Sashe 57
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abin duniya ya ishi Asiya dole ta nemo hujjar da zata nuna masa tasan me yake yi. Karshe ta yanke shawarar kiran Fati akwai bukatar ta yi magana da ita. Tana ringing Fati ta daga,, Asiya tace Kingane mai magana ? Fati tace .Na gane ki, Asiya ce me miji,. Asiya kanta ya daure, tace bangane Asiya me miji ba Maman Umar ce fa daga Gandun Sarki. Fati tace ke dai nake nufi nima. Asiya tace To ai naji kin kirani da wani suna ne wai Asiya me miji. Fati tace ina dai jinki faɗi abinda ya sa kika kira ni. Asiya ta rasa me zata ce tunda Fati ta Faɗi wannan sunan. Kiyi magana ko in kashe tunda yanzu dai ba a gidanki nake ba bare ki yimin iko.Asiya tace Shikenan na fasa maganar da zan yi miki sai anjima. Fati tace mu jima da yawa, mijine dai kuma nima yanzu sai dai in banso auren shi ba, amma ya zo hannu. Gaban Asiya ya faɗi tace saidai ki nemi naki mijin amma ba nawa ba me zai yi da ke? Fati ta cafke da faɗin duk abinda ya yi da ke shi zai yi da ni.Koda kika kore mu ya zo har gida kuma yana ci gaba da zuwa in kina son ki sheda zance na,ki zo anjima ki ganewa idon ki,in baki bari mun shigo ba, mu zamu zame miki kishiyoyin waje.
Asiya tace Allah ya kiyaye ni mijina ba dan iska bane, babu abinda zai yi dake. Fati ta sa dariya, sai dai kar a kuma ke ma din ai ya fada min ki gudo ne kin dawo gidansa bayan Mahaifiyar ki tana zargin cewa ya sake ki, dan haka kika haihu ba dangin iya bare na Baba munzo mu taimaka miki kuma shine harda cewa mu shirya kin sallame mu, ke ga matar gida. To mun ƙaru ba shakka amma kin bar baya da kura ko ince kin kashe maciji baki sare kan ba.. Git Asiya ta kashe wayarta. Ta zauna cike da bakin cikin abinda Fati ta fada mata, wato dai ta tabbata Halifa yana nema Fati hakan bai isheshi ba har sai ya hada da tona mata asiri. Duk zantukan Fati ba karya a ina zata ji in bai faɗa mata ba.Wata zuciyar tace ki tafi gidan ku kawai ki bar masa gidan sa. Asiya ta shiga hada kayanta da na ɗanta. Babu shakka ta hakura da Halifa in ba haka ba zuciyar ta zata buga. Ta gama komai bata da kudin mota, ko a kafa gara ki tafi. Wata zuciyar ta faɗa mata. Tana kaiwa bakin gate Motar Halifa tana isowa kofar gidan da alamun mantuwa ya yi ya dawo dauka. Cike da mamaki yake kallon Asiya da akwati tana ja. Ta kalle shi rai bace,zantukan Fati suka yi ta zuwa mata. Baice kala ba,ya wuce cikin gidan ta miƙi layin tana tafiya. Ya dakko abinda ya manta ya dawo ya wuceta ya tafi. Asiya cike da mamaki tace kenan ko kallo bata ishe shi ba, bare yace mata ina zata a zaton ta zai tsaya ya yi mata magana daga fara neman matanshi har daraja da kimarta ta zube a idon shi haka?.
Ta tsaya tana tunanin inda zata samu kudin mota domin tasan karya ne taje Fage da kafarta ga goyo ga kaya. Ta karasa gurin wani mai P.O.S dake kan titi tace dan Allah in baka wayata ka bani dubu daya zan kawo maka sai in karba jakar kudin nawa na yarda. Ta sheka masa karya. Wani dake kirga kudi a gefe ya ciro dubu daya ya bata yace je da wayar ki ga wannan saboda Allah. Asiya ta karba ta yi godiya ta kama hanya tana tare mai Adaidaita.
Ta fi minti Talatin kafin ta samu wani da mata biyu a ciki zashi Kurna tace ya sauke ta Kano Gest in. Tun kafin ta shiga taji matar ciki tana yiwa diyarta faɗa. Tana faɗin na fada miki tun ba yau ba ki kauda kai daga abinda Baban su baby yake yi ki yi masa addu'a kika taurare ke bazaki zauna ba yana neman mata, kika dawo gida kika bar masa gidan to gashi in da yana dibansu zuwa Hotel ne yanzu kam kin hutar da shi, tunda makota sun fada miki yana kawo mata gidan aurenki ai gashi zaki koma babu shiri. Inda kina gidan karyarshi ya kawo mace gidan. An fada miki shifa namiji in yana boye miki abu ko kin gane karki nuna kimarki ta sa hakan to gashi dai tun yana zuwa lallashi kinƙi ki koma gashi yanzu zaki koma bayan ya watsar da ke. Asiya taji kamar wani karatu ake yi mata, kenan shima Halifa zai iya kawo su gidan hankalin sa kwance motarsa da gilashi baƙi ya wuce da mace ya fito da ita ba tare da an sani ba. Kuma babu tabbacin zai biyota ko ya gyara kuskuren sa,tunda gashi a gabanta ya wuce ko ajikin shi,ran nan da tace zata tafi ai lallashinta ya yi da ban baki, amma yau dubi yadda ya watsar da ita. Ba shakka ance in ka rasa uwar da zata yi maka fada,to ka saurari faɗan da wata uwar zata yi wa ɗanta sai ka dauka kai ya yi maka amfani. Wadda ake yi wa faɗan tace "Ni wallahi dan Baba ya ki ne, da kawai takarda ta ya bani yanzu gashi duk makota sunsan abinda ya aikata.Uwar tace ki fada min waye ya ja? Kece nan tun farko me ya kaiki bincike da saka masa ido. Allah ya hana bin diddigi.Kika kwafe ki duba masa waya ki bibiye shi har sai da kika ga no tashin hankali tun lokacin har zuwa yau wace ribar kika ci? Bayan da kuna zaune lafiya abin shi awa.
Me a daidaita ya karbe zancen da faɗin Babata in saka muku baki? " Ya ci gaba kanwata baki san me yake faruwa ba a wannan zamanin mu da muke jan Adaidaita mun san komai, mata ne suke neman maza yanzu, in har kika yi sakwasakwa da mijinki wata ce kawai zata samu ta yi ta masa abinda ke bazaki iya yi masa ba,wasu fa harda kuɗi suke kashewa maza,wasu malamai suke shiga. Shaiɗan fa da kika gani babu abunda yake so irin ya girgide auren sunna,dan haka ki koma gidan ki ki rike mijinki kici gaba da addu'a. Ki fita batun yan unguwa su aka san me mazan su ke aikatawa sanin na Allah ai sai Allah ko malami karyar sa yace miki ga na Allah
Sam Asiya bata san anzo Kano Gest ba sai da mai Adaidaita ya dakata yace munzo Ta sauka ta bashi dari biyar ta tsallaka ta kuma tare wata ta hau zuwa gandun Sarki. Domin dai ta wadatu da faɗan da aka yiwa yarinyar nan. Ta dawo ta bude gidanta ta shiga. Ta kwantar da ɗanta a kujera sannan ta koma gefe ta zabga tagumi dole ta sake kiran Anty Halima da alamu dai shawarar nan ta ta itace mafita.
Take ta kira bayan sun gaisa ta zayyana mata dukkan abinda ya faru a tsakanin su. Dariya ta ji Anty Halima tana yi.Haushi ya kamata kamar ta kashe amma saita share ta ci gaba da fadin Anty abin dariya aka yi? E mana abin dariya ne, ace wai kin tafi kuma kin dawo.Na faɗa miki fa,duk abinda zai yi karki nuna kin gane,baki ga abinda Baby ta cikin Hamshakiyar uwa ta yi ba? Ki karanta littafin zaki samu Illimin zama da miji me neman mata, naki mijin sabon shiga ne,kuma ke kike kara rura wutar dan haka ki nutsu in ya dawo ki bashi hakuri karma ki nuna kinyi waya da wannan yarinyar karki masa zanceta sam sam. Ki daure kishi da zafi musamman da matar waje amma Allah yana saurin amsar addu'ar wanda ke cikin damuwa.
Asiya ta yi wanka ta gyara jikinta sosai ta yi kwalliya tsaf. Zan tukan Fati suna ɓata mata rai in ta tuna.
Saidai kuma Halifa bai dawo ba sai sha biyu saura. Ran Asiya ya sosu amma ta dake ta zauna a falo. Ya sa makulli ya bude kofar falon dan bai zaci tana nan ba.
Ya shigo yana waya abinda taji kawai shine, dadin baki kawai ki ke yi min, domin yaushe rabon da ki nemeni amma ni yau gashi na kiraki da..... Maganar ta tsaya cak ganin Asiya ta zuba masa ido. Cikin yanayi irin na mara gaskiya yace zan kira ki da safe, barista zan kira. Bai jira me zata faɗa ba, ya kashe wayar.
Asiya ta daure ta kalle shi sannu da zuwa. Ya dube ta da in ina ya ce yaw wa, ya sa kai ciki, ta bishi yana cire kayan jikin shi ta iso dab dashi,in ka yi wanka akwai abinci. Ta fada tana kokarin ƙaƙaro fara a. "A koshe na ke, ya karkace wai dan kar ya taɓa jikinta ya nufi banɗaki.
Asiya ta rumtse idon ta zuciyar ta ta soma tuna mata da maganarsu da Fati, ina ma ace ta yi recoding din ta yana fitowa ta kunna masa ya san ta san komai.
Zuciyar ta tace ki hakura kawai. Wata zuciyar tace, kar ki hakura ki faɗa masa komai da zaran ya fito ki kunyata shi. Tana zaune bakin gado. Ya fito yana shafa turare ya yi wanka.Yana mata kwarjini ne amma ta daure tace Yaya ina son magana da kai.
'Bisimillahi " Ya faɗa lokacin da ya dauki filo zai fita kenan. Yaya dan Allah ban hana ka soyayya da kowa ba amma dan Allah kar ka kara faɗawa wata sirrina. Ga mamakin ta sai taji yace 'To' ya sa kai zai fita. Tace Yaya amma me yasa ka rasa wadda zaka nema sai Fati me mana aiki? Har ya kama kofa zai murda sai ya tsaya cak bai waiwayo ba, ganin ta fara kama shi sai ta ci gaba da faɗin kuma neman na na lalacewa har kai ne zaka dauki mace Yaya zuwa Hotel dan ka.....
Asiya tace Allah ya kiyaye ni mijina ba dan iska bane, babu abinda zai yi dake. Fati ta sa dariya, sai dai kar a kuma ke ma din ai ya fada min ki gudo ne kin dawo gidansa bayan Mahaifiyar ki tana zargin cewa ya sake ki, dan haka kika haihu ba dangin iya bare na Baba munzo mu taimaka miki kuma shine harda cewa mu shirya kin sallame mu, ke ga matar gida. To mun ƙaru ba shakka amma kin bar baya da kura ko ince kin kashe maciji baki sare kan ba.. Git Asiya ta kashe wayarta. Ta zauna cike da bakin cikin abinda Fati ta fada mata, wato dai ta tabbata Halifa yana nema Fati hakan bai isheshi ba har sai ya hada da tona mata asiri. Duk zantukan Fati ba karya a ina zata ji in bai faɗa mata ba.Wata zuciyar tace ki tafi gidan ku kawai ki bar masa gidan sa. Asiya ta shiga hada kayanta da na ɗanta. Babu shakka ta hakura da Halifa in ba haka ba zuciyar ta zata buga. Ta gama komai bata da kudin mota, ko a kafa gara ki tafi. Wata zuciyar ta faɗa mata. Tana kaiwa bakin gate Motar Halifa tana isowa kofar gidan da alamun mantuwa ya yi ya dawo dauka. Cike da mamaki yake kallon Asiya da akwati tana ja. Ta kalle shi rai bace,zantukan Fati suka yi ta zuwa mata. Baice kala ba,ya wuce cikin gidan ta miƙi layin tana tafiya. Ya dakko abinda ya manta ya dawo ya wuceta ya tafi. Asiya cike da mamaki tace kenan ko kallo bata ishe shi ba, bare yace mata ina zata a zaton ta zai tsaya ya yi mata magana daga fara neman matanshi har daraja da kimarta ta zube a idon shi haka?.
Ta tsaya tana tunanin inda zata samu kudin mota domin tasan karya ne taje Fage da kafarta ga goyo ga kaya. Ta karasa gurin wani mai P.O.S dake kan titi tace dan Allah in baka wayata ka bani dubu daya zan kawo maka sai in karba jakar kudin nawa na yarda. Ta sheka masa karya. Wani dake kirga kudi a gefe ya ciro dubu daya ya bata yace je da wayar ki ga wannan saboda Allah. Asiya ta karba ta yi godiya ta kama hanya tana tare mai Adaidaita.
Ta fi minti Talatin kafin ta samu wani da mata biyu a ciki zashi Kurna tace ya sauke ta Kano Gest in. Tun kafin ta shiga taji matar ciki tana yiwa diyarta faɗa. Tana faɗin na fada miki tun ba yau ba ki kauda kai daga abinda Baban su baby yake yi ki yi masa addu'a kika taurare ke bazaki zauna ba yana neman mata, kika dawo gida kika bar masa gidan to gashi in da yana dibansu zuwa Hotel ne yanzu kam kin hutar da shi, tunda makota sun fada miki yana kawo mata gidan aurenki ai gashi zaki koma babu shiri. Inda kina gidan karyarshi ya kawo mace gidan. An fada miki shifa namiji in yana boye miki abu ko kin gane karki nuna kimarki ta sa hakan to gashi dai tun yana zuwa lallashi kinƙi ki koma gashi yanzu zaki koma bayan ya watsar da ke. Asiya taji kamar wani karatu ake yi mata, kenan shima Halifa zai iya kawo su gidan hankalin sa kwance motarsa da gilashi baƙi ya wuce da mace ya fito da ita ba tare da an sani ba. Kuma babu tabbacin zai biyota ko ya gyara kuskuren sa,tunda gashi a gabanta ya wuce ko ajikin shi,ran nan da tace zata tafi ai lallashinta ya yi da ban baki, amma yau dubi yadda ya watsar da ita. Ba shakka ance in ka rasa uwar da zata yi maka fada,to ka saurari faɗan da wata uwar zata yi wa ɗanta sai ka dauka kai ya yi maka amfani. Wadda ake yi wa faɗan tace "Ni wallahi dan Baba ya ki ne, da kawai takarda ta ya bani yanzu gashi duk makota sunsan abinda ya aikata.Uwar tace ki fada min waye ya ja? Kece nan tun farko me ya kaiki bincike da saka masa ido. Allah ya hana bin diddigi.Kika kwafe ki duba masa waya ki bibiye shi har sai da kika ga no tashin hankali tun lokacin har zuwa yau wace ribar kika ci? Bayan da kuna zaune lafiya abin shi awa.
Me a daidaita ya karbe zancen da faɗin Babata in saka muku baki? " Ya ci gaba kanwata baki san me yake faruwa ba a wannan zamanin mu da muke jan Adaidaita mun san komai, mata ne suke neman maza yanzu, in har kika yi sakwasakwa da mijinki wata ce kawai zata samu ta yi ta masa abinda ke bazaki iya yi masa ba,wasu fa harda kuɗi suke kashewa maza,wasu malamai suke shiga. Shaiɗan fa da kika gani babu abunda yake so irin ya girgide auren sunna,dan haka ki koma gidan ki ki rike mijinki kici gaba da addu'a. Ki fita batun yan unguwa su aka san me mazan su ke aikatawa sanin na Allah ai sai Allah ko malami karyar sa yace miki ga na Allah
Sam Asiya bata san anzo Kano Gest ba sai da mai Adaidaita ya dakata yace munzo Ta sauka ta bashi dari biyar ta tsallaka ta kuma tare wata ta hau zuwa gandun Sarki. Domin dai ta wadatu da faɗan da aka yiwa yarinyar nan. Ta dawo ta bude gidanta ta shiga. Ta kwantar da ɗanta a kujera sannan ta koma gefe ta zabga tagumi dole ta sake kiran Anty Halima da alamu dai shawarar nan ta ta itace mafita.
Take ta kira bayan sun gaisa ta zayyana mata dukkan abinda ya faru a tsakanin su. Dariya ta ji Anty Halima tana yi.Haushi ya kamata kamar ta kashe amma saita share ta ci gaba da fadin Anty abin dariya aka yi? E mana abin dariya ne, ace wai kin tafi kuma kin dawo.Na faɗa miki fa,duk abinda zai yi karki nuna kin gane,baki ga abinda Baby ta cikin Hamshakiyar uwa ta yi ba? Ki karanta littafin zaki samu Illimin zama da miji me neman mata, naki mijin sabon shiga ne,kuma ke kike kara rura wutar dan haka ki nutsu in ya dawo ki bashi hakuri karma ki nuna kinyi waya da wannan yarinyar karki masa zanceta sam sam. Ki daure kishi da zafi musamman da matar waje amma Allah yana saurin amsar addu'ar wanda ke cikin damuwa.
Asiya ta yi wanka ta gyara jikinta sosai ta yi kwalliya tsaf. Zan tukan Fati suna ɓata mata rai in ta tuna.
Saidai kuma Halifa bai dawo ba sai sha biyu saura. Ran Asiya ya sosu amma ta dake ta zauna a falo. Ya sa makulli ya bude kofar falon dan bai zaci tana nan ba.
Ya shigo yana waya abinda taji kawai shine, dadin baki kawai ki ke yi min, domin yaushe rabon da ki nemeni amma ni yau gashi na kiraki da..... Maganar ta tsaya cak ganin Asiya ta zuba masa ido. Cikin yanayi irin na mara gaskiya yace zan kira ki da safe, barista zan kira. Bai jira me zata faɗa ba, ya kashe wayar.
Asiya ta daure ta kalle shi sannu da zuwa. Ya dube ta da in ina ya ce yaw wa, ya sa kai ciki, ta bishi yana cire kayan jikin shi ta iso dab dashi,in ka yi wanka akwai abinci. Ta fada tana kokarin ƙaƙaro fara a. "A koshe na ke, ya karkace wai dan kar ya taɓa jikinta ya nufi banɗaki.
Asiya ta rumtse idon ta zuciyar ta ta soma tuna mata da maganarsu da Fati, ina ma ace ta yi recoding din ta yana fitowa ta kunna masa ya san ta san komai.
Zuciyar ta tace ki hakura kawai. Wata zuciyar tace, kar ki hakura ki faɗa masa komai da zaran ya fito ki kunyata shi. Tana zaune bakin gado. Ya fito yana shafa turare ya yi wanka.Yana mata kwarjini ne amma ta daure tace Yaya ina son magana da kai.
'Bisimillahi " Ya faɗa lokacin da ya dauki filo zai fita kenan. Yaya dan Allah ban hana ka soyayya da kowa ba amma dan Allah kar ka kara faɗawa wata sirrina. Ga mamakin ta sai taji yace 'To' ya sa kai zai fita. Tace Yaya amma me yasa ka rasa wadda zaka nema sai Fati me mana aiki? Har ya kama kofa zai murda sai ya tsaya cak bai waiwayo ba, ganin ta fara kama shi sai ta ci gaba da faɗin kuma neman na na lalacewa har kai ne zaka dauki mace Yaya zuwa Hotel dan ka.....