Sashe 58
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*✍🏻 HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[1/12, 17:34] Ummi Tandama😇: *Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
Saukar mari da Asiya ta ji shine ya katse mata maganar ta,ta kalle shi sai tsuma yake "me yasa ne ki ke son in yi losing ɗin temper?" Kafin ta fahimci abin da yake faɗa ya kuma kifa mata wani marin ya jefa ta kan kujera,a tsorace ta ɗago hancinta yana zubar da jini, kamar dai ya haukace, ya kuma nifo ta, ta ruga ɗakin da ke kusa da ita ta faɗa ta rufo ƙofa jikinta yana ta ɓari tana jiyo shi gaba ɗaya ya haukace yana ta fashe-fashe yana cewa ki fito ki faɗamin ko saki nawa kike buƙata?.
Ya faɗa ɗakin su ya ɗakko takarda da biro "ki faɗi adadin sakin da ki ke so in yi miki yanzun nan na fara jin cewa na tsane ki. In har tsanar ki ta yiwa zuciya ta tasiri ko a hanya ba zan so ganin ki ba Asiya. Ta leƙo ta window tana kallon shi.
Baki da wani tunani sai na zargina mata mata dai in neme su mana ba kuɗina bane ko kabarin mu ɗaya? Kina da wuta ne ko kina da aljanna? Haba kin hanani zaman lafiya, me ma ya hana ki tafiya gidan naku ɗazun da kika fita? Ki fito ki tafi da hujjarki a hannu in huta nima.
Asiya ta firgita ta manta da dukan da ya yi mata ta isa bakin ƙofa ta buɗe a gigice ta zo gaban shi ta fisge takardar. "Yaya bana son ka sake ni don Allah" ta faɗa jikinshi ta rungume shi kam tana kuka tana faɗin "wallahi na daina zargin ka sherrin shaiɗan ne Yaya na tuba ka yi haƙuri. Jikinshi sai rawa yake kamar wanda ake kaɗawa gangi.... kamar minti uku ya ya kice ta ya jefar ita da biron ya fice daga falon ya shiga ɗaki ya fito ya fice
Asiya tana kuka ta ji tashin motar sa ya fice daga gidan.
Ta nufi banɗaki ta wanke jinin, zuciyar ta ta rasa wane irin tunani zata yi,borin kunya yasa ya dake ta ko kuwa zafin ƙazafin da tayi masa ne?
Borin kunya ne zuciyar ta ta faɗa mata,ki zauna tunda ya fara dukanki ki zama jaka, yanzu ma ya fice zai je ya samu wadda ya kira ɗazu su ƙwana tare, gara fa kin koma gaban uwarki ki haƙura da talaucin ku yafi dukiya babu ƙwanciyar hankali. In ba haka ba wataran sai ya kashe ki kuma babu abin da za ayi.
Da sauri ta tashi fuska kumbure ta kuma janyo aƙwati ta loda kaya lokacin karfe ɗaya ta wuce na dare,bazata ƙara ƙwana a wannan gidan ba tafa a fili.
Tana kici kicin fito da aƙwati ta ji shigowar motar shi tace ai ko motar shi bazan hau ba gara in kwana a hanya cak ta tsaya a farfajiyar gidan tana kallon su sun nufo ta Inna da Sulaiman.
Asiya!! Inna ta furta da ƙarfi, Asiya ta saki akwati ta ruga ta rungume Inna ta ma manta wai tana da goyo sai kuka ita da Inna.
Sun ɗauki mintuna Halifa ya ce ya isa Inna ku shigo. Asiya ta ce Inna mu tafi kawai ni bazan kuma shiga gidan nan ba, tunda na ganki ƙafar ki ƙafata. Inna ta ce ina zaki da tsohon daren nan,bani ɗan naki in ganshi.
Asiya tace gurin ki zan je, kullum sai na yi yunƙurin tafiya. Halifa ya kalle ta fuska a ɗaure ya kau da kai. Inna tace "me kuma ya samu fuskar ki haka?"
Asiya tace faɗuwa na yi a banɗaki. Halifa ya yi karaf yace "marinta na yi Inna."
Ina ganin kawai ku tafi tare da ita zata fi samun nutsuwar zuciyarta. Sulaiman zai yi magana Halifa ya ɗaga masa hannu tare da miƙa masa makullin mota. Kuna iya tafiya za mu yi waya kawai.
Asiya ta yi gaba Inna ta bita a baya dan Sulaiman ya ɗauki akwatin,sai da suka fice a gidan Halifa ya dawo ya shige ɗaki
*** **** ***
Bros ya kalli Maman Nihal "ki daina wata faɗuwar gaba ita fa Anty yanzu tayi nadama,dan Allah kar ki nuna komai game da abinda ya faru a baya." Amarya dake riƙe da jaririn Maman Nihal mai sunan Dady tace Anty dan Allah ki daina wata fargaba.
Suka shiga su ukun domin ɗakko Nihal da Nur. Anty tana zaune a falo tana kallon T.V sai dai sam hankalin ta baya kan abin da ake yi tana can cikin tunanikanta mafarkan ta da har yanzu babu wanda ya zama gaskiya,sai zuwa yaushe zata samu nasara? komai ta shirya sai ya lalace.
Bata ji sallamar su ba sai da Bros ya ce Anty! Da ƙarfi sannan ta firgigit ta ɗauki sakwanni sannan ta fahimci su waye a gabanta.
Ta ɗaure fuska tare da kau da kai. Maman Nihal ta durƙusa ina yini Anty? Bata amsa ba amarya ta je ta ɗora mata yaron a cinya ga mijin ki nan. Ta yi kamar zata ture shi da taga zai faɗi kuma babu wanda ya yinƙuro dan kamashi sai ta yi saurin riƙe shi. Bros ya yi murmushi ya yin da amarya ta saki dariya tare da faɗin ashe dai ana so. Anty ta dubi amarya "ke bana son rashin kunya zanyi maganin ki wallahi in zaki kawo min raini,bana wasa da yara." Allah ya baki haƙuri ta faɗa tana dariya "bari in nemo su Nihal" amarya ta faɗa tare da nufar ciki.
Anty ta kalli Maman Nihal ta taɓe baki, Maman Nihal ta sunkuyar da kai cike da tausayin Anty,duk ta yi baƙi ta rame. Anty ta katse mata tunani da faɗin "wannan yarinyar makira ce,naga take taken ta sai kinyi da gaske. Cike da mamaki Maman Nihal tace "to Anty zan kula." Bros yace amma kuma ni banga wani aibunta ba,tana girmama mu. Anty tace "in kai baka gane abin da nike nufi ba ita matarka ta gane" ta kalli ɗan dake cinyar ta tace "sai ya tuna min kai kana yaro sak haka kake." Cike da jin daɗi suka yi yar dariya.
Maman Nihal tace Anty shima bai yi rigima ba ke nan dan shi wannan bashi da rigima sai kirin kirin ba zai nutsu guri guda ba.
Haka dai uban yake. Amarya ta dawo da su Nihal cike da murna suka faɗa jikin uwar su abin tausayi Nihal tace Momy Baba ya faɗa mana kin haifa mana Baby boy shine wannan a gurin Anty? Ungo kayanku Anty ta faɗa tana miƙa ma Nihal shi. Nur kuwa ta kasa sauka daga jikin Mamansu domin ita dai baza ta sake yarda ta tafi ta barta ba.
Amarya ta ce Anty naga Hafsa tana kuka kuma bata faɗa min abinda ke damunta ba. Duk suka kalli Anty. Ta dubi Bros ita da Dadynku ne,ya ce ya saka mata ranar aure sati shidda bata san waye mijin ba." Maman Nihal tace Allah sarki amma ai da Dady ya bata dama ta fito da wanda take so tukunna. Bros ya ce "ya fa bata,ai munyi maganar da shi,banga laifin sa ba amma bari inga Hafsar shegiya sai dai ka shiga lamarin ta amma ba domin halinta ba." Ya nufi ɗakin.
Ganin shigowar shi yasa Hafsi da ke ƙwance tashi zaune,Bros yace "kinga sakamakon mugun hali tun yanzu ko? Hafsi tace don Allah ka bawa Dady haƙuri wallahi ba zan sake shiga harkar matarsa ba. Bros yace "mafita ɗaya ce ina shi wannan saurayin naki bani number ɗin shi inyi magana dashi, amma Dady wannan ranar da ya saka miki ta aure bazai taɓa ɗage ta ba." Cikin sauri ta tashi ta ɗakko waya ta fito da number ta miƙa wa Bros tana cewa nayi nayi dashi ya zo Anty tana kiranshi yaƙi zuwa yanzu ma baya ɗaga kirana. Bros yace zanga ya zanyi da shi. Ya koma wajen su Anty suka ƙwashe ƴaƴansu,Bros ya kawo kuɗi ya ba Anty suka tafi.
Anty har labulen window ta ɗaga tana leƙensu wai ashe aƙwai ranar da zata zo tana ganin Maman Nihal su jera da ɗanta a gabanta kuma har ta furta ku gaida gida. Batasan hujjar da zata bayar a matsayin dalilin hawayenta ba, abinda kawai ta sani shine bata yi nasara akan ta ba.
Akan wa kika yi nasara ma? Zuciyar ta ta tambaye ta. A fili tace akan Asiya matar Halifa na kashe kuɗi na wahala nayi asarori, amma ban faɗi ba, na yi nasara tunda Yanzun ta Haukace ta shiga Duniya ba shakka wannan nasara ce.
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[1/31, 12:32] Ummi Tandama😇: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ
*Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
Inna ranta ya kasa kwanciya da kalmar da Halifa ya furta a gabanta cewar ya mari Asiya. Dan haka Inna tace to ke me kika yi masa har ya yi miki wannan mari haka? Nifa bana son aure da dole wallahi sai na samu kaina a sabon tashin hankalin da naji kamar ina ma banganki ba?
Sulaiman ya yi gyaran murya sannan yace Inna kar ki yi saurin yanke hukunci ki jira muje gida sannan da zai yiwu karki saurari me Asiya zata fada gobe zanzo da motar sa in dauke shi muje gata gashi a yi musu ba cuta ba cutarwa. Inna tace shike nan a yi hakan abin babu dadi Sam. Wa ya sani ko akan tace sai ta zo gurina ne? Inna ta fada ta na Kallon Asiya wadda take tunani anya zata iya tona asirin Uban ɗanta kuwa?
Inna ki bari mu nutsu Zan fada miki komai.
[1/12, 17:34] Ummi Tandama😇: *Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
Saukar mari da Asiya ta ji shine ya katse mata maganar ta,ta kalle shi sai tsuma yake "me yasa ne ki ke son in yi losing ɗin temper?" Kafin ta fahimci abin da yake faɗa ya kuma kifa mata wani marin ya jefa ta kan kujera,a tsorace ta ɗago hancinta yana zubar da jini, kamar dai ya haukace, ya kuma nifo ta, ta ruga ɗakin da ke kusa da ita ta faɗa ta rufo ƙofa jikinta yana ta ɓari tana jiyo shi gaba ɗaya ya haukace yana ta fashe-fashe yana cewa ki fito ki faɗamin ko saki nawa kike buƙata?.
Ya faɗa ɗakin su ya ɗakko takarda da biro "ki faɗi adadin sakin da ki ke so in yi miki yanzun nan na fara jin cewa na tsane ki. In har tsanar ki ta yiwa zuciya ta tasiri ko a hanya ba zan so ganin ki ba Asiya. Ta leƙo ta window tana kallon shi.
Baki da wani tunani sai na zargina mata mata dai in neme su mana ba kuɗina bane ko kabarin mu ɗaya? Kina da wuta ne ko kina da aljanna? Haba kin hanani zaman lafiya, me ma ya hana ki tafiya gidan naku ɗazun da kika fita? Ki fito ki tafi da hujjarki a hannu in huta nima.
Asiya ta firgita ta manta da dukan da ya yi mata ta isa bakin ƙofa ta buɗe a gigice ta zo gaban shi ta fisge takardar. "Yaya bana son ka sake ni don Allah" ta faɗa jikinshi ta rungume shi kam tana kuka tana faɗin "wallahi na daina zargin ka sherrin shaiɗan ne Yaya na tuba ka yi haƙuri. Jikinshi sai rawa yake kamar wanda ake kaɗawa gangi.... kamar minti uku ya ya kice ta ya jefar ita da biron ya fice daga falon ya shiga ɗaki ya fito ya fice
Asiya tana kuka ta ji tashin motar sa ya fice daga gidan.
Ta nufi banɗaki ta wanke jinin, zuciyar ta ta rasa wane irin tunani zata yi,borin kunya yasa ya dake ta ko kuwa zafin ƙazafin da tayi masa ne?
Borin kunya ne zuciyar ta ta faɗa mata,ki zauna tunda ya fara dukanki ki zama jaka, yanzu ma ya fice zai je ya samu wadda ya kira ɗazu su ƙwana tare, gara fa kin koma gaban uwarki ki haƙura da talaucin ku yafi dukiya babu ƙwanciyar hankali. In ba haka ba wataran sai ya kashe ki kuma babu abin da za ayi.
Da sauri ta tashi fuska kumbure ta kuma janyo aƙwati ta loda kaya lokacin karfe ɗaya ta wuce na dare,bazata ƙara ƙwana a wannan gidan ba tafa a fili.
Tana kici kicin fito da aƙwati ta ji shigowar motar shi tace ai ko motar shi bazan hau ba gara in kwana a hanya cak ta tsaya a farfajiyar gidan tana kallon su sun nufo ta Inna da Sulaiman.
Asiya!! Inna ta furta da ƙarfi, Asiya ta saki akwati ta ruga ta rungume Inna ta ma manta wai tana da goyo sai kuka ita da Inna.
Sun ɗauki mintuna Halifa ya ce ya isa Inna ku shigo. Asiya ta ce Inna mu tafi kawai ni bazan kuma shiga gidan nan ba, tunda na ganki ƙafar ki ƙafata. Inna ta ce ina zaki da tsohon daren nan,bani ɗan naki in ganshi.
Asiya tace gurin ki zan je, kullum sai na yi yunƙurin tafiya. Halifa ya kalle ta fuska a ɗaure ya kau da kai. Inna tace "me kuma ya samu fuskar ki haka?"
Asiya tace faɗuwa na yi a banɗaki. Halifa ya yi karaf yace "marinta na yi Inna."
Ina ganin kawai ku tafi tare da ita zata fi samun nutsuwar zuciyarta. Sulaiman zai yi magana Halifa ya ɗaga masa hannu tare da miƙa masa makullin mota. Kuna iya tafiya za mu yi waya kawai.
Asiya ta yi gaba Inna ta bita a baya dan Sulaiman ya ɗauki akwatin,sai da suka fice a gidan Halifa ya dawo ya shige ɗaki
*** **** ***
Bros ya kalli Maman Nihal "ki daina wata faɗuwar gaba ita fa Anty yanzu tayi nadama,dan Allah kar ki nuna komai game da abinda ya faru a baya." Amarya dake riƙe da jaririn Maman Nihal mai sunan Dady tace Anty dan Allah ki daina wata fargaba.
Suka shiga su ukun domin ɗakko Nihal da Nur. Anty tana zaune a falo tana kallon T.V sai dai sam hankalin ta baya kan abin da ake yi tana can cikin tunanikanta mafarkan ta da har yanzu babu wanda ya zama gaskiya,sai zuwa yaushe zata samu nasara? komai ta shirya sai ya lalace.
Bata ji sallamar su ba sai da Bros ya ce Anty! Da ƙarfi sannan ta firgigit ta ɗauki sakwanni sannan ta fahimci su waye a gabanta.
Ta ɗaure fuska tare da kau da kai. Maman Nihal ta durƙusa ina yini Anty? Bata amsa ba amarya ta je ta ɗora mata yaron a cinya ga mijin ki nan. Ta yi kamar zata ture shi da taga zai faɗi kuma babu wanda ya yinƙuro dan kamashi sai ta yi saurin riƙe shi. Bros ya yi murmushi ya yin da amarya ta saki dariya tare da faɗin ashe dai ana so. Anty ta dubi amarya "ke bana son rashin kunya zanyi maganin ki wallahi in zaki kawo min raini,bana wasa da yara." Allah ya baki haƙuri ta faɗa tana dariya "bari in nemo su Nihal" amarya ta faɗa tare da nufar ciki.
Anty ta kalli Maman Nihal ta taɓe baki, Maman Nihal ta sunkuyar da kai cike da tausayin Anty,duk ta yi baƙi ta rame. Anty ta katse mata tunani da faɗin "wannan yarinyar makira ce,naga take taken ta sai kinyi da gaske. Cike da mamaki Maman Nihal tace "to Anty zan kula." Bros yace amma kuma ni banga wani aibunta ba,tana girmama mu. Anty tace "in kai baka gane abin da nike nufi ba ita matarka ta gane" ta kalli ɗan dake cinyar ta tace "sai ya tuna min kai kana yaro sak haka kake." Cike da jin daɗi suka yi yar dariya.
Maman Nihal tace Anty shima bai yi rigima ba ke nan dan shi wannan bashi da rigima sai kirin kirin ba zai nutsu guri guda ba.
Haka dai uban yake. Amarya ta dawo da su Nihal cike da murna suka faɗa jikin uwar su abin tausayi Nihal tace Momy Baba ya faɗa mana kin haifa mana Baby boy shine wannan a gurin Anty? Ungo kayanku Anty ta faɗa tana miƙa ma Nihal shi. Nur kuwa ta kasa sauka daga jikin Mamansu domin ita dai baza ta sake yarda ta tafi ta barta ba.
Amarya ta ce Anty naga Hafsa tana kuka kuma bata faɗa min abinda ke damunta ba. Duk suka kalli Anty. Ta dubi Bros ita da Dadynku ne,ya ce ya saka mata ranar aure sati shidda bata san waye mijin ba." Maman Nihal tace Allah sarki amma ai da Dady ya bata dama ta fito da wanda take so tukunna. Bros ya ce "ya fa bata,ai munyi maganar da shi,banga laifin sa ba amma bari inga Hafsar shegiya sai dai ka shiga lamarin ta amma ba domin halinta ba." Ya nufi ɗakin.
Ganin shigowar shi yasa Hafsi da ke ƙwance tashi zaune,Bros yace "kinga sakamakon mugun hali tun yanzu ko? Hafsi tace don Allah ka bawa Dady haƙuri wallahi ba zan sake shiga harkar matarsa ba. Bros yace "mafita ɗaya ce ina shi wannan saurayin naki bani number ɗin shi inyi magana dashi, amma Dady wannan ranar da ya saka miki ta aure bazai taɓa ɗage ta ba." Cikin sauri ta tashi ta ɗakko waya ta fito da number ta miƙa wa Bros tana cewa nayi nayi dashi ya zo Anty tana kiranshi yaƙi zuwa yanzu ma baya ɗaga kirana. Bros yace zanga ya zanyi da shi. Ya koma wajen su Anty suka ƙwashe ƴaƴansu,Bros ya kawo kuɗi ya ba Anty suka tafi.
Anty har labulen window ta ɗaga tana leƙensu wai ashe aƙwai ranar da zata zo tana ganin Maman Nihal su jera da ɗanta a gabanta kuma har ta furta ku gaida gida. Batasan hujjar da zata bayar a matsayin dalilin hawayenta ba, abinda kawai ta sani shine bata yi nasara akan ta ba.
Akan wa kika yi nasara ma? Zuciyar ta ta tambaye ta. A fili tace akan Asiya matar Halifa na kashe kuɗi na wahala nayi asarori, amma ban faɗi ba, na yi nasara tunda Yanzun ta Haukace ta shiga Duniya ba shakka wannan nasara ce.
*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[1/31, 12:32] Ummi Tandama😇: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ
*Alhamdulillah masu jiran a gama littafin HASASHE na HALIMA K MASHI document ya kammala ga duk me buƙata zai iya turo kuɗin shi ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank, shedar biya ta wannan number 0814 000 4302*
Inna ranta ya kasa kwanciya da kalmar da Halifa ya furta a gabanta cewar ya mari Asiya. Dan haka Inna tace to ke me kika yi masa har ya yi miki wannan mari haka? Nifa bana son aure da dole wallahi sai na samu kaina a sabon tashin hankalin da naji kamar ina ma banganki ba?
Sulaiman ya yi gyaran murya sannan yace Inna kar ki yi saurin yanke hukunci ki jira muje gida sannan da zai yiwu karki saurari me Asiya zata fada gobe zanzo da motar sa in dauke shi muje gata gashi a yi musu ba cuta ba cutarwa. Inna tace shike nan a yi hakan abin babu dadi Sam. Wa ya sani ko akan tace sai ta zo gurina ne? Inna ta fada ta na Kallon Asiya wadda take tunani anya zata iya tona asirin Uban ɗanta kuwa?
Inna ki bari mu nutsu Zan fada miki komai.