Sashe 54
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wata zuciyar tace dama ki bishi ki ga ina zashi haka, ya zuba kaya masu kyau yana ta kamshi, da ka ganshi kaga matashin mai kudi, ko karyawa ya kasa.
Ta tashi a gurin ta koma falo domin ita ma baza ta iya cin komai ba. Ta shiga zirga zirga da tunanin mafita,wayar ta ta tuna lokacin da Hajjo suke nan suna sauraron shirin rai dangin goro ta ji Labarin Hamshakiyar Uwa tun bata sauraro in suna ji har itama tazo tana ji, Fati ce ta bata lambar marubuciyar da niyyar zata sai littafin tun da bataji farkon labarin ba, bata ma samu ta siya din ba, amma dai zata kira marubuciyar dan ta nemi shawara tana kyauta ta mata zato.
Ta kira layin sau biyu duk ba a daga ba, tace Ummm dama fa ana cewa irin wadanan suna da wulakanci bari dai in sake tunanin wa zan kira. Doni in rage wannan damuwar ta hanyar fada wa wani halin da nake ciki.Kukan danta ta jiyo dan haka ta nufi dakin da sauri,tana daukar shi wayarta ta soma ringing. Ta kalla Number da ta kira ce, da sauri ta daga tana Sallama marubuciyar ta amsa amma sai ta jiyo kukan jariri, sai tace a kula da me kukan nan tukunna. Asiya tace "To Anty zan kira ki anjima kadan.
Anty Halima tace ba damuwa. Sai taji kamar matsalar ta ta yaye, kamar ta gama samun mafita,ba shakka Anty Halima zata bata shawara.
Sai da ta gama dashi tsaf ya sha wanka ya koma bacci sai ta koma falo ta zauna ta sake kiran Anty Halima. Bayan sun gaisa Asiya tace To Anty ni bansan yadda zan yi miki bayani ba, ni dai na kasance ina karanta littafin ki kuma ina da shawara da nake nema. Anty Halima tace babu damuwa ina sauraron ki ki yi magana kamar kina tare da mahaifiyar ki ko wata yayarki ta jini. Asiya ta sake samun nutsuwa ta kwashe dukkan labarinta har zuwa inda ake yanzu ta sanar da Anty Halima.lokacin katin Asiya ya kare, tana kokarin cin bashin kati sai ga shi Anty Halima ta kira, . Asiya ta daga tace bari in saka kati Anty Halima tace babu damuwa ci gaba. Asiya tace Yanzu dai haka kinga ya fita yau ko karyawa bai yi ba, kuma ina zargin wata ce ta kira shi. Sai ta fashe da kuka. Anty Halima tace Yi hakuri ki saurara da kukan haka, kina jina, ki nutsu, kuma yadda baki masa magana ba ina baki shawara karki yi masa maganar, domin shiru hanyace ta dafa mutum a ruwan sanyi musamman abokin zama, kuma ki daure ki daina nuna masa wata alama da ke nuna kina zarginsa. Abu na farko ki rage bacci ki fadawa Allah duk wata damuwar ki cikin dare, sannan ki daina saka ido akan wayarsa karma ki sake dauka,domin zaki iya ganin abinda zai kawo karshen zama lafiyar ku har na nan gaba. Asiya tace Allah ya sa in iya zan gwada. Sai abu na gaba maganar Mahaifiyar ki tun da abin da zai faru ya riga ya faru, to kawai ki saurari lokacin da ya ce ki bashi din, domin tafiyarki ke kadai kuma kina cikin damuwa zai iya haifar da komai tunda kina son mijinki ko kuwa? Asiya tace haka ne. Ni yanzu abinda yafi daga min hankali Anty Halima guda ɗaya ne ya fita gurin wata zuciya ta wallahi tana cike da kunci. Kina da tabbacin gurin wata ya fita? Anty Halima ta katse ta. Asiya ta soma kuka Ina da tabbaci Anty, boye boyen da yake yi min fa? Kuma ai ko me aiki na ya nuna damuwa da na sallame su. Ina zargin ma ko ita yake bi. Assha!! Inji Anty Halima, ta katseta, kar ki yanke hukuncin da iya hasashe ba lallai ya zama gaskiya ba, amma ki daure ki kau da kanki, kinsan fa zargi in ya yi yawa yana bata aure. Ki yi masa addu'a ko ya dawo kar ki nuna masa, cin amana bata dorewa a cikin aure, kuma yana bukatar ki kusa da shi tunda shi ba mai abokai bane barkatai yawan shige masa da bashi shawara za su taimaka miki gurin maido shi hanya,karki nuna kyankyami a gare shi ko da ta tabbata cewa kin kamashi dumu dumu na abinda ki ke hasashe. Hakan zai ba matan wajen damar samun shi, kin fada min cewa shi mutum ne mabukaci ga kudi ga lafiya dan haka ki ja abinki a jiki, Mata da ki ke gani a wannan zamanin su ne ke neman mazan da kansu Dan haka ki kula sosai amma addu'a tafi komai muhimmanci kar ki manta.
Asiya ta yi godiya suka yi sallama duk da ta samu kwanciyar hankali kadan sai dai fa bata yarda wai ta kauda kai ba.
Ina zata samu labarin su Fati, tana son sani ko fati ya ke so. Ta tuna da nurse wadda ta ke kula da baby, ta daga waya ta kira ta suka gaisa, ta tambayi yaro tace ko anyi masa allurar wata ta farko da ake yi? Ta ga ya wuce sati shida. Asiya tace ba ayi ba, ai su basu san anayi ba. Nurse tace ya kamata ku kai shi yau ko gobe, Asiya tace insha Allahu. Sannan tace yawwa wai kuwa kinsan wannan Hajjo din da suka min aiki Ina nufin Unguwar su. Nurse tace kinsan tana aikin shara ne a Asibitin mu,na dai san kamar a Darmanawa aka ce take amma bansan gidan ta ba. Asiya tace Allah sarki Dan Allah ko zaki iya samo min lambarta sai dai dan Allah karki ce ni ce, ina son ne in ziyarce ta, na bazata, ta yi min mutunci kamar yarta ko jikarta muka zauna. Nurse tace "Ki tambayi megidanki mana ai kamar ba zai rasa ba. Asiya tace bashi da ita gaskiya, domin dashi mukayi maganar yace in tambaye ki.
Nurse tace to in naganta zan karba miki, in kuma bata bayarba shike nan.Sai bayan sun yi sallama zuciyar ta ke ce mata wai me kike son aikatawa ne Asiya.
Cikin sa a ba a jima ba,lambar ta shigo. Asiya kuwa ta kira Hajjo suka gaisa da ta tabbatar Hajjo bata gane ta ba, sai tace wai ita kawar Fati ce daga Maiduguri ta kira lambar Fati bata samu ba shine ta ke son a hada su. Hajjo tace Allah sarki ga shi kuwa Fati yau tun safe suka fita ni ma na kira layin nata ma baya shiga ko bata da caji ne. Gaban Asiya ya fadi, zufa ta karyo mata kenan dai suna tare, tace na shiga uku.ta darsa a zuciyarta ta. To dan Allah ko zaki tura min lambar ta wannan da nake ta kira din kamar tsohon layinta ne Intel ko shine har yanzu? Hajjo tace A a wannan MTN ne bari zan turo miki sai ki gwada,amma yau ko kunu bata sha ba ta fice tana sauri. Asiya tace Allah sarki ko ta samu aikin ne da tace min tana nema? Hajjo tace gurin wani ma ta tafi da zai saka sunan ta a aikin poliyo zan turo miki lambar yanzu sai anjima.
Asiya ta yi shiru tana nazari kenan karya Fati ta yi wa Hajjo dan ta fita da Halifa maganar aure suke yi kokuwa dai sakarcin su za su yi?
Kuka Asiya ta zauna tana rerawa, zuciyar ta tana tafasa wata zuciyar ta faɗa mata cewa kuka fa bazai zame mata mafita ba. Ta kira layin Halifa bai daga ba sai a kashi na uku, ya daga kafin ta yi magana ya rigata,muryarsa can kasa kasa, gashi sai taji gurin yana amsawa. Yace "Baby Yaya akwai damuwa ne? Ta ce dama Nurse ce muka yi waya tace min ya kamata a kai yaron nan allurar sati shidda yau ko zaka zo yanzu ka kai mu? Yace Baby tace dole sai yau ba za a bari gobe ba? Inda nake yanzu ba zan iya fitowa ba gaskiya. Gaban Asiya ya kuma yanke wa ya fadi, kenan wata ta fi su muhimmanci. Kin san ya za ayi?" Ya katse mata tunani. "Ki samu dan Adaidaita sahu sai ki hada ni da shi muyi magana,amma ki kula kar ki fita ba tare da kin rufe fuskar ki ba, kar ki hadu da wani. Asiya ta kuma hadiye fushinta tace Yaya ba kudi a gurina. Yace "Ki bude Sif din nan karama zan turo miki lambar da zaki saka ki bude yanzu sai ki dauki dubu goma in na zama free zan kira ki kinji, ki kula da kanki. Bai jira amsarta ba kawai ya kashe wayar. Hakan ya tabbatar miki da cewa suna tare da wata Zuciyar ta ta fada mata. Ta soma hasaso su shi da Fati da abubuwan da suke aikatawa.
Karar shigowar sako taji a wayar ta, lambobin da zata buda ma adanar kudin ce. Tana kuka ta bude, kudi ta gani kaloli na kasashen waje ta kirgi dubu goma ta kudinmu na Najeriya ta mayar ta rufe.
Ta tashi a gurin ta koma falo domin ita ma baza ta iya cin komai ba. Ta shiga zirga zirga da tunanin mafita,wayar ta ta tuna lokacin da Hajjo suke nan suna sauraron shirin rai dangin goro ta ji Labarin Hamshakiyar Uwa tun bata sauraro in suna ji har itama tazo tana ji, Fati ce ta bata lambar marubuciyar da niyyar zata sai littafin tun da bataji farkon labarin ba, bata ma samu ta siya din ba, amma dai zata kira marubuciyar dan ta nemi shawara tana kyauta ta mata zato.
Ta kira layin sau biyu duk ba a daga ba, tace Ummm dama fa ana cewa irin wadanan suna da wulakanci bari dai in sake tunanin wa zan kira. Doni in rage wannan damuwar ta hanyar fada wa wani halin da nake ciki.Kukan danta ta jiyo dan haka ta nufi dakin da sauri,tana daukar shi wayarta ta soma ringing. Ta kalla Number da ta kira ce, da sauri ta daga tana Sallama marubuciyar ta amsa amma sai ta jiyo kukan jariri, sai tace a kula da me kukan nan tukunna. Asiya tace "To Anty zan kira ki anjima kadan.
Anty Halima tace ba damuwa. Sai taji kamar matsalar ta ta yaye, kamar ta gama samun mafita,ba shakka Anty Halima zata bata shawara.
Sai da ta gama dashi tsaf ya sha wanka ya koma bacci sai ta koma falo ta zauna ta sake kiran Anty Halima. Bayan sun gaisa Asiya tace To Anty ni bansan yadda zan yi miki bayani ba, ni dai na kasance ina karanta littafin ki kuma ina da shawara da nake nema. Anty Halima tace babu damuwa ina sauraron ki ki yi magana kamar kina tare da mahaifiyar ki ko wata yayarki ta jini. Asiya ta sake samun nutsuwa ta kwashe dukkan labarinta har zuwa inda ake yanzu ta sanar da Anty Halima.lokacin katin Asiya ya kare, tana kokarin cin bashin kati sai ga shi Anty Halima ta kira, . Asiya ta daga tace bari in saka kati Anty Halima tace babu damuwa ci gaba. Asiya tace Yanzu dai haka kinga ya fita yau ko karyawa bai yi ba, kuma ina zargin wata ce ta kira shi. Sai ta fashe da kuka. Anty Halima tace Yi hakuri ki saurara da kukan haka, kina jina, ki nutsu, kuma yadda baki masa magana ba ina baki shawara karki yi masa maganar, domin shiru hanyace ta dafa mutum a ruwan sanyi musamman abokin zama, kuma ki daure ki daina nuna masa wata alama da ke nuna kina zarginsa. Abu na farko ki rage bacci ki fadawa Allah duk wata damuwar ki cikin dare, sannan ki daina saka ido akan wayarsa karma ki sake dauka,domin zaki iya ganin abinda zai kawo karshen zama lafiyar ku har na nan gaba. Asiya tace Allah ya sa in iya zan gwada. Sai abu na gaba maganar Mahaifiyar ki tun da abin da zai faru ya riga ya faru, to kawai ki saurari lokacin da ya ce ki bashi din, domin tafiyarki ke kadai kuma kina cikin damuwa zai iya haifar da komai tunda kina son mijinki ko kuwa? Asiya tace haka ne. Ni yanzu abinda yafi daga min hankali Anty Halima guda ɗaya ne ya fita gurin wata zuciya ta wallahi tana cike da kunci. Kina da tabbacin gurin wata ya fita? Anty Halima ta katse ta. Asiya ta soma kuka Ina da tabbaci Anty, boye boyen da yake yi min fa? Kuma ai ko me aiki na ya nuna damuwa da na sallame su. Ina zargin ma ko ita yake bi. Assha!! Inji Anty Halima, ta katseta, kar ki yanke hukuncin da iya hasashe ba lallai ya zama gaskiya ba, amma ki daure ki kau da kanki, kinsan fa zargi in ya yi yawa yana bata aure. Ki yi masa addu'a ko ya dawo kar ki nuna masa, cin amana bata dorewa a cikin aure, kuma yana bukatar ki kusa da shi tunda shi ba mai abokai bane barkatai yawan shige masa da bashi shawara za su taimaka miki gurin maido shi hanya,karki nuna kyankyami a gare shi ko da ta tabbata cewa kin kamashi dumu dumu na abinda ki ke hasashe. Hakan zai ba matan wajen damar samun shi, kin fada min cewa shi mutum ne mabukaci ga kudi ga lafiya dan haka ki ja abinki a jiki, Mata da ki ke gani a wannan zamanin su ne ke neman mazan da kansu Dan haka ki kula sosai amma addu'a tafi komai muhimmanci kar ki manta.
Asiya ta yi godiya suka yi sallama duk da ta samu kwanciyar hankali kadan sai dai fa bata yarda wai ta kauda kai ba.
Ina zata samu labarin su Fati, tana son sani ko fati ya ke so. Ta tuna da nurse wadda ta ke kula da baby, ta daga waya ta kira ta suka gaisa, ta tambayi yaro tace ko anyi masa allurar wata ta farko da ake yi? Ta ga ya wuce sati shida. Asiya tace ba ayi ba, ai su basu san anayi ba. Nurse tace ya kamata ku kai shi yau ko gobe, Asiya tace insha Allahu. Sannan tace yawwa wai kuwa kinsan wannan Hajjo din da suka min aiki Ina nufin Unguwar su. Nurse tace kinsan tana aikin shara ne a Asibitin mu,na dai san kamar a Darmanawa aka ce take amma bansan gidan ta ba. Asiya tace Allah sarki Dan Allah ko zaki iya samo min lambarta sai dai dan Allah karki ce ni ce, ina son ne in ziyarce ta, na bazata, ta yi min mutunci kamar yarta ko jikarta muka zauna. Nurse tace "Ki tambayi megidanki mana ai kamar ba zai rasa ba. Asiya tace bashi da ita gaskiya, domin dashi mukayi maganar yace in tambaye ki.
Nurse tace to in naganta zan karba miki, in kuma bata bayarba shike nan.Sai bayan sun yi sallama zuciyar ta ke ce mata wai me kike son aikatawa ne Asiya.
Cikin sa a ba a jima ba,lambar ta shigo. Asiya kuwa ta kira Hajjo suka gaisa da ta tabbatar Hajjo bata gane ta ba, sai tace wai ita kawar Fati ce daga Maiduguri ta kira lambar Fati bata samu ba shine ta ke son a hada su. Hajjo tace Allah sarki ga shi kuwa Fati yau tun safe suka fita ni ma na kira layin nata ma baya shiga ko bata da caji ne. Gaban Asiya ya fadi, zufa ta karyo mata kenan dai suna tare, tace na shiga uku.ta darsa a zuciyarta ta. To dan Allah ko zaki tura min lambar ta wannan da nake ta kira din kamar tsohon layinta ne Intel ko shine har yanzu? Hajjo tace A a wannan MTN ne bari zan turo miki sai ki gwada,amma yau ko kunu bata sha ba ta fice tana sauri. Asiya tace Allah sarki ko ta samu aikin ne da tace min tana nema? Hajjo tace gurin wani ma ta tafi da zai saka sunan ta a aikin poliyo zan turo miki lambar yanzu sai anjima.
Asiya ta yi shiru tana nazari kenan karya Fati ta yi wa Hajjo dan ta fita da Halifa maganar aure suke yi kokuwa dai sakarcin su za su yi?
Kuka Asiya ta zauna tana rerawa, zuciyar ta tana tafasa wata zuciyar ta faɗa mata cewa kuka fa bazai zame mata mafita ba. Ta kira layin Halifa bai daga ba sai a kashi na uku, ya daga kafin ta yi magana ya rigata,muryarsa can kasa kasa, gashi sai taji gurin yana amsawa. Yace "Baby Yaya akwai damuwa ne? Ta ce dama Nurse ce muka yi waya tace min ya kamata a kai yaron nan allurar sati shidda yau ko zaka zo yanzu ka kai mu? Yace Baby tace dole sai yau ba za a bari gobe ba? Inda nake yanzu ba zan iya fitowa ba gaskiya. Gaban Asiya ya kuma yanke wa ya fadi, kenan wata ta fi su muhimmanci. Kin san ya za ayi?" Ya katse mata tunani. "Ki samu dan Adaidaita sahu sai ki hada ni da shi muyi magana,amma ki kula kar ki fita ba tare da kin rufe fuskar ki ba, kar ki hadu da wani. Asiya ta kuma hadiye fushinta tace Yaya ba kudi a gurina. Yace "Ki bude Sif din nan karama zan turo miki lambar da zaki saka ki bude yanzu sai ki dauki dubu goma in na zama free zan kira ki kinji, ki kula da kanki. Bai jira amsarta ba kawai ya kashe wayar. Hakan ya tabbatar miki da cewa suna tare da wata Zuciyar ta ta fada mata. Ta soma hasaso su shi da Fati da abubuwan da suke aikatawa.
Karar shigowar sako taji a wayar ta, lambobin da zata buda ma adanar kudin ce. Tana kuka ta bude, kudi ta gani kaloli na kasashen waje ta kirgi dubu goma ta kudinmu na Najeriya ta mayar ta rufe.