Sashe 65
Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
husnah ta gama hada abinci ta Shiga dakinta tayi wanka ta fito daure da towel a jikinta ta gansa zaune gefen gadonta tana ganinsa ta hada rai dan fushi takeyi ya saci kallonta suna hada ido tayi masa wata harara ya mike ya zuba hannuwansa cikin aljihunsa yace"fushi kikeyi dani saboda matata ta aikata zina?"damm gabanta ya fadi ta kallesa idonta jajir zatayi magana yace "Tou ki cigaba da fushin nima zan tafi inbarku kinga tafiyata"yasa kai ya fice kasa magana tayi sai zama datayi gefen gado tana tunanin me yaseer ke nufi shin besan kaddara bace?koko beyi imani da Allah bane?"nusrah ta shigo dakin cike da damuwa husnah tace "lafiya na ganki hakan meya faru?kin duba abincun yayi kuwa?"
"ehh yanzun nadawo daga dubawa Anty husnah,yaya muneeba nacan ta soma ciwo"kuuuuuu husnah taji cikinta na kugi cike da tashin hankali ta zaro Ido cikin sauri ta zura rigar data ajiye zatasa ta sa ta fice ko ganin gabanta batayi
*NAGODE KWARAI DA ADDUOI DA UZURIN DA KUKAIMUN ALHAMDULILLAH MUBEENA AN SALLAMEMU A ASIBITI SAIDAI JIKIN SAI A HANKALI A TAYATA DA ADDUA*
*GA MAI BUKATAR WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAI BIYA YA KARANTA*
07042277401
08036953516
*SLIMZY*✍🏻
51
tafe yaseer yake cikin mota tuki yakeyi hankalinsa gaba daya baya tare dashi tunanin cin amanar da muneeba tayi masa yakeyi don me husnah zatace ya yafe mata yanzun inda ciwo ta dauko fa?da yanzun tasa masa shi gaba daya hankakinsa a tashe yake dole ya dauki husnah suje a gwadasu horn yakeyiwa mutanen da sukai cincirindo a bakin titi shiru basuda niyyar matsawa a fusace ya fito daga motar "dalla kunzo kun taru a gefen titi sai kace...."cakk harshensa ya tsaya kallon hajiya rabi yayi jini na zuba a goshinta gefenta sadiya ce kwance warwas babu alamar rai a tattare da ita wani jiri ne ke neman daukarsa suka hada Ido da hajiya rabi kallonsa takeyi kamar tasanshi saidai ta kasa ganesa yaseer surutan da takeyi ne ya furgitasa "kun gani ko motace ta bugeni boka ya mutu yabar muneeba da ciki a jikinta tanacan a wani kauye yanzun gashi Alhaji yq sakeni umm kungani ko ninasan sharrin matarsa ne itace ta karya asirin da nayiwa Alhaji"damm gaban yaseer ya yanke ya fadi ya karasa inda take jikinsa na rawa wani mutumi daga bayansa yace "kai bawan Allah zaka kai kanka ne wajen wacce take tare da tsinuwar Allah bakajin kalaman da take fada ai bataga komiba yanzun tafara gani daga gani asiri tayi ya dawo mata shedaniya ka dawo Baya 'jikin yaseer a sanyaye ya hadiyi wani miyau mai kauri jikinsa babu kwari ya juya hajiya rabi ta mike ta ruko yaseer "karka tafi baka bani kudiba kabani kudi kawai ninasan me zanyi dasu"wani saurayi dake tsaye ya zabga mata mari ya fincike ta daga jikin yaserr ya hankadatw "yanzun nan mota zatazo a kaiki asibitin mahaukata a cillar dake daga ganin yadda kuke dambe a titi da abokiyar tafiyarki bakuda dangi "
"dambe?"yaseer yace a sanyaye
"ehh dambe sukeyi suna surutai mota tazo ta bugesu waccen kanta ya bugu a titi dayar kuwa har yanzun bata motsi kamar ma ta mutu"goge gumi sa yayi yace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun umm"
"kasan su ne?"da sauri yaserr ya girgiza kai 'bansanta ba"cikin sauri yabar wajen mutane na tsaitsaye ya Shiga cikin motarsa ya had'a kansa da sitiyarin mota yanajin jiniyar mota emergency na asibiti yaja motarsa yayi kwana ya koma gida dakyar yake tukin motar ya iso kofar gida kasa fitowa yayo daga ciki motar ya kunna karatun alkurani ya kwantar da kanta a jikin seat na mota
kuka husnah keyi shabe shabe rike da muneeba dake durkushe akan gwiwoyinta gabanta ke budewa wani abu na turowa sai tayi saurin hade kafa hajiya saude ta riketa da kyau ummah hadiza addua take tofa mata ta saki wata kara cikin ikon Allah saiga abu ya fado sukuf a kasa kallon juna sukeyi a razane cike da tsoro da furgici ummah hadiza ta kalla sak mutum saidai babu ido babu komi babu baki a fuskar sai hannuwa da kafafu jikinsa tamkar kifi tarwada fatar jikinsa bakinkirin kana kallon wasu jijiyoyi cikin abun baya numfashi,hajiya saude ta janye muneeba gefe da tuni ta suma tsananin masifar da take ciki da ciwo husnah ta mike ummah hadiza tace "dauko zaninta gashi can a rufe abun"da sauri husnah tayi yadda ummah hadiza tace ta rufe tana kokarin tabawa hajiya saude ta daka mata tsawa "ke husnah bakida hankaline zaki taba wanan halittar a tare dake ga juna biyu kinadashi salon ki janyo mana fitina dama dakyar muka rabu da fitinannen aljanin nan"jiki ba kwari husnah ta fito tayi gumi kaca kaca mahaifiyarta ce ta shigo parlorn dakin "yadai husnah ina muneeba?ta haihu kuwa"gyada mata kai husnah tayi tana kokarin fita hajiya zainab ta daga hannu sama cikin farin ciki tace "Alhamdulillah "ta kutsa kai cikin dakin ummah hadiza na shafawa muneeba ruwa a fuska a hankali ta bude idonta tana kallon sama wani zugi da radadi ne takeji a kasanta ta motsa a hankali tace "washhh wayyoo Allah"ta kasa hada kafafuwanta hajiya saude wani takaici taji ya tsaya mata a wuya tsananin tsanar hajiya rabi taji da haushin ita kanta muneebar tace "gaba ki sake wanan kuskuren kindaiga ishara na tabbatar mu da wani gidan ne ko wata zuriar ne saidai kibi mahaifiyarki kusan yadda zakuyi amma dayake mahaifinki jininmu ne bazamu taba barin jininsa ya wulakanta munada rayuwa ba muneeba"jikin muneeba yayi sanyi ta sunkuyar da kanta kasa momy dake tsaye tace "sannu muneeba sannu kinji Allah ya baki lafiya"ta jinjina kai dakyar ta motsa bakinta tace "Ameen momy"wasu hawaye masu zafi ke zubowa daga idanuwanta,
momy ta kalli sashen da aka rufe da zani ta kalli ummah hadiza tace "ummah hadiza abinda ta haifa babu rai ne?meta haifa?"
ummah hadiza ta nuna mata kafin tayi magana cikin azama momy ta bude zanin da sauri ta saki tace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"tsigar jikinta ta mike ta runtse idonta da sauri tabbas tayi gamo ummah hadiza tace "dodo ne ta haifa tayi arziki da yazo babu rai kuma yazo baa mutum ba da tasha bakar wuya kila Allah ne ya dubeta sakamakon tubar da tayi da wuri dikda saida taji wuya ta tuba"momy ta girgiza kai cikin sanyin jiki tace "ku daina fadin haka yanzun a kira yaserr a Kira malam yazo ya gani sai asan yadda zaayi da abun ko?"hajiya saude tace "hakan ya kamata amma yaserr baya daukar waya husnah ta sanar mun da yayi fushi yayi tafiyar sa ma koda tazo be gidan batasan inda yaje ba"
muneeba wani abu taji ya caki zuciyarta wani radadi takeji a kirjinta wani irin kaunar mijinta takeji da tausayinsa son da takeyiwa yaseer a halin yanzun yafi wanda takeyi masa a baya fargabar rabuwa takeyi dashi idan yaseer ya rabu da ita tabbas bazata iya rayuwa cikin gidan ba bazata iya rayuwa tana ganinsa ba wutar sonsa ke ruruwa a zucuyarta batasan sanda ta fashe da kuka ba hajiya saude da ummah hadiza suka shiga da ita toilet tare sukai mata wanka kafin su fito Momy ta gyara wajen ya fice,
husnah ta dade tsaye tana kwankwasa kofar motat tasan shine dikda fitowarta bataga motar ba tasan ya dawo tana hangensa ta glas din motar daya dan bude dago kai yayi fuskarsa jajir cikin tsananin takaici yayi tsaki yasan husnah ce yasa keyy ya Bude motar tanajin alamar budewa tasa hannu ta bude murfin motar sukai Ido hudu da yaseer ya zuba mata ido itama shi take kallo ta kasa motsawa dakyar ya bude baki yace"kinzo ki rokeni in zauna da muneeba ne?ko me kikazoyi?"ya watsa mata wani kallo tq sunkuyar da kanta kasa ta danne zucuyarta ta shiga ta rufe motar ta ruko hannunsa kasa kwacewa yayo cikin wani irin salo take murza tafin hannusa ta kwantar da kanta a kafadarsa murya kasa kasa cike da shagwaba tace"yanzun fushin yar uwata ya shafeni kenan?saboda nace ka sassauta hukunci kada ka yanke hukunci cikin fushi?bance saika zauna da muneeba ba ina tsananin tausayinta dikda tayi maka babban laifi sanan karka manta mahaifiyarta tabar gidan ta gudu baasan inda takeba"cike da karfin hali yace "ehh anyi asibitin mahaukata da ita yar uwarta kuma ta mutu an dauki gawarta"da sauri husnah ta kallesa "yaya yaserr kasame kake fada kuwa ko tsabar fushi yasa kawai kake zaro maganganu kamar wanda kwakwalwarsa ta samu matsala?'ya tallabo habarta yana girgiza kai "ko kadan husnah shine sanadin fasa fitata shine sanadin da kika sameni cikin motar nan nashiga damuwa yau nakara tabbatar da cewa mai rai baa bakin komi yakeba sanan dan adam dik iskancinsa zaiyitayi Allah na kallonsa yayi masa talala saidai da zarar ya damkesa to fa zai zama abun tausayi abun misali sanan darasi ga sauran mutane"jikin husnah yayi sanyi ta zuba masa ido cike da kwalla ya kwashe komi abinda ya faru ya fada mata jikinta ne ya kama rawa ta kasa magana ta rushe da kuka ta fada jikinsa tana shashekar kuka rungumeta yayi cikin sigar lallashi da kalamai masu dadi yake lallashinta yasamu tayi shiru ya shafa fuskarta ya hade bakinsu waje daya ya soma kissing dinta cikin wani irin salo yake tafiyar da ita yana shasshafa ta horn din mota yasa yayi furgigit ya saketa ya kalli motar dake gabansa ya girgiza kai yace "hafeez ne naga kamar shida malam ne kota haifo dan boka ne?"hararsa husnah tayi ya hade rai Shi kuma ta kauda kai tace"ta haihu tun dazun?"ya kalleta ta jinjina masa kai ta kauda kanta gefe ta bude motar ta fita jiki a sanyaye shima ya Bude motar ya fito hafeez yace "ah ah kune a cikin mota kuke zuba soyayya?"cikin kasa kasa da murya hafeez yace hakan! yaseer yayi masa wata harara suka dunguma cikin gidan.....
"ehh yanzun nadawo daga dubawa Anty husnah,yaya muneeba nacan ta soma ciwo"kuuuuuu husnah taji cikinta na kugi cike da tashin hankali ta zaro Ido cikin sauri ta zura rigar data ajiye zatasa ta sa ta fice ko ganin gabanta batayi
*NAGODE KWARAI DA ADDUOI DA UZURIN DA KUKAIMUN ALHAMDULILLAH MUBEENA AN SALLAMEMU A ASIBITI SAIDAI JIKIN SAI A HANKALI A TAYATA DA ADDUA*
*GA MAI BUKATAR WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAI BIYA YA KARANTA*
07042277401
08036953516
*SLIMZY*✍🏻
51
tafe yaseer yake cikin mota tuki yakeyi hankalinsa gaba daya baya tare dashi tunanin cin amanar da muneeba tayi masa yakeyi don me husnah zatace ya yafe mata yanzun inda ciwo ta dauko fa?da yanzun tasa masa shi gaba daya hankakinsa a tashe yake dole ya dauki husnah suje a gwadasu horn yakeyiwa mutanen da sukai cincirindo a bakin titi shiru basuda niyyar matsawa a fusace ya fito daga motar "dalla kunzo kun taru a gefen titi sai kace...."cakk harshensa ya tsaya kallon hajiya rabi yayi jini na zuba a goshinta gefenta sadiya ce kwance warwas babu alamar rai a tattare da ita wani jiri ne ke neman daukarsa suka hada Ido da hajiya rabi kallonsa takeyi kamar tasanshi saidai ta kasa ganesa yaseer surutan da takeyi ne ya furgitasa "kun gani ko motace ta bugeni boka ya mutu yabar muneeba da ciki a jikinta tanacan a wani kauye yanzun gashi Alhaji yq sakeni umm kungani ko ninasan sharrin matarsa ne itace ta karya asirin da nayiwa Alhaji"damm gaban yaseer ya yanke ya fadi ya karasa inda take jikinsa na rawa wani mutumi daga bayansa yace "kai bawan Allah zaka kai kanka ne wajen wacce take tare da tsinuwar Allah bakajin kalaman da take fada ai bataga komiba yanzun tafara gani daga gani asiri tayi ya dawo mata shedaniya ka dawo Baya 'jikin yaseer a sanyaye ya hadiyi wani miyau mai kauri jikinsa babu kwari ya juya hajiya rabi ta mike ta ruko yaseer "karka tafi baka bani kudiba kabani kudi kawai ninasan me zanyi dasu"wani saurayi dake tsaye ya zabga mata mari ya fincike ta daga jikin yaserr ya hankadatw "yanzun nan mota zatazo a kaiki asibitin mahaukata a cillar dake daga ganin yadda kuke dambe a titi da abokiyar tafiyarki bakuda dangi "
"dambe?"yaseer yace a sanyaye
"ehh dambe sukeyi suna surutai mota tazo ta bugesu waccen kanta ya bugu a titi dayar kuwa har yanzun bata motsi kamar ma ta mutu"goge gumi sa yayi yace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun umm"
"kasan su ne?"da sauri yaserr ya girgiza kai 'bansanta ba"cikin sauri yabar wajen mutane na tsaitsaye ya Shiga cikin motarsa ya had'a kansa da sitiyarin mota yanajin jiniyar mota emergency na asibiti yaja motarsa yayi kwana ya koma gida dakyar yake tukin motar ya iso kofar gida kasa fitowa yayo daga ciki motar ya kunna karatun alkurani ya kwantar da kanta a jikin seat na mota
kuka husnah keyi shabe shabe rike da muneeba dake durkushe akan gwiwoyinta gabanta ke budewa wani abu na turowa sai tayi saurin hade kafa hajiya saude ta riketa da kyau ummah hadiza addua take tofa mata ta saki wata kara cikin ikon Allah saiga abu ya fado sukuf a kasa kallon juna sukeyi a razane cike da tsoro da furgici ummah hadiza ta kalla sak mutum saidai babu ido babu komi babu baki a fuskar sai hannuwa da kafafu jikinsa tamkar kifi tarwada fatar jikinsa bakinkirin kana kallon wasu jijiyoyi cikin abun baya numfashi,hajiya saude ta janye muneeba gefe da tuni ta suma tsananin masifar da take ciki da ciwo husnah ta mike ummah hadiza tace "dauko zaninta gashi can a rufe abun"da sauri husnah tayi yadda ummah hadiza tace ta rufe tana kokarin tabawa hajiya saude ta daka mata tsawa "ke husnah bakida hankaline zaki taba wanan halittar a tare dake ga juna biyu kinadashi salon ki janyo mana fitina dama dakyar muka rabu da fitinannen aljanin nan"jiki ba kwari husnah ta fito tayi gumi kaca kaca mahaifiyarta ce ta shigo parlorn dakin "yadai husnah ina muneeba?ta haihu kuwa"gyada mata kai husnah tayi tana kokarin fita hajiya zainab ta daga hannu sama cikin farin ciki tace "Alhamdulillah "ta kutsa kai cikin dakin ummah hadiza na shafawa muneeba ruwa a fuska a hankali ta bude idonta tana kallon sama wani zugi da radadi ne takeji a kasanta ta motsa a hankali tace "washhh wayyoo Allah"ta kasa hada kafafuwanta hajiya saude wani takaici taji ya tsaya mata a wuya tsananin tsanar hajiya rabi taji da haushin ita kanta muneebar tace "gaba ki sake wanan kuskuren kindaiga ishara na tabbatar mu da wani gidan ne ko wata zuriar ne saidai kibi mahaifiyarki kusan yadda zakuyi amma dayake mahaifinki jininmu ne bazamu taba barin jininsa ya wulakanta munada rayuwa ba muneeba"jikin muneeba yayi sanyi ta sunkuyar da kanta kasa momy dake tsaye tace "sannu muneeba sannu kinji Allah ya baki lafiya"ta jinjina kai dakyar ta motsa bakinta tace "Ameen momy"wasu hawaye masu zafi ke zubowa daga idanuwanta,
momy ta kalli sashen da aka rufe da zani ta kalli ummah hadiza tace "ummah hadiza abinda ta haifa babu rai ne?meta haifa?"
ummah hadiza ta nuna mata kafin tayi magana cikin azama momy ta bude zanin da sauri ta saki tace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"tsigar jikinta ta mike ta runtse idonta da sauri tabbas tayi gamo ummah hadiza tace "dodo ne ta haifa tayi arziki da yazo babu rai kuma yazo baa mutum ba da tasha bakar wuya kila Allah ne ya dubeta sakamakon tubar da tayi da wuri dikda saida taji wuya ta tuba"momy ta girgiza kai cikin sanyin jiki tace "ku daina fadin haka yanzun a kira yaserr a Kira malam yazo ya gani sai asan yadda zaayi da abun ko?"hajiya saude tace "hakan ya kamata amma yaserr baya daukar waya husnah ta sanar mun da yayi fushi yayi tafiyar sa ma koda tazo be gidan batasan inda yaje ba"
muneeba wani abu taji ya caki zuciyarta wani radadi takeji a kirjinta wani irin kaunar mijinta takeji da tausayinsa son da takeyiwa yaseer a halin yanzun yafi wanda takeyi masa a baya fargabar rabuwa takeyi dashi idan yaseer ya rabu da ita tabbas bazata iya rayuwa cikin gidan ba bazata iya rayuwa tana ganinsa ba wutar sonsa ke ruruwa a zucuyarta batasan sanda ta fashe da kuka ba hajiya saude da ummah hadiza suka shiga da ita toilet tare sukai mata wanka kafin su fito Momy ta gyara wajen ya fice,
husnah ta dade tsaye tana kwankwasa kofar motat tasan shine dikda fitowarta bataga motar ba tasan ya dawo tana hangensa ta glas din motar daya dan bude dago kai yayi fuskarsa jajir cikin tsananin takaici yayi tsaki yasan husnah ce yasa keyy ya Bude motar tanajin alamar budewa tasa hannu ta bude murfin motar sukai Ido hudu da yaseer ya zuba mata ido itama shi take kallo ta kasa motsawa dakyar ya bude baki yace"kinzo ki rokeni in zauna da muneeba ne?ko me kikazoyi?"ya watsa mata wani kallo tq sunkuyar da kanta kasa ta danne zucuyarta ta shiga ta rufe motar ta ruko hannunsa kasa kwacewa yayo cikin wani irin salo take murza tafin hannusa ta kwantar da kanta a kafadarsa murya kasa kasa cike da shagwaba tace"yanzun fushin yar uwata ya shafeni kenan?saboda nace ka sassauta hukunci kada ka yanke hukunci cikin fushi?bance saika zauna da muneeba ba ina tsananin tausayinta dikda tayi maka babban laifi sanan karka manta mahaifiyarta tabar gidan ta gudu baasan inda takeba"cike da karfin hali yace "ehh anyi asibitin mahaukata da ita yar uwarta kuma ta mutu an dauki gawarta"da sauri husnah ta kallesa "yaya yaserr kasame kake fada kuwa ko tsabar fushi yasa kawai kake zaro maganganu kamar wanda kwakwalwarsa ta samu matsala?'ya tallabo habarta yana girgiza kai "ko kadan husnah shine sanadin fasa fitata shine sanadin da kika sameni cikin motar nan nashiga damuwa yau nakara tabbatar da cewa mai rai baa bakin komi yakeba sanan dan adam dik iskancinsa zaiyitayi Allah na kallonsa yayi masa talala saidai da zarar ya damkesa to fa zai zama abun tausayi abun misali sanan darasi ga sauran mutane"jikin husnah yayi sanyi ta zuba masa ido cike da kwalla ya kwashe komi abinda ya faru ya fada mata jikinta ne ya kama rawa ta kasa magana ta rushe da kuka ta fada jikinsa tana shashekar kuka rungumeta yayi cikin sigar lallashi da kalamai masu dadi yake lallashinta yasamu tayi shiru ya shafa fuskarta ya hade bakinsu waje daya ya soma kissing dinta cikin wani irin salo yake tafiyar da ita yana shasshafa ta horn din mota yasa yayi furgigit ya saketa ya kalli motar dake gabansa ya girgiza kai yace "hafeez ne naga kamar shida malam ne kota haifo dan boka ne?"hararsa husnah tayi ya hade rai Shi kuma ta kauda kai tace"ta haihu tun dazun?"ya kalleta ta jinjina masa kai ta kauda kanta gefe ta bude motar ta fita jiki a sanyaye shima ya Bude motar ya fito hafeez yace "ah ah kune a cikin mota kuke zuba soyayya?"cikin kasa kasa da murya hafeez yace hakan! yaseer yayi masa wata harara suka dunguma cikin gidan.....