Sashe 30
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maganar Sulaiman. ce ta ke neman tabbata, yayan makota suka. soma shigowa daga nan sai iyayen sai kuma ga wani gida radio wai sun zo jin ta bakin Asiya. Ta kulle kanta adaki. Dole Asiya tabi duhun magriba ta tafi gidan wata yar Uwar su a Kurna ta kwana washe gari ta yi asubanci hanyar Malumfashi dangin Innar su.....
*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/29, 21:25] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w
Ga zaton ta barawo aka kama, ta dubi Halifa ta ce a ina ya yi sata? Kafin Halifa ya bata amsa sai taji barawo na cewa Dan Allah ku yi hakuri wallahi sai da nace wa Asi baby kawai ta zo inda muka saba haduwa gidan abokina wanda ya rabu da matarsa can take zuwa idan Halifa ya tafi kasuwa, to da yake ina zuwa wasu lokutan a nan idan ya fita yauma wallahi na musa amma tace yanayin jikinta ya sa ta kasa...... Halifa ya sa kafa ya tokari cikin sa, sai da ya yi kara sannan jini ta hanci ta baki aka rike Halifa yana fizgewa akan cewa a sake shi sai ya kashe shi. Sai lokacin Asiya ta fahimci sharrin da aka yi mata ta daga ido ta kalli Anty sai ta saki wani murmushi irin na takaici. Tace tanan aka sake bullo min? Ta je gaban mutumin ta kalle shi. Ina son ka fadi tsakanin ka da Allah ka taba ganina? Ya fashe da kuka tare da fadin Asiya kalli ki gani kefa ki ka ce inzo gidan ki ke kika ce mijin ya tafi kasuwa amma shine kike alaye kamar baki san komai ba. Zufa ta karyo wa Asiya lallai sun tsara abin su. Ta kalli Halifa Dan Allah Yaya kar ka yarda da shi wallahi ban san shiba.
Anty tace amma wannan yazo gidan nan ba so daya ba akwai ranar da na ta tambaye shi ya ce min yayanku ne, to amma ganin yadda in ya fito yake sanda shiyasa na kasa yarda da shi. Halifa wanda takaici ya hana shi magana ya fidda hannu ya wanka wa Asiya mari yace kinsan tin yaushe nake a gidan nan tun ina fita kasuwa Anty ta kira ni tace ga wani ya zo tana ganin shi yana yawan zuwa, har nace kila Dan Uwa ku ne sai kuma na kasa nutsuwa kasancewar yadda mata suka koma a wanna zamanin. Nayi awa daya ina jiran fitowar shi sannan ya fito daga dakin mu dakin auren mu Asiya yana gyara wando ya dakko takalmanshi a inda ya boye ya saka ina Kallon shi ba zan iya barin shi ya fita ba, ni ne nayi masa wannan dukan. Sai Halifa ya fashe da kuka. Asiya cikin firgici da tashin hankali, ta kama hannun shi tace "Yaya kar ka yarda wallahi wannan shiryayyen al amari ne ka yi tunani sosai wallahi ni bacci nake ina kwance a dakina wannan hayaniyar ce ta farkar da ni. Halifa ya hankade ta da karfi ta fadi, yace ki daina taba ni hakikar ke abar kyamace,kin bani mamaki. Zafin maganganun Halifa sun fi mata zafin faduwar kuma ta tabbatar Allah ne kawai zai wanke ta. Sai lokacin ta soma kuka tana furta Allahumma ajirni fimusibati. Ta mike domin bata da sauran wani abu da zata fadawa mijin nata giyar kishi da bakin cikin abinda ya gani ke dibar sa, ta yi masa uzri a yanzu tasan lokacin yi nadamar hakan zai zo a gaba. Bazata yanke hukunci cikin fushi ba, amma tasan auren ta ya gama lalacewa.
Ta mike da nufin ta tafi dakin ta ta saurari hukuncin Ubangiji sai taji ana ku rike shi ta bishi da kallo ya kama bishiya ya haye katanga ya dira ta baya wanda kafin a zagaya ta tabbata ya gudu.
Ta zauna akan kujera ta fashe da sabon kuka. Tana fadin Allah yau kuma da wannan na wayi gari ya Allah! Allah ka kubutar dani kamar yadda ka kubutar da Annabi Yusuf daga khaidin mata. Allah ka wanke ni kamar yadda ka wanke Uwar muminai Nana Aisha daga sharrin masu sharri. Alwala ta yi da ta samu sanyi a zuciyar ta. Ina ma ace mafarki ne.
A tsakar gida kuwa kwarto ya gudu Halifa yaji takaicin haka domin ya so yasa a daure masa shi. Ya shiga dakin a fusace Asiya wadda ta gama sarewa ta dube shi. Yace "Wai Asiya in tambaye ki, dame na rage ki har ki ke kula wannan kazamin daga gani ko sana'a bashi da ita. Ko bana iya gamsar da ke a shimfida ne? Asiya sai Kallon shi take ba shakka ya gama yarda cewa ta aikata laifin.
Ta mike ta shiga daki ta gama amincewa auren su ya kare ta sauke akwati tana duba kayan da zata dauka a kayanta na gida dai kala daya ne wata doguwar rigar atamfa Dan haka ta ciro ta da wani hijabbinta na idin da akayi kafin auren su. Ya shigo dakin lokacin ta gama sakawa ta duba jakar ta ta dauki dan kudin ta wanda yakan bata. Ya ce ina zaki ko binshi za kiyi? Ta dube shi cikin wani yanayi wanda bazata iya fassara shi ba. Duk abinda aka yi ba sukai wannan kalmar da ya fada mata yin daci a zuciyar ta ba. Hawaye suka kwaranyo daga Idanuwanta. Cikin rawar murya tace "Ka yi duk zargin da zaka yi bazan hana ka ba. Gaskiyar ita ce, ban aikata komai ba, banda masaniya akan komai, sannan yanzu kuma gidan mu zanje. Zaki je ki tona wannan maganar ta yi ta yawo cikin mutane? Abinda ya sa ban samu ba koda wancan yaron ya gudu bana son in kai shi gaba maganar ta zama abin tattaunawa a satin nan, can kuma abin ya koma Soshiyal midiya. Asiya tace ni ba zan damu ba ko waye ma zaiji ya ji kuma ba zan hana shi yarda ba tunda kaima ka yarda. Kuskuren da nayi na dauka cewa zaka bani kariya a matsayin ka na mijina ashe nayi kuskure. Ta fito fallo ya biyota ban fa baki izinin fita ba. " Halifa bana bukatar izini domin aure da zargi basa haduwa." To kin fi son kije ki tada hankalin Inna gata da hawan jini? Asiya tace bari kaji Inna tafi kowa sani na, ko a mafarki bazata taba yarda da wannan wasan kwaikwayon ba.
Ta kama kofa ta bude yace Cikina kar kije min dashi ko ina. Anty dake bakin kofa ta a she. Ta ce ta ina ya zama cikin ka, kana jin me cikin ya fada? Ka barta taje gida tunda tana gaddama cewar bata aikata ba sai ka bincika ka samu Tabbaci. Halifa bai ce kala ba har Asiya ta fice.
Shima ya rufe dakin ya fice. A baya yake bin Napep din da ta hau har Unguwar su.
Asiya ta shiga gida Inna tana kwance Abba yana girki Maman Annur taje gidan aiki. Inna ta tashi zaune tana fadin Asiya ce yau da wuri haka? Asiya tace inna ai ba zuwan dadi bane. Nan ta kwashe komai ta sanar da ita. Inna ta shiga salati da sallallami tace yau kuma da haka na wayi gari. Allah ka fidda wannan yarinyar sai kuma ta shiga lallashin Asiya tare da bata magana. Inna dai ta boye wa Asiya damuwar ta ne kawai amma fa ta shiga tashin hankali domin duk yadda Asiya take Kallon abin ya fi haka, ga shi su ba karfi ba ta yi imani Asiya bazata taba aikata abinda aka danganta ta dashi ba.
Da dare Halifa yana ta kai kawo daga falo zuwa daki yana auna abin da ya faru wata zuciyar tace kai. me yasa baka zo ka shigo dakin ba a lokacin? Ya tuna yadda Anty ta rike shi tana karkaje kar ayi mugun abu, zaka yi mugun gani. To amma gashi yana kokwanto kodai sharri ne aka yi mata masu bata guba din nan. Ya kamata ya fahimci cewa lallai akwai wani abu. Ya fita zuwa sasan Anty tana waya da ƙawarta Wai ta kira tana cewa ta ga abinda ya faru a gidan an dora a tiktok. Anty tana cewa wallahi kuwa nima dazu Hafsa ke nuna min ko suwaye suka dauka suka dora ga shinan shi kwarton an masa duka ita kuma Asiya tana ta kuka, aiko ta sha zagi. Halifa yace Anty me aka dora a Tiktok? Matar tawa aka dora? Waye yake da tabbci ko shedar cewa zina ake aikatawa adakin? Waye ya yi musu kamu irin Na shari 'a?
Anty ta juyo da sauri cike da mamaki ta kalli Halifa tana murna ta zare masa yarinyar daga zuciya yanzu Sai batun zubda ciki amma shine zai mata tsalle? Ta mike a fusace " Halifa idan har na isa da kai wallahi sai ka bar yarinyar nan. Wane irin asiri ta yi maka haka wallahi ko waye ya tsaya maka sai ka barta ba dai a zuri a taba. Halifa yace Anty gaskiyar magana ina son mata ta kuma zuciyata ta ki amincewa da cewar Asiya ta aikata wannan abin in halinta ne da ta yi kafin ta zo gidana amma yarinyar nan a budurwa na same ta, ni ne mutum na farko da na fara kusantar ta. Bazan manta hakan ba. Dan haka saina bincika sosai kuma duk wanda na gano da hannun shi a dauka ta a Video ya yada sai na yi shara a da shi.
*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/29, 21:25] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w
Ga zaton ta barawo aka kama, ta dubi Halifa ta ce a ina ya yi sata? Kafin Halifa ya bata amsa sai taji barawo na cewa Dan Allah ku yi hakuri wallahi sai da nace wa Asi baby kawai ta zo inda muka saba haduwa gidan abokina wanda ya rabu da matarsa can take zuwa idan Halifa ya tafi kasuwa, to da yake ina zuwa wasu lokutan a nan idan ya fita yauma wallahi na musa amma tace yanayin jikinta ya sa ta kasa...... Halifa ya sa kafa ya tokari cikin sa, sai da ya yi kara sannan jini ta hanci ta baki aka rike Halifa yana fizgewa akan cewa a sake shi sai ya kashe shi. Sai lokacin Asiya ta fahimci sharrin da aka yi mata ta daga ido ta kalli Anty sai ta saki wani murmushi irin na takaici. Tace tanan aka sake bullo min? Ta je gaban mutumin ta kalle shi. Ina son ka fadi tsakanin ka da Allah ka taba ganina? Ya fashe da kuka tare da fadin Asiya kalli ki gani kefa ki ka ce inzo gidan ki ke kika ce mijin ya tafi kasuwa amma shine kike alaye kamar baki san komai ba. Zufa ta karyo wa Asiya lallai sun tsara abin su. Ta kalli Halifa Dan Allah Yaya kar ka yarda da shi wallahi ban san shiba.
Anty tace amma wannan yazo gidan nan ba so daya ba akwai ranar da na ta tambaye shi ya ce min yayanku ne, to amma ganin yadda in ya fito yake sanda shiyasa na kasa yarda da shi. Halifa wanda takaici ya hana shi magana ya fidda hannu ya wanka wa Asiya mari yace kinsan tin yaushe nake a gidan nan tun ina fita kasuwa Anty ta kira ni tace ga wani ya zo tana ganin shi yana yawan zuwa, har nace kila Dan Uwa ku ne sai kuma na kasa nutsuwa kasancewar yadda mata suka koma a wanna zamanin. Nayi awa daya ina jiran fitowar shi sannan ya fito daga dakin mu dakin auren mu Asiya yana gyara wando ya dakko takalmanshi a inda ya boye ya saka ina Kallon shi ba zan iya barin shi ya fita ba, ni ne nayi masa wannan dukan. Sai Halifa ya fashe da kuka. Asiya cikin firgici da tashin hankali, ta kama hannun shi tace "Yaya kar ka yarda wallahi wannan shiryayyen al amari ne ka yi tunani sosai wallahi ni bacci nake ina kwance a dakina wannan hayaniyar ce ta farkar da ni. Halifa ya hankade ta da karfi ta fadi, yace ki daina taba ni hakikar ke abar kyamace,kin bani mamaki. Zafin maganganun Halifa sun fi mata zafin faduwar kuma ta tabbatar Allah ne kawai zai wanke ta. Sai lokacin ta soma kuka tana furta Allahumma ajirni fimusibati. Ta mike domin bata da sauran wani abu da zata fadawa mijin nata giyar kishi da bakin cikin abinda ya gani ke dibar sa, ta yi masa uzri a yanzu tasan lokacin yi nadamar hakan zai zo a gaba. Bazata yanke hukunci cikin fushi ba, amma tasan auren ta ya gama lalacewa.
Ta mike da nufin ta tafi dakin ta ta saurari hukuncin Ubangiji sai taji ana ku rike shi ta bishi da kallo ya kama bishiya ya haye katanga ya dira ta baya wanda kafin a zagaya ta tabbata ya gudu.
Ta zauna akan kujera ta fashe da sabon kuka. Tana fadin Allah yau kuma da wannan na wayi gari ya Allah! Allah ka kubutar dani kamar yadda ka kubutar da Annabi Yusuf daga khaidin mata. Allah ka wanke ni kamar yadda ka wanke Uwar muminai Nana Aisha daga sharrin masu sharri. Alwala ta yi da ta samu sanyi a zuciyar ta. Ina ma ace mafarki ne.
A tsakar gida kuwa kwarto ya gudu Halifa yaji takaicin haka domin ya so yasa a daure masa shi. Ya shiga dakin a fusace Asiya wadda ta gama sarewa ta dube shi. Yace "Wai Asiya in tambaye ki, dame na rage ki har ki ke kula wannan kazamin daga gani ko sana'a bashi da ita. Ko bana iya gamsar da ke a shimfida ne? Asiya sai Kallon shi take ba shakka ya gama yarda cewa ta aikata laifin.
Ta mike ta shiga daki ta gama amincewa auren su ya kare ta sauke akwati tana duba kayan da zata dauka a kayanta na gida dai kala daya ne wata doguwar rigar atamfa Dan haka ta ciro ta da wani hijabbinta na idin da akayi kafin auren su. Ya shigo dakin lokacin ta gama sakawa ta duba jakar ta ta dauki dan kudin ta wanda yakan bata. Ya ce ina zaki ko binshi za kiyi? Ta dube shi cikin wani yanayi wanda bazata iya fassara shi ba. Duk abinda aka yi ba sukai wannan kalmar da ya fada mata yin daci a zuciyar ta ba. Hawaye suka kwaranyo daga Idanuwanta. Cikin rawar murya tace "Ka yi duk zargin da zaka yi bazan hana ka ba. Gaskiyar ita ce, ban aikata komai ba, banda masaniya akan komai, sannan yanzu kuma gidan mu zanje. Zaki je ki tona wannan maganar ta yi ta yawo cikin mutane? Abinda ya sa ban samu ba koda wancan yaron ya gudu bana son in kai shi gaba maganar ta zama abin tattaunawa a satin nan, can kuma abin ya koma Soshiyal midiya. Asiya tace ni ba zan damu ba ko waye ma zaiji ya ji kuma ba zan hana shi yarda ba tunda kaima ka yarda. Kuskuren da nayi na dauka cewa zaka bani kariya a matsayin ka na mijina ashe nayi kuskure. Ta fito fallo ya biyota ban fa baki izinin fita ba. " Halifa bana bukatar izini domin aure da zargi basa haduwa." To kin fi son kije ki tada hankalin Inna gata da hawan jini? Asiya tace bari kaji Inna tafi kowa sani na, ko a mafarki bazata taba yarda da wannan wasan kwaikwayon ba.
Ta kama kofa ta bude yace Cikina kar kije min dashi ko ina. Anty dake bakin kofa ta a she. Ta ce ta ina ya zama cikin ka, kana jin me cikin ya fada? Ka barta taje gida tunda tana gaddama cewar bata aikata ba sai ka bincika ka samu Tabbaci. Halifa bai ce kala ba har Asiya ta fice.
Shima ya rufe dakin ya fice. A baya yake bin Napep din da ta hau har Unguwar su.
Asiya ta shiga gida Inna tana kwance Abba yana girki Maman Annur taje gidan aiki. Inna ta tashi zaune tana fadin Asiya ce yau da wuri haka? Asiya tace inna ai ba zuwan dadi bane. Nan ta kwashe komai ta sanar da ita. Inna ta shiga salati da sallallami tace yau kuma da haka na wayi gari. Allah ka fidda wannan yarinyar sai kuma ta shiga lallashin Asiya tare da bata magana. Inna dai ta boye wa Asiya damuwar ta ne kawai amma fa ta shiga tashin hankali domin duk yadda Asiya take Kallon abin ya fi haka, ga shi su ba karfi ba ta yi imani Asiya bazata taba aikata abinda aka danganta ta dashi ba.
Da dare Halifa yana ta kai kawo daga falo zuwa daki yana auna abin da ya faru wata zuciyar tace kai. me yasa baka zo ka shigo dakin ba a lokacin? Ya tuna yadda Anty ta rike shi tana karkaje kar ayi mugun abu, zaka yi mugun gani. To amma gashi yana kokwanto kodai sharri ne aka yi mata masu bata guba din nan. Ya kamata ya fahimci cewa lallai akwai wani abu. Ya fita zuwa sasan Anty tana waya da ƙawarta Wai ta kira tana cewa ta ga abinda ya faru a gidan an dora a tiktok. Anty tana cewa wallahi kuwa nima dazu Hafsa ke nuna min ko suwaye suka dauka suka dora ga shinan shi kwarton an masa duka ita kuma Asiya tana ta kuka, aiko ta sha zagi. Halifa yace Anty me aka dora a Tiktok? Matar tawa aka dora? Waye yake da tabbci ko shedar cewa zina ake aikatawa adakin? Waye ya yi musu kamu irin Na shari 'a?
Anty ta juyo da sauri cike da mamaki ta kalli Halifa tana murna ta zare masa yarinyar daga zuciya yanzu Sai batun zubda ciki amma shine zai mata tsalle? Ta mike a fusace " Halifa idan har na isa da kai wallahi sai ka bar yarinyar nan. Wane irin asiri ta yi maka haka wallahi ko waye ya tsaya maka sai ka barta ba dai a zuri a taba. Halifa yace Anty gaskiyar magana ina son mata ta kuma zuciyata ta ki amincewa da cewar Asiya ta aikata wannan abin in halinta ne da ta yi kafin ta zo gidana amma yarinyar nan a budurwa na same ta, ni ne mutum na farko da na fara kusantar ta. Bazan manta hakan ba. Dan haka saina bincika sosai kuma duk wanda na gano da hannun shi a dauka ta a Video ya yada sai na yi shara a da shi.