sauka a filin jirgin sama na Kano da karfe shidda na safe, mota ya dauka kai tsaye ta kai shi gidan sa, sai da yayi bacci ya huta yunwa ta fito dashi, yaje gidan ci abinci ya ci sannan ya sake daukan mai a daidaita sahu zuwa gida. Kiran Baffan sa ya shigo wayarsa, mamaki ya kama shi tunda ya shigo ya maida layinsa yake jin saukar sakwanni tunda ya duba daya biyu babu na Asiya kawai ya fita sabgar su. Ba wanda ya kira shi dan bai fadawa kowa cewar ya dawo ba.
Ya daga cike da girmamawa suka gaisa Baffa yace ashe ka dawo? Halifa yace na dawo tun sassafiya da yake gidana na wuce ko su Anty ba su san na dawo ba. Baffa yace to idan babu damuwa ina son kazo yanzu. To ganinan Insha Allah. Ya saka me a daidaita suka kama hanyar gidan Baffa. Cike da sake sake.
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[8/28, 10:09] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w
Hajiya Talatu ce ta binciko cewar Asiya tana garin su, ta hanyar yin amfani da wata makociyar su Inna. Kuma ta bata aikin cewar duk lokacin da Asiya ta dawo ga lambar ta nan Dan Allah ta sanar da ita, domin ita tana aiki ne da Hukumar kare hakkin dan Adam sannan taga Videon Asiya yana yawo wanda ta san cewa sharri akai mata.
Makociya ta saki jiki tare da fadin tabbas sharri ne, domin Asiya yarinyar kirki ce zan sanar da Innar su kuma nasan in ta dawo zata sanar da ni.
Haka kuwa makociya ta shiga gidan cike da murnar taimakon su Inna ta sanar da Inna komai. Inna tace to gaskiya dai ni bana ma son sai muje muna wata shara a ko wani maida zance. Allah dai na barwa komai Asiya zata dawo amma bansan rana ba wallahi. Makociya ta yi ta kokarin wayar wa da Inna kai amma Inna tace Allah ya zaba abinda yake mafi alkairi.
Ko dan wannan tashin hankali na yan Biñdiga da suka soma kawo hari makotan kauyen nan Asiya dole ki koma gida tun da can komai ya lafa ko kuma ki zauna a kurna. Domin muma kaura zamu yi daga nan zamu tafi Kankiya Baba Tabawa take fadawa Asiya. Asiya tace "Nima na yi tunanin haka amma ji nake gaba daya an cire min Kano a raina sai dai inje dole." Tabawa tace Hakuri za ki yi saidai in zaki bimu hijirar sai mu tafi. Asiya tace haba dai, babu wani abu zuwa gobe sai in koma Kano.
Makociya ta sanar da Hajiya Talatu bayan dawowar Asiya da kwana biyu dan haka suka soma shirya abinda za su aiwatar.
Sulaiman Asiya ta sa Abba ya kira mata. Suka gaisa a soro. Tace kasan abinda ya sa na kira ka Yaya Sulaiman? Yace 'A' a. Tace Ina son inji ko kunyi magana da Abokin ka ne, bansan zaman da nake yi ba har yanzu gara ya bani takarda ta sannan in san matsayin dan ciki na. Ta kai karshen maganar da kuka.
Sulaiman ya ce Kiyi Hakuri wallahi Halifa nima bai daga wayata ba tunda aka shiga wannan kwamacalar yanzu ma ina zaton ya yi Blocking dina ne dan bana samun shi, kawai, ina son Kiyi hakuri zanje har kasuwar su in same shi zuwa kamar karfe biyu. Duk yadda ake ciki zan sanar da ke zuwa magariba.
Tace to Na gode ina son zuwa Asibiti ne amma sai naji inda muka kwana da zancen shi. Yace ba damuwa.
Kamar yadda Sulaiman ya alkawarta haka ya yi. Yaje saidai yaran shagon sun tabbatar masa da cewa Halifa baya kasar kusan wata daya kenan amma suna sa ran dawowar shi cikin satin nan. Ya bukaci lambar da zai same shi. Suka ce ai ba a samun shi sai dai in shine ya kira.
Haka Sulaiman ya sanar da Asiya lokacin da ya shiga gidan bayan magariba. Yace ki kara hakuri nima sai yanzu na huce dana fahimci ashe baya nan ne, kuma gaskiya ko can dama abotarmu bawai ta yi mugun karfin da duk inda zashi sai ya sanar da mu bane. Yana dai son mu ne gaskiya dan kafin mu nemeshi ya nememu ya yi mana alkairi kinga kenan baya nan Anty ta kawo wa Inna yansanda bana tunanin ya sani. Asiya ta sauke Ajiyar zuciya Sannan tace haka ka ke gani? Yace Gaskiya dai haka ne ma ance ya yi wata baya nan su kuma ai ba ayi wata ba. Sannan a iya sanina da Halifa Koda abinda ya faru da gaske ne ba zai sa a kama Inna ba. Asiya tace to Allah ya sa hakan ne. Sulaiman ya kawo kudi dubu goma ya ba Asiya ga wannan kije Asibitin inhar da wata damuwa ki sanar dani. Asiya zata ki amsa ya yi mata tsawa da cewa baya son haka. Ta amsa ta yi godiya. Inna ma ta yi masa godiya. Asiya ta na kwance tana tunani ko da ba gaskiya bane abinda Sulaiman ya fada ta ji sanyi da farin ciki. Allah ya sa su koma zaman su da mijinta tana sonshi sosai.
Asiya da Sadiyan su Maman Annur suka tafi Asibiti tun a gida suke ta shawara suje Asibitin Unguwa ne ko kuwa suje Murtala. Karshe dai suka tafi wani Asibitin kudi amma ba shi da tsada wata mata da suka hau kekenapep ta basu shawara tace ga kula sosai.Sun isa Asibitin nan suka fada mata cewar dubu ishirin ne zata biya har ta haihu, saidai hoton ciki ko magani su siya zata yi. Tace zata fara ba su dubu goma kafin ta haihu sai ta cika, suka ce babu damuwa.
An tabbatar mata ita da abinda ke cikin nata duk suna lafiya domin bugun zuciyar sa daidai, amma an bata takardar da zata yi hoto domin aga yanayi zaman sa. Sadiya ce ta bata kudin hoton domin anyi mata albashinta ba jimawa. Sunce cikin nata watan shi Hudu da sati uku kuma sun saka mata ranar
haihuwa.
Hajiya Talatu da Anty suka shiga duba katuna sun samu masu suna Asiya guda biyu saidai ba za su gane wacce ce ba saboda Anty bata san sunan Baban Asiya ba. Likitan yace ku duba shekarun mana, inhar baku gane nata shekarun ba sai ku bincika sunan Babanta. Sun samu Asiya daya shekaru Talatin dayar sha takwas, dan haka suka gano yar sha takwas din nan dai ita ce suka zo akan ta.
Hajiya Talatu itace ta sanar da Likitan abinda suke bukata suna son a zubda cikin Asiya suna son ya fadi abinda za su bashi.
Ya dan jima yana Nazari Sannan yace "To da farko dai ina mijinta domin bana son in shiga abinda zai bada matsala. Anty tace bata da miji sun rabu sakamakon kamata da ya yi tirmi da tabar ya da wani, to sai ta zo da wannan cikin tace nasa ne, nasan in anje kotun musulinci shi za a bawa cikin nan, ni kuma gaskiya bazan yarda a bashi ciki da ba nasa ba, shine kawai zamu raba gaddamar.
Likitan yace to ba damuwa miliyan daya zaki bani. Anty ta mike tsaye a gigice haba dai kai kuwa milinyan fa da yawa gaskiya yace to baki duba girman laifin da kike son a aikata wadda ta saba da Dokar likitanci akan wannan aikin naki sai a rufe asibitin tare da kwace lasisin Asibitina, ya dan yi shiru gaskiya nama fasa domin aikin yana da hadari sosai.
Hajiya Talatu tace "Kinji matsalar ki ke baki son fidda kudi kuma kina son ayi miki aikin kudi. " Anty tace ke bazaki gane bane, nifa ba nice me kudin ba Halifa ne me kudin rigar alfamar sa ce ke nuna ni ake min kallon kudi. Hajiya Talatu ta kyakyace da dariyar keta, sannan tace To sai ki ta shi mu tunda ba kudi. Anty ta danyi tsai tana tunanin inda zata samar da wannan kudin kai tsaye.
In kawo miki mai sayen ragowar kayan Lefen nan ku karasar da su har akwatunan ki biya bukatar gabanki. Anty ta danyi shiru tana tunanin Anya kuwa Halifa zai yafe mata ta saida masa kayan masu tsada ta hanyar karyar da su kuma ta yi amfani da kudin gurin zubar masa da ciki dan sa. Ta saki murmushin mugunta tare da fadin hakuri zai yi kawai. Ta kalli Talatu shikenan zanje in nemo rabi aiki yana kammala zan cika maka saura.
Asiya taga Anty da Hajiya Talatu sun biyo ta da gudu tana ta boyewa kuma a cikin Asibitin da taje awo. Ta labe a wani daki suna ta neman ta sai taga wani likita ya shigo yace karki damu zan boye ki biyoni. Bayan ta bishi ya boye ta sai kuma ta hango shi ta windor yana magana da su suna tuntsira dariya. Firgugit ta farka ta tashi zaune tana addu"a, tayi hamdala da ta ga mafarki ne, Asiya tana da girmama mafarki, bata yawan yin sa, amma kuma duk lokacin da zata yi shi sai ya zame mata kamar ishara ko nuni zuwa ga wani abu.
Suna karyawa da safe tace wa Maman Annur nifa ina zargin kamar Anty tana bibiyata domin na yi wani mafarki da ya bani tsoro abin ya shafi cikin jikina domin harda Asibitin da mukaje. ta bata labarin mafarkin. "Karki baiwa mafarki muhimmanci. Da Yawan mafarkai shedan ne ki kyautata zato kiyi addua khairan insha Allah.
Halifa ya sauka a filin jirgin sama na Kano da karfe shidda na safe, mota ya dauka kai tsaye ta kai shi gidan sa, sai da yayi bacci ya huta yunwa ta fito dashi, yaje gidan ci abinci ya ci sannan ya sake daukan mai a daidaita sahu zuwa gida. Kiran Baffan sa ya shigo wayarsa, mamaki ya kama shi tunda ya shigo ya maida layinsa yake jin saukar sakwanni tunda ya duba daya biyu babu na Asiya kawai ya fita sabgar su. Ba wanda ya kira shi dan bai fadawa kowa cewar ya dawo ba.
Ya daga cike da girmamawa suka gaisa Baffa yace ashe ka dawo? Halifa yace na dawo tun sassafiya da yake gidana na wuce ko su Anty ba su san na dawo ba. Baffa yace to idan babu damuwa ina son kazo yanzu. To ganinan Insha Allah. Ya saka me a daidaita suka kama hanyar gidan Baffa. Cike da sake sake.