← Book details Duhu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 68

Sashe 59

Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

momyn tace "ke waye abokinki kuma?har wani aboki gareki bansaniba?kodai Yaseer kike magana?"husnah ta jijiiga kai tace "ah ah momy inada aboki bakisanshiba yana zuwa ya daukeni mu fita yawo muje can wani waje"momyn tace "kin cika sambatu husnah"ta tafi tabarta na shigo ta rungume ni sosai tanajin dadi yarinyar ta shiga raina sosai yakai daddare ina zuwa wajenta sau dayawa mahaifiyarta zata farka cikin dare ta ganta zaune tana wasa tana magana ita kadai lokacin tana shekara daya da wata takwas bakinta ya bude nine na koyawa husnah magana sosai,bata damuwa zatace "Kar kiyi baccin kiyita zama"mahaifinta yasha tambayarta dawa husnah ke surutai a shekararta bekai tayi wayau haka ba dole akwai wanda ke koya mata hakan amma bata damuwa bata taba bincikar metakeyi ba dikda cikin surutanta tana fada mata abokinta kaza abokinta kaza,tsananin son da nakeyiwa yarinyar yasa bana zama cikin jinsin mu kullum ina tare da ita sakamakon mun shaku har yakai idan zan tafi kuka takeyi zata bini,tsananin kaunar da nakeyi mata mahaifiyarta tasha nemanta ta rasa ta dudduba wurare bata gantaba bata damuwa saidai tace tasan tanacan tana wasa da yaseer sau dayawa ba wajen yaserr takeba wajena take"husnah ta kalli mahaifiyarta idonta jajir cikin tsananin damuwa da jin haushinta

malam yace "tabdijan, Tou ya akayi ka saceta?"yayi girgiza yayi kuww hade da kururuwa yanason guduwa dik inda ya dosa babu hanyar gudu malam ya daddauresa tamau yace "wata rana ana magriba husnah tana wasa wajen gate dinsu yaseer ya taho zashi masallaci ya rukota taxo wajensa tanayi masa surutai lokacin shekararta biyu da sati biyu yace"ki jirani husnah zanzo yanzun bari naje nayi sallah nadawo"ta makale kafada tasa kuka ya fice ya rufo gate din ina tsaye bata ganniba tana juyowa muka hada ido tausayinta ya kamani ba kalli cikin gidan ba kowa sai ita kadai tana wasa mahaifiyarta bata damu da killaceta ba a wanan lokacin manyan shedanun aljanu lokacin suke yawo lokacin cikin gidansu dik mutanenmu ne sun baza kaya tanata yawo na rukota"zaka tafi dani?"tace idonta cike da hawaye na gyada mata kai tace "katafi dani abokina kaji?"na jinjina mata kai nima inasonta banaso daidai da minti daya in nisanceta ina samun matsala sosai da mahaifiyata akan husnah saboda bana zama cikinsu ranan nasawa raina tafiya da ita haka na dauketa natafi da ita cikin iska......bayan natafi da ita nasamu matsala sosai da yan uwana yadda suke kyamarta babu wanda yake sonta hakan yasa dik inda zani da ita nake zuwa nasamu matsala sosai da mahaifanaa akanta tun basu amince da itaba ganin son da nakeyi mata zasu rasani yasa suka amince da ita nina bude mata ido take ganin kowa a suffar mutane a duniyar mu dik wani abu da takeso inayi Mata shi ko menene koda zan cutu kakata wadda husnah tasani da goggo kande itace ta rikemun ita take kula da ita babu me yunkurin cutar da ita dik wanda yace zaiyi hakan kuwa sai inda karfina ya kare a haka nake rayuwa da husnah bana bata abincinmu abincinta nake bata ina zuwa da ita Rafi insa hannu in kamo kifi in gasa mata ta saba dani nasaba da ita tsananin shakuwarmu tasa nasan aurenta ne kadai zaisa mu dawwama tare saidai a yan uwana aljanu akwai mesona wadda itace narjisu itace silar dawo da husnah duniyarku wanda a yanzun take hannunku"

hajiya saude ta kalli momyn husnah ta girgiza kai tace "sakacinki ya jefa husnah cikin halin da take ciki tabbas nakara gasgata cewar baason barin jarirai su kadai a daki batare da anyi musu addua ko ankara musu wani abuba gashi ya tabbata innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"ta zauna dirshan ta fashe da kuka,

kururuwa Abraham yakeyi ya soma rokon malam "Dan Allah kada ka rabani da husnah ina tsananin kaunarta karku rabamu itama tana sona husnah tasan irin gwagwarmayar da nasha akanta ko kafin na aureta"malam ya jinjina kai tabbas akwai sabo da shakuwa tsakanin husnah da Abraham saidai aljani bashida amana kuma bashida alkawari dik yadda zaiso karya kashesa yasan tunda yana sonta bazai taba daina bibiyarta ba,

gyaran murya malam yayi yace "ku aljanu bakuda amana kuma bakuda alkawari idan har na kyaleka yanzun na tabbatar zakayi abinda yafi hakan tunda abinda ke cikinta kake hari idan har na kyaleka na tabbatar abinda zakayi gaba sai yafi wanan dikda irin tausayin da kabani da ganin bakada laifi wajen daukarta mahaifiyarta ce mai laifi"

Abraham yana yawo cikin dakin yana rimi yana hankoro "koda kun kasheni ko kun illatani da soyayyarta na rayu kuma bazan taba daina sonta ba"

furucun da yayi yasa malam yayi yunkuri yayi addua ya tofa masa sanan ya soma karatun alkurani cikin dakin mai girma yana daga murya Abraham ihu yakeyi cikin dakin cikin tsananin azaba,

yadda yake kururuwa da kuwwa ba karamin tausayi yabawa husnah ba kuka ta fashe dashi tanaso ta hana a kashesa ta kalli Yaseer ya cije lebe ta tashi dakyar wani jiri ke daukarsa har yanzun kafadarsa kamar ba tasa ba ihu Abraham yakeyi yana fadin "zaka kasheni kana konani karka kasheni koda ka kasheni zan mutu ne da soyayyar husnah a cikin zuciyata.....

cikin momy ne ya karta mararta taji tanayi kamar zata bude ta durkushe kasa cikin tsananin jin ciwo tace "wash marata".....da sauri ummah hadiza da hajiya saude sukayi kanta....

******
gumi ke karyowa daddy a dakin innah tace "haka zakayi hakuri da auren hajiya rabi da kayi badamasi dikda yadda kake nunamin kamar baa cikin hayyacinka kake ba"wayarsa ce tayi ringing cikin damuwa ya cirota a aljihunsa ya kalla yace "ummah hadiza ke kira"ya dauka ya kara a kunne yana jiyo karatun alkurani sanan cikin numfarfashi yakejin ummah hadiza na fadin "badamasi kazo fa zainab zata haihu"ta kashe wayar ya yunkura ya mike takalmin hagu a dama yasa innah tace "kai lafiya ina zaka meke faruwa"dakyar yace "zainab ce zata haihu"

"banga ta zama ba nima"innah ta yunkura a waje ta yafa mayafinta ta bi bayan daddy dako ganin gabansa bayayi.....

*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BANYAFEBA*

07042277401
08036953516

*SLIMZY*🫣kuyi maneji yau sunday oga na nan.....🤪

47
a gaggauce ummah hadiza da hajiya saude suka shiga da momy cikin gidanta suna kokarin shiga da ita cikin daki hajiya rabi ta taresu "lafiya?meke faruwa meyasameta"tana kokarin rike momy hajiya saude ta dakatar da ita "ba sai kin riketa ba ina mijin naku yake?"tabe baki tayi ta harde hannuwanta a kirjinta tace "ita zan tambaya tunda ai tare na gansu suka fita"yunkurin nishi momy takeyi gumi ke karyo mata basubi ta kan hajiya rabi ba suka Shiga daki da ita horn din motar daddy ummah hadiza taji ta fito da sauri sukai arangama da daddy "ina zainab din take?"

"tana cikin daki tare da saude inaga abun nan akan gaba take ko zamu barta a gida karta haihu a mota?"gumi daddy ya goge innah ce ta shigo cikin sauri ummah hadiza ta tarbeta "ah ah innah tare kuke kenan dashi"

"ehh yaje gidana muna magana bamu karasa ba saiga kira ina zainab din take ko zamu tafi asibiti ne?"muneeba ce cikin takun kasaita ta shigo sashensu tana tura ciki dakyar innah ta kalleta tace "ikon Allah ke kuma fa? wanan ciki muneeba kodai yaya goma ne ciki haka yayi girman?"murnushi muneeba tayi tace "sannunku ina yini?"hajiya rabi ta taho da kissa ganin daddy "dama yanzun zan kiraka ince ko zakazo muje akai zainab asibiti?"wata harara daddy ya watsa Mata sanan cikin basarwa yace "ummm gani nazo ai sun kirani"yaja gauron numfashi ya sauke ya harde hannuwansa a kirjinsa ya koma gefe cikin damuwa muneeba kallon yadda daddy ya amsawa hajiya rabi tayi da mamaki ta kalli mahaifiyarta wadda ta ruko hannunta dakyar suka nufi sashenta.....

ummah hadiza tabisu da kallo innah ma kallon muneeba takeyi cike da mamaki tace "ikon Allah kenan ku duba yarinyar nan cikin daban uwar jikin daban ni gaba daya tausayi take bani anya bazaaje aji yara nawa ne a cikin ba?"murmushin takaici ummah hadiza tayi "tou ai ance baaga cikin ba"dafe kirji innah tayi zatayi magana hajiya saude ta fito ta jike da gumi sharkaf cikin farin ciki ta rangad'a gud'a tace "Alhamdulillah Zainab ta sauka"jikin daddy na rawa yace "haba metasamu ina take?"yana kokarin shigewa dakin hajiya saude ta dakatar dashi"kada ka Shiga ban gama da itaba inaso ummah hadiza mu taimaka mata nadai yanke cibiya ta sauka tasamu yara biyu maza"cakkk daddy yayi ya kasa magana yace "biyu maza?dagaske kikeyi saude?"innah cikin farin ciki ta daga hannu tace "Alhamdulillah Alhamdulillah "ta kwashi rawa ummah hadiza da hajiya saude suka shige....

*****
Abraham ihu yakeyi tin yana ihu ya gagara sai wani irin gurnani yakeyi wani irin hayaki ke tashi a dakin gabaki dayansu tari sukeyi cikin dakin husnah idonta dik ya firfito malam ya tsagaita da addua da karatun da yakeyi jin shiru "ka Kone ka yarda cewar zaka rabu da ita?"a wahale Abraham yake cikin wani yanayi yacev"na kone malam kayimun illar da bazan tashiba bazan moruba inaji a jikina mutuwa zanyi zanbar wanan duniyar da soyayyar husnah bil'adamar dana rayu da ita da tsananin kaunarta"yana gama maganar sukaji wata irin kara a tsorace yaseer yayi tsalle kan gadon da husnah ke zaune ya janyota ya rungumeta dakin ke wani irin juyawa wata murya sukaji ta mace "Assalamu alaikum"da sauri Yaseer ya gyara zama jin muryar yasan muryar bazai taba mantawa da itaba yace a hankali kowa na jinsa "narjisu....."malam ya amsa sallamar cikin kwarin gwiwa yace "ke wacece?"basa ganinta dukkansu kowa waige waige yakeyi tace "ni aljana ce narjisu malam ka kona Abraham kayi masa kunar da bazai sake moruwaba karshema ya mutu babu abinda yaja masa face taurin kansa da rashin jin magana da tsananin soyayyar da yakewa god'oyarku"malam yayi hamdala ya kalli yaserr murmushi yayi "zan taimaka masa zan daukesa zan tafi dashi sanan nayi muku alkawarin bazai sake dawowa ba"
Chapter 59 · 0% Book details