Sashe 59
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asiya ta furta cike da son a bar maganar. Ta ci gaba da fa ɗin Ina Abba da Su Annur Maman Annur tana zuwa gidan aikin ta kuwa? Inna tace Tana zuwa kullum dai ita ma tana cikin damuwa da kewa amma ta kusa daina aikin ma. Abba kuma jiya muka dawo daga Asibiti. ‘Bashi da lafiya ne? Sadiya ta katse Inna.
Sulaiman ya yi karaf ya ce ai ya samu sauki ma. Asiya ta yi shiru tana tunanin kamar akwai wata matsala game da Abba.Har suka isa gida.
Sulaiman ya kira Inna gefe yace kar ki yi mata zancan Abba tun da dai shi bai fada mata ba. Kinsan dai tana da ruɗewa Inna tace shike nan. Ya kira Asiya itama yace, kar ki fada wa Inna matsalar mijinki kin san dai har yanzu ba a warware wata matsalar ba sannan ban da haka kuma Inna tana da wuyar fahimta . Asiya tace shike nan.
Ga mamakin Asiya sai ta ga sun zo wani gida wanda ba gidan su ba, dan madaidaici mai kyau ba ginin kasa ba kamar na su. Ta cika da mamaki tana kallon Inna, “Nan kuka dawo Inna?” Tace Nan muka dawo bamu jima ba.Sadiya taji tsaiwar mota ta bude gidan ta fito da gudu tana fadin Asiya ! Asiya tace
Maman Annur Suka rungume Juna Sadiya tana murna ta amshi jariri tana kallo ranar har ukun dare suna hira kafin kowa ya kwanta. Inna ta sauka a ɗan gadon ta tace ki kwanta ke da ɗan na ki. Asiya tace a a Inna shima ya kwanta a ƙasan dan ya saba. Inna ta amshe shi tana fadin kawo shi mu kwanta in ya farka kya tashi ki bashi ya sha. Asiya cike da farin ciki ta kwanta iyaye daban ne ta ayyana a zuciyarta. Sai dai fa kogin tunani ta fada maimakon bacci rayuwa baza ta yiwu mata ba babu Halifa ba haka kuma akan kunnen ta aka kira salla dan haka ta tashi ta fita ta tayo alwala tabi gidan da kallo ko ya akayi su Inna suka dawo nan gidan Mai kyau ga tayas ko ina ga ruwa daki uku ne da Siti rum da safe dai taji yadda aka samu gidan. Ta zo tana nafila, motsinta ya tada Inna ta ce baki tashe ni ba na makara koda yake bamu kwanta da wuri ba Asiya tace shiyasa na barki amma ba'a shiga salla ba har zakiyi raka atanil fijir. Inna ta fita tana fadin Asiya dan naki bashi da rigima.
Tana idar da salla bacci mai nauyi ya dauke ta Kuka ɗanta ya tashe ta, taga Inna ta rufo kofa tana mishi wanka. Ta bisu da kallo cikin farin ciki tace “Inna a ina kuka samo robar wanka?
Inna tace a makota na aika aka karbo min. Asiya ta gaida Inna ta tashi ta nufi tsakar gida ta wanke baki Sadiya tana hada abin kari kunu da dumamen shinkafa. Asiya tace maman Annur sai ga ku a sabon gida, wai ya akayi ne? Sadiya tace Hummm wallahi kuwa tun daga abin Abba Halifa ya dawo da mu nan ko bai fada miki ba? Asiya cike da rashin fahimta tace ban gane ba.
Inna ta kwaɗawa Asiya kira ta amshi ɗanta yana ta ragsa kuka. Inna tana faɗin zauna ki bashi ai yana da hakuri tun jiya bai farka ba. Ta zauna tana bashi, tace ai bai cika tashin dare ba, . Inna tace. Wai kuwa me ya hada ku da Mijin naki har ya mare ki? Lamarin fa ya tsaya min a rai. Bana son auren duka.
Asiya ta yi shiru tana tunani ta ina zata dakko maganar. Inna tace “Ban tsanan ta sai kin fada min ba amma aure da duka Asiya ba zai yiwu ba dan haka shi yasa tun jiyan bance komai ba da yace mu taho.
Sallamar Sadiya ce ta dakatar da Inna , ta kawo musu abin kari, Abba ya shigo yana gaida su Asiya ta bishi da kallo ya dashe ya rame cike da mamaki Asiya tace Inna “Me ya samu Abba haka?” Sadiya cike da mamaki tace wai baki sani ba? Asiya tace “Maman Annur in har na sani bazan tambaye ki ba. Inna tace Wai kina mufin shi Halifa bai sanar da ke komai ba?
Sallamar Sulaiman ce ta katse su.Ya shigo Halifa yana bayan sa. Sadiya ta yi musu shinfida suka zauna Halifa ya gaida Inna ko inda Asiya take bai kalla ba bare ɗanta. Ya amsa gaisuwar Sadiya. Sadiya ta miko musu ɗan sai Sulaiman ne ya amshe shi Halifa dai a fusace yake har Wannan lokacin Asiya ta dake domin zuciyar ta
ta fada mata cewa ta dake kawai Yanzu lokaci ne na kwatar yanci kodai ya tuba nan gaban Inna akan bazai ƙara ba, kokuma ta haƙura da shi domin sai ta fallasa shi.
Halifa ya katse ma Asiya tunani da faɗin Inna kamar yadda na fada jiya na mari Asiya har ture ta na yi domin har sai da ta yi habo wannan tabbas na aikata shi. To amma ko zata iya fada miki abinda ya jawo hakan? Asiya ta kalle shi cike da mamaki wannan yana nufin baima damu ba da abinda ya aikata. Yanzu har ya kai ba zai iya boye zunubin shi ba.Ya katse mata tunani bance ki rufamin asiri ba fa, nan gurin babu bakon ki mahaifiyar ki ce da yar ki, Sulaiman ma kamar wane a gareki dan haka karma ki tsaya boye komai.
Kawai ki tona shi zuciyar ta ta faɗa mata haka.
Asiya ta kalli Inna wadda yanayinta ya canza tunda Halifa ya ambaci cewa ya dake ta. Ko mutuwa ance tana jin kunyar idon mahaifi amma Halifa kamar yana gadara da ya dake ta. Tace ‘Inna ki yi hakuri ki yafe min har da alhakin ki na gudu na tafi Gurin Halifa ashe ban sani ba ya canza daga Halifan da na sani.
Da na haihu ya kawo min wata Dattijuwa mai suna Hajjo ita da jikarta sai jikar ta fara nuna tana son shi, sai kuma wai ya biye mata. Har na kore su shine kuma ya ci gaba da kulata. Ya ma kama fa kulakulen mata shine har dayan dare sha biyu ba zai dawo gida ba gashi bani da sirri gurin matan Duk ya fada musu wai na gudo ne na dawo gurin sa. Ta kai karshen maganar da fashewa da kuka. Cikin kuka taci gaba da fadin wai dan na masa maganar ya daina jiya shine ya dake ni wai kuma zai sake ni.
Idanun Halifa suka kada suka yi ja ya kalli Inna bazai iya fassara me take tunani ba. Dakin ya yi tsit sai kuka Asiya. “In kare kai na ko kawai Inna ta yanke hukunci? Halifa ya tambaya cike da bacin rai. Sadiya ta yi saurin fadin Ka kare kanka shine adalci Sulaiman yace Ka yi maganar ka aboki na.
Halifa yace “Lokacin da na fahimci cewa Sulaiman ya gama yi min kokari Inna ta gane gaskiya ba ni ne na saki yarinyar nan ba, sai na fara kokarin yadda zan kawo ainihin wadda ta yi laifin ta fada a gaban Inna da kanta kuma in yi musu ba zata daga Antyn nawa har Inna wato in kawo musu Asiya da ɗanta su san tana cikin koshin lafiya.
Katsam sai wani tashin hankalin ya samu Anty an mata kishiya a boye,dan haka na jinkirta, nan ita kuma wannan yarinyar naga ta soma damuwa da harkar masu mata aiki tana bay yana kishinta har da korar su. Duk ban damu ba har gida naje na basu hakuri na kuma biya su hakkin su,gata nan ko faɗa ban mata ba tunda nasan ina da fushi Sosai.
Ranar da da na lura ta soma bata rai game da gida ta damu da son ganin ku sai na yanke shawarar in zo in sanar da Inna Asiya tana gurina kuma in tafi da su Innar can gurinta.
Sai da na fara duba Sulaiman a shago baya nan sannan na nufo gidan ni daya, tun daga nesa na hango mutane cike a layin sai na yi tunani in juya domin gaskiya bana zuwa inda duk ake fada.
Muryar Sulaiman na jiyo yana cewa ba zai yiwu a bashi hakuri ba, dan yana ganin ba su da wanda zai tsaya musu.
Kawai sai na koma ashe rigimar a gidan su Inna ce. Naje na dafa Sulaiman ina tambayar shi, abinda ke faruwa sai na ji Yayi hamdala yana fadin ga me tsaya musu ya zo.
Na tambaye shi abinda ke faruwa sai ya nuna wani mutum yana tsaye sanye da jallabiyya fara yace “Ga wanda ya dake su kuma wai kar su yi kuka, ya samu yara ya lalata su kuma Abba da ya tona asiri bayan ya haike masa shine ya zo yana fuffka zai kai kara.
Na kalle shi cike da mamaki ban gane ya haike musu ba su da ba mata ba. Halifa yace mazan fa kuma yara kanana kowa ya sani a layin nan an kasa yi masa magana dan yana da abin hannu.
Bansan lokacin da na zabga wa uwar sa zagi ba, nace za a kai yaro Asibiti in ya tabbata wallahi sai kaje gidan yari. Saboda ƙarfin hali wai ya taso zai mare ni, ni kuwa na dinga jibgarsa sai da naga baya motsi sannan na kyale shi.
Muna Asibiti aka tabbatar an haike wa Abba Sai da aka yi masa karamar tiyata. Yan sanda suka zo suka same ni a Asibiti suka tafi dani wai ana za ton Mutumin ya mutu ne.
Na kira Yaya Bashir Babanmu daya shine mataimakin Kwamishina na faɗa mishi halin da ake ciki take ya kira DPO yace ni kanin sane ya na son case din ya koma hannun sa dan haka akai ni can yanzu.
Sulaiman ya yi karaf ya ce ai ya samu sauki ma. Asiya ta yi shiru tana tunanin kamar akwai wata matsala game da Abba.Har suka isa gida.
Sulaiman ya kira Inna gefe yace kar ki yi mata zancan Abba tun da dai shi bai fada mata ba. Kinsan dai tana da ruɗewa Inna tace shike nan. Ya kira Asiya itama yace, kar ki fada wa Inna matsalar mijinki kin san dai har yanzu ba a warware wata matsalar ba sannan ban da haka kuma Inna tana da wuyar fahimta . Asiya tace shike nan.
Ga mamakin Asiya sai ta ga sun zo wani gida wanda ba gidan su ba, dan madaidaici mai kyau ba ginin kasa ba kamar na su. Ta cika da mamaki tana kallon Inna, “Nan kuka dawo Inna?” Tace Nan muka dawo bamu jima ba.Sadiya taji tsaiwar mota ta bude gidan ta fito da gudu tana fadin Asiya ! Asiya tace
Maman Annur Suka rungume Juna Sadiya tana murna ta amshi jariri tana kallo ranar har ukun dare suna hira kafin kowa ya kwanta. Inna ta sauka a ɗan gadon ta tace ki kwanta ke da ɗan na ki. Asiya tace a a Inna shima ya kwanta a ƙasan dan ya saba. Inna ta amshe shi tana fadin kawo shi mu kwanta in ya farka kya tashi ki bashi ya sha. Asiya cike da farin ciki ta kwanta iyaye daban ne ta ayyana a zuciyarta. Sai dai fa kogin tunani ta fada maimakon bacci rayuwa baza ta yiwu mata ba babu Halifa ba haka kuma akan kunnen ta aka kira salla dan haka ta tashi ta fita ta tayo alwala tabi gidan da kallo ko ya akayi su Inna suka dawo nan gidan Mai kyau ga tayas ko ina ga ruwa daki uku ne da Siti rum da safe dai taji yadda aka samu gidan. Ta zo tana nafila, motsinta ya tada Inna ta ce baki tashe ni ba na makara koda yake bamu kwanta da wuri ba Asiya tace shiyasa na barki amma ba'a shiga salla ba har zakiyi raka atanil fijir. Inna ta fita tana fadin Asiya dan naki bashi da rigima.
Tana idar da salla bacci mai nauyi ya dauke ta Kuka ɗanta ya tashe ta, taga Inna ta rufo kofa tana mishi wanka. Ta bisu da kallo cikin farin ciki tace “Inna a ina kuka samo robar wanka?
Inna tace a makota na aika aka karbo min. Asiya ta gaida Inna ta tashi ta nufi tsakar gida ta wanke baki Sadiya tana hada abin kari kunu da dumamen shinkafa. Asiya tace maman Annur sai ga ku a sabon gida, wai ya akayi ne? Sadiya tace Hummm wallahi kuwa tun daga abin Abba Halifa ya dawo da mu nan ko bai fada miki ba? Asiya cike da rashin fahimta tace ban gane ba.
Inna ta kwaɗawa Asiya kira ta amshi ɗanta yana ta ragsa kuka. Inna tana faɗin zauna ki bashi ai yana da hakuri tun jiya bai farka ba. Ta zauna tana bashi, tace ai bai cika tashin dare ba, . Inna tace. Wai kuwa me ya hada ku da Mijin naki har ya mare ki? Lamarin fa ya tsaya min a rai. Bana son auren duka.
Asiya ta yi shiru tana tunani ta ina zata dakko maganar. Inna tace “Ban tsanan ta sai kin fada min ba amma aure da duka Asiya ba zai yiwu ba dan haka shi yasa tun jiyan bance komai ba da yace mu taho.
Sallamar Sadiya ce ta dakatar da Inna , ta kawo musu abin kari, Abba ya shigo yana gaida su Asiya ta bishi da kallo ya dashe ya rame cike da mamaki Asiya tace Inna “Me ya samu Abba haka?” Sadiya cike da mamaki tace wai baki sani ba? Asiya tace “Maman Annur in har na sani bazan tambaye ki ba. Inna tace Wai kina mufin shi Halifa bai sanar da ke komai ba?
Sallamar Sulaiman ce ta katse su.Ya shigo Halifa yana bayan sa. Sadiya ta yi musu shinfida suka zauna Halifa ya gaida Inna ko inda Asiya take bai kalla ba bare ɗanta. Ya amsa gaisuwar Sadiya. Sadiya ta miko musu ɗan sai Sulaiman ne ya amshe shi Halifa dai a fusace yake har Wannan lokacin Asiya ta dake domin zuciyar ta
ta fada mata cewa ta dake kawai Yanzu lokaci ne na kwatar yanci kodai ya tuba nan gaban Inna akan bazai ƙara ba, kokuma ta haƙura da shi domin sai ta fallasa shi.
Halifa ya katse ma Asiya tunani da faɗin Inna kamar yadda na fada jiya na mari Asiya har ture ta na yi domin har sai da ta yi habo wannan tabbas na aikata shi. To amma ko zata iya fada miki abinda ya jawo hakan? Asiya ta kalle shi cike da mamaki wannan yana nufin baima damu ba da abinda ya aikata. Yanzu har ya kai ba zai iya boye zunubin shi ba.Ya katse mata tunani bance ki rufamin asiri ba fa, nan gurin babu bakon ki mahaifiyar ki ce da yar ki, Sulaiman ma kamar wane a gareki dan haka karma ki tsaya boye komai.
Kawai ki tona shi zuciyar ta ta faɗa mata haka.
Asiya ta kalli Inna wadda yanayinta ya canza tunda Halifa ya ambaci cewa ya dake ta. Ko mutuwa ance tana jin kunyar idon mahaifi amma Halifa kamar yana gadara da ya dake ta. Tace ‘Inna ki yi hakuri ki yafe min har da alhakin ki na gudu na tafi Gurin Halifa ashe ban sani ba ya canza daga Halifan da na sani.
Da na haihu ya kawo min wata Dattijuwa mai suna Hajjo ita da jikarta sai jikar ta fara nuna tana son shi, sai kuma wai ya biye mata. Har na kore su shine kuma ya ci gaba da kulata. Ya ma kama fa kulakulen mata shine har dayan dare sha biyu ba zai dawo gida ba gashi bani da sirri gurin matan Duk ya fada musu wai na gudo ne na dawo gurin sa. Ta kai karshen maganar da fashewa da kuka. Cikin kuka taci gaba da fadin wai dan na masa maganar ya daina jiya shine ya dake ni wai kuma zai sake ni.
Idanun Halifa suka kada suka yi ja ya kalli Inna bazai iya fassara me take tunani ba. Dakin ya yi tsit sai kuka Asiya. “In kare kai na ko kawai Inna ta yanke hukunci? Halifa ya tambaya cike da bacin rai. Sadiya ta yi saurin fadin Ka kare kanka shine adalci Sulaiman yace Ka yi maganar ka aboki na.
Halifa yace “Lokacin da na fahimci cewa Sulaiman ya gama yi min kokari Inna ta gane gaskiya ba ni ne na saki yarinyar nan ba, sai na fara kokarin yadda zan kawo ainihin wadda ta yi laifin ta fada a gaban Inna da kanta kuma in yi musu ba zata daga Antyn nawa har Inna wato in kawo musu Asiya da ɗanta su san tana cikin koshin lafiya.
Katsam sai wani tashin hankalin ya samu Anty an mata kishiya a boye,dan haka na jinkirta, nan ita kuma wannan yarinyar naga ta soma damuwa da harkar masu mata aiki tana bay yana kishinta har da korar su. Duk ban damu ba har gida naje na basu hakuri na kuma biya su hakkin su,gata nan ko faɗa ban mata ba tunda nasan ina da fushi Sosai.
Ranar da da na lura ta soma bata rai game da gida ta damu da son ganin ku sai na yanke shawarar in zo in sanar da Inna Asiya tana gurina kuma in tafi da su Innar can gurinta.
Sai da na fara duba Sulaiman a shago baya nan sannan na nufo gidan ni daya, tun daga nesa na hango mutane cike a layin sai na yi tunani in juya domin gaskiya bana zuwa inda duk ake fada.
Muryar Sulaiman na jiyo yana cewa ba zai yiwu a bashi hakuri ba, dan yana ganin ba su da wanda zai tsaya musu.
Kawai sai na koma ashe rigimar a gidan su Inna ce. Naje na dafa Sulaiman ina tambayar shi, abinda ke faruwa sai na ji Yayi hamdala yana fadin ga me tsaya musu ya zo.
Na tambaye shi abinda ke faruwa sai ya nuna wani mutum yana tsaye sanye da jallabiyya fara yace “Ga wanda ya dake su kuma wai kar su yi kuka, ya samu yara ya lalata su kuma Abba da ya tona asiri bayan ya haike masa shine ya zo yana fuffka zai kai kara.
Na kalle shi cike da mamaki ban gane ya haike musu ba su da ba mata ba. Halifa yace mazan fa kuma yara kanana kowa ya sani a layin nan an kasa yi masa magana dan yana da abin hannu.
Bansan lokacin da na zabga wa uwar sa zagi ba, nace za a kai yaro Asibiti in ya tabbata wallahi sai kaje gidan yari. Saboda ƙarfin hali wai ya taso zai mare ni, ni kuwa na dinga jibgarsa sai da naga baya motsi sannan na kyale shi.
Muna Asibiti aka tabbatar an haike wa Abba Sai da aka yi masa karamar tiyata. Yan sanda suka zo suka same ni a Asibiti suka tafi dani wai ana za ton Mutumin ya mutu ne.
Na kira Yaya Bashir Babanmu daya shine mataimakin Kwamishina na faɗa mishi halin da ake ciki take ya kira DPO yace ni kanin sane ya na son case din ya koma hannun sa dan haka akai ni can yanzu.