Sashe 41
Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*****
muneeba kwance tana sauke numfashi zazzabi ya rufeta tsananin kishi da damuwa yasa ciwon gaske ya kamata yaseer cikin sassarfa ya shigo dakin da sallamarsa ummah ya gani zaune tana rike da hannun muneeba sai Anty sadiya data jefesa da wani mugun kallo ya karasa yana fadin "muneeba sannu meyasameki ummah meke faruwa?"hawaye ne kebin fuskar muneeba tana kallonsa cikin tuhuma gashin kansa ta kalla taji gabanta ya fadi ta mike zumbur ta zauna ummah ta rukota ganin yadda tayi "sannu muneeba sannu kinji?"Yaser jiki a sanyaye yake kallonta ta fita hayyacinta yace "shirya mutafi asibiti"ta fashe da kuka hajiya rabi da sadiya suka fice a dakin yana kokarin riketa cikin tausayawa tace "kada katabani nidai karka tabani"ta kwalla kara yaji tsoro kardai itama ta kamu da aljanun.....
a wahalce Abraham ya warware daga daurin da babansa yayi masa tare da taimakon zabariyya wadda ta kasa jure ganinsa a daure tsananin kaunar da take masa.....
*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BAN YAFEBA*
08036953516
07042277401
*SLIMZY*✍🏻
35
Tallabo husnah momy tayi tace "mikomun ruwan gorarcan yusrah"da sauri yusrah ta dauka ta mikawa momy addua ta tofa ciki sanan ta guntsi ruwan a bakinta ta fesa mata a fuska wata wawuyar ajiyar zucuya husnah tayi ta bude idanuwanta tana binsu da kallo take ta tuno da abinda ta ganni ta kalli kujerar bataga kowa ba ta yunkura jikinta ciwo yakeyi mata momy ta d'agota zafi taji ya ziyarceta a kasanta momy ta tsura mata ido tana karantarta tace "husnah meyake damunki?kafarkice takeyi miki ciwo?"husnah ta girgiza kai take ta tuno da yaseer yadda ya cakud'ata daren jiya ruwa ne ya kawo a idanuwanta Momy ta taimaka mata ta zaunar da ita a kujera tace "fadamun meyake damunki?wanan aljanin yazo ne?"sunkuyar da kai husnah tayi hawaye na zubo mata hankalin hajiya saude yayi mugun tashi tace "kifadamun yaseer yayi miki wani abu ne?"gyada mata kai tayi momy ta soma tafa hannu ta kalli yan matanta biyu tace "kubani waje"suka bar wajen tace "yaseer ya taba jikinki ko?"ta jinjinawa momy kai ta fashe da kuka tace "nafada masa banaso kada yayimun shine yayi fushi ni kuma banason yayi fushi kinga yayi hatsari saboda ni"mommy ta jinjina kai tace "tabdijan lallai yaseer zanci ubansa a gidan nan wato ko kunyata baiji ba ya kusanceki? innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"husnah ta share hawayenta ta sunkuyar da kai momy ta matsa mata da plate din soyayyen dankali da kwai ta had'a mata tea mai zafi cike da tausayawa "ci abincinki kinji?kirabu dashi zaizo gidan nan ya sameni"husnah cakula abincin takeyi gaba daya hankalinta baya wajen ta juyo ta kalli plate din abincin wasu tsutsotsi ta gani cikin plate din manya manya suna yawo ta kalli cup din wani irin ruwa bakinkirin ne ciki ta kalli momy,"ci abincin mana husnah"girgiza kai husnah tayi tace "momy tsutsotsi ne gasu nan cikin kwanon bazan iyaci ba"momy ta kalli dankalin ta kalli kofin ruwan tea din"girgiza kai tayi ta mike tabar wajen inuwar mutum kawai ta gani a gabanta tana d'ago kai sukai ido hudu da Abraham zabura tayi ta mike wani irin kallo yakeyi mata wasu jijiyoyi ne koraye suka fito cikin idonsa wajen bakin idanuwansa ya koma mai ruwan toka farin kuma ya koma ja ta matukar tsorata momy ce ta dawo da karatun kurani yayiwa momy wani kallo ya bace,
a furgice Momy taga husnah tace "yadai husnah?"ta girgiza kai tace "momy banajin yunwa Bari inje wajensu yusrah kitchen na tayasu aiki"momy ta jinjina kai a hankali take taka kafarta ta girgiza kai kawai ta shiga laluben layin yaseer bata samesa ba dole zataje gidan su yau din nan....
*****
rungume muneeba yayi cikin sigar lallashi yace"kiyi shiru kiyi Hakuri nima bansan cewar hakan zai faru zam kwana can ba banje da niyyar kwana ba ankira malam ne mai bada magani shine na tsaya in shafawa husnah magani tunda ni mijinta ne"tana kokarin kurban ruwan tea batasam lokacin data furzar ba ta shiga tari sakamakon sarketa da yayi idanuwanta suka firfito ya rukota"lafiya?menene muneeba?"yake tambayarta cikin kulawa tace "yaseer ni yanzun kake fadawa cewa ka shafawa husnah magani?"wani kishi ne ya rufe mata idanuwa tace"kaje kaci amanata kenan?me kukayi daga shafa maganin?"cikin daga murya take masa magana abinda yaseer ya tsana kenan a rayuwarsa ya harzuka cikin bacin rai yace "kwanciya nayi da ita ko itadin ba matata bace?ko karuwa ce ita?"bude baki tayi tana kallonsa ta dafe kirjinta hawaye ya soma zuba a idanuwanta tace "yaseer ni kake fadawa ka kwanta da husnah?"
"na kwanta da ita me zakiyi?"yace yana kokarin mikewa ta rushe da kuka har ya kai kofa ya tsaya tausayinta yad'an kamasa dikda haushinta da yakeji ta yaya zata rinka challenging dinsa?yasan tana bashi tausayi saboda cikinsa da take dauke dashi ganin ya tsaya kawai ta soma wani irin tari tasa hannunta a wuyanta da sauri ya dawo cikin dakin "kingani ko?kinga abinda nake fada miki muneeba meyasa kikeso ki kashe kanki ne akan abinda Allah ya halarta?husnah fa matatacw kuma kece kika matsamun da bimcike yasa nafada miki abinda nafada miki har ya bata miki rai"ta sunkuyo kawai ta soma kwara amai a wajen ya dafe kansa daya dau zafi,ya furgar da iska mai zafi daga bakinsa ya dafe kansa ya runtse idonsa husnah ya tuno yadda ta mike tana d'ingisa kafa ko wani hali take ciki oho,tambayar da yayiwa kansa kenan sam bayason nisa da ita matsowa yayi ya zubawa muneeba ido yadda take kwara amai tana gamawa ta durkushe ta soma myrkususun ciwon ciki hankalin yaseer yayi mugun tashi nan ya tube rigarsa kasantuwar weekend ne ba aiki ya soma gyara wajen sanan ya dawo ya ciccibeta ya nufi toilet da ita da kansa ya tube mata kayan jikinta ta faki idonsa tayi murmushi dikda tsananin kishin dake cin ta tayi hakan ne dan ta d'aga masa hankali tsuru yayi da ido yana kallonta fuskarta ce take masa gizo tana komawa husnah yasan ba husnah bace tsabar tunanin husnah da yakeyi ne ya janyo hakan ko taci abinci ma bai saniba yayi mata wanka ya fito da ita ya nad'eta a towel sanan yana kokarin fita cikin murya mai tsananin Jin jiki tace "sweetheart karka tafi kabarni nasan nibaka sona dama husnah kakeso"cak ya tsaya badan ransa yaso ba ya dawo cikin dakin ya zauna gefen gado ya cije lebe yana kallon kiran momy ya kasa dauka tsoron me zata fada masa yakeyi haka kawai yake jin kansa cikin fad'uwar gaba....
******
daga kitchen ta fito tana jin fitsari nusrah tace "Anty husnah ina zakijene naga har yanzun kina dingisa kafa"murmushi tayi "fitsari nakeji nusrah yanzun zan dawo ai naji sauki"ta fito daga kitchen din yusrah na ganin ta fita ta matso kusa da yar uwarta tace "nifa a tsorace nake da Antu husnah gani nakeyi kamar ba ita bace kinsan aljanun nan"nusrah tayi ajiyar zuciya tace "haka ne amma fa yau kam tabbas itace saidai alamunta sum nuna tana cikin damuwa"suka girgiza kai dukkansu suka cigaba da aikinsu,
tana shiga dakin kofa ta rufe cikin sauri take kokarin shiga toilet din taga mutum kwance kan gadonta ta murza idonta "wanene waye wanan kwance akan gado na"a sanyaye tayi maganar d'agowa yayi daga kwanciyar da yayi kafin kiftawar ido har ta gansa a gabansa cikin fargaba da faduwar gaba take kallonsa ta tsaresa da Ido shima ita yake kallo saidai baizo mata a kamar ban tsoroba a kammanninsa ta gansa fad'awa jikinsa tayi ya tureta gefe tsananin tausayinsa yasa batasan lokacin data fada jikinsa ba kallomsa takeyi cikin tsananin mamaki ya girgiza kai ya cije baki fuskarsa tayi bakin kirin yace"Babu sauran soyayyarki a cikin zuciyata husnah"dam gabanta ya fadi tayi masa wani kallo ta kauda kanta gefe bugun zucuyarta ya tsananta yace"kinci amanata husnah dama ku bil'adama haka kuke amma zan koya miki hankali zakisan kin cutar dani husnah inaji ina gani jiya kika mikawa d'an uwanki bil'adama jikinki ya kwanta dake lokacin da kike tsananin kaunata kin mance yadda naso in kusanceki kika hanani?"hawaye ke zubowa a idanuwansa yana kallonta jikinta a sanyaye momy ta turo kofar ta shigo ganinta tsaye cak yasa tace"lafiya?"girgiza kai tayi bata gansa ba yana cikin dakin kuma cikin jin haushinta yake kawai ya shige jikinta, momy tace "husnah zan fita zani gidansu innah daga nan zan wuce gidanku can akwai maganar da zamuyi"jinjinawa momy kai kawai akayi ta fice dikda jikinta bai bataba tasan wanan ba husnah bace saidai ta kasa gasgata hakan tana fita ya fita daga jikin husnah dakin ne ya shiga jujjuya mata cikin minti biyar kawai taga ko ina ya zama kogi ruwa nayo kanta ta fito aguje nusrah tana kokarin riketa ta bankadeta ta fadi kasa waje tayi tana gudu kamar zararriya nusrat ta window ta leka tana kwalawa mai gadi kira "karka bar Anty husnah ta fito"
Abraham harde hannuwansa yayi a kirjinsa daga gefe yana kallon yadda ta fita a hayyacinta tsananin tsoro da furgici ta kalli gidan sauyawa gidan ya shigayi wasu dogayen bishiyoyi take ganinta wajen,yacev"husnah saina koya miki hankali sai kinsan baacin amanar aljani sanan wanan abun dake cikin mararki saina rabaki dashi"yana kallonta cike da tsana,
maigadi yace"ina zakije husnah?"fuskar mai gadin ce ta koma mata Abraham fadi takeyi "nidai karabu dani kabarni in fita karka sake maidani duniyar Aljanu kaji ina tsananin sonka bazan iya rayuwa dakai ba jinsin mu daya ba kalli yadda muke cikin daji nida kai ka maidani wajensu momy"sakin baki mai gadi yayi yana kallonta yusrah kuka takeyi ta kasa matsawa wajen husnah wadda ta runtse idi ihu kawai takeyi tana fuzge fuzgen zata gudu....
muneeba kwance tana sauke numfashi zazzabi ya rufeta tsananin kishi da damuwa yasa ciwon gaske ya kamata yaseer cikin sassarfa ya shigo dakin da sallamarsa ummah ya gani zaune tana rike da hannun muneeba sai Anty sadiya data jefesa da wani mugun kallo ya karasa yana fadin "muneeba sannu meyasameki ummah meke faruwa?"hawaye ne kebin fuskar muneeba tana kallonsa cikin tuhuma gashin kansa ta kalla taji gabanta ya fadi ta mike zumbur ta zauna ummah ta rukota ganin yadda tayi "sannu muneeba sannu kinji?"Yaser jiki a sanyaye yake kallonta ta fita hayyacinta yace "shirya mutafi asibiti"ta fashe da kuka hajiya rabi da sadiya suka fice a dakin yana kokarin riketa cikin tausayawa tace "kada katabani nidai karka tabani"ta kwalla kara yaji tsoro kardai itama ta kamu da aljanun.....
a wahalce Abraham ya warware daga daurin da babansa yayi masa tare da taimakon zabariyya wadda ta kasa jure ganinsa a daure tsananin kaunar da take masa.....
*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BAN YAFEBA*
08036953516
07042277401
*SLIMZY*✍🏻
35
Tallabo husnah momy tayi tace "mikomun ruwan gorarcan yusrah"da sauri yusrah ta dauka ta mikawa momy addua ta tofa ciki sanan ta guntsi ruwan a bakinta ta fesa mata a fuska wata wawuyar ajiyar zucuya husnah tayi ta bude idanuwanta tana binsu da kallo take ta tuno da abinda ta ganni ta kalli kujerar bataga kowa ba ta yunkura jikinta ciwo yakeyi mata momy ta d'agota zafi taji ya ziyarceta a kasanta momy ta tsura mata ido tana karantarta tace "husnah meyake damunki?kafarkice takeyi miki ciwo?"husnah ta girgiza kai take ta tuno da yaseer yadda ya cakud'ata daren jiya ruwa ne ya kawo a idanuwanta Momy ta taimaka mata ta zaunar da ita a kujera tace "fadamun meyake damunki?wanan aljanin yazo ne?"sunkuyar da kai husnah tayi hawaye na zubo mata hankalin hajiya saude yayi mugun tashi tace "kifadamun yaseer yayi miki wani abu ne?"gyada mata kai tayi momy ta soma tafa hannu ta kalli yan matanta biyu tace "kubani waje"suka bar wajen tace "yaseer ya taba jikinki ko?"ta jinjinawa momy kai ta fashe da kuka tace "nafada masa banaso kada yayimun shine yayi fushi ni kuma banason yayi fushi kinga yayi hatsari saboda ni"mommy ta jinjina kai tace "tabdijan lallai yaseer zanci ubansa a gidan nan wato ko kunyata baiji ba ya kusanceki? innahlillahi wa innah ilaihi rajiun"husnah ta share hawayenta ta sunkuyar da kai momy ta matsa mata da plate din soyayyen dankali da kwai ta had'a mata tea mai zafi cike da tausayawa "ci abincinki kinji?kirabu dashi zaizo gidan nan ya sameni"husnah cakula abincin takeyi gaba daya hankalinta baya wajen ta juyo ta kalli plate din abincin wasu tsutsotsi ta gani cikin plate din manya manya suna yawo ta kalli cup din wani irin ruwa bakinkirin ne ciki ta kalli momy,"ci abincin mana husnah"girgiza kai husnah tayi tace "momy tsutsotsi ne gasu nan cikin kwanon bazan iyaci ba"momy ta kalli dankalin ta kalli kofin ruwan tea din"girgiza kai tayi ta mike tabar wajen inuwar mutum kawai ta gani a gabanta tana d'ago kai sukai ido hudu da Abraham zabura tayi ta mike wani irin kallo yakeyi mata wasu jijiyoyi ne koraye suka fito cikin idonsa wajen bakin idanuwansa ya koma mai ruwan toka farin kuma ya koma ja ta matukar tsorata momy ce ta dawo da karatun kurani yayiwa momy wani kallo ya bace,
a furgice Momy taga husnah tace "yadai husnah?"ta girgiza kai tace "momy banajin yunwa Bari inje wajensu yusrah kitchen na tayasu aiki"momy ta jinjina kai a hankali take taka kafarta ta girgiza kai kawai ta shiga laluben layin yaseer bata samesa ba dole zataje gidan su yau din nan....
*****
rungume muneeba yayi cikin sigar lallashi yace"kiyi shiru kiyi Hakuri nima bansan cewar hakan zai faru zam kwana can ba banje da niyyar kwana ba ankira malam ne mai bada magani shine na tsaya in shafawa husnah magani tunda ni mijinta ne"tana kokarin kurban ruwan tea batasam lokacin data furzar ba ta shiga tari sakamakon sarketa da yayi idanuwanta suka firfito ya rukota"lafiya?menene muneeba?"yake tambayarta cikin kulawa tace "yaseer ni yanzun kake fadawa cewa ka shafawa husnah magani?"wani kishi ne ya rufe mata idanuwa tace"kaje kaci amanata kenan?me kukayi daga shafa maganin?"cikin daga murya take masa magana abinda yaseer ya tsana kenan a rayuwarsa ya harzuka cikin bacin rai yace "kwanciya nayi da ita ko itadin ba matata bace?ko karuwa ce ita?"bude baki tayi tana kallonsa ta dafe kirjinta hawaye ya soma zuba a idanuwanta tace "yaseer ni kake fadawa ka kwanta da husnah?"
"na kwanta da ita me zakiyi?"yace yana kokarin mikewa ta rushe da kuka har ya kai kofa ya tsaya tausayinta yad'an kamasa dikda haushinta da yakeji ta yaya zata rinka challenging dinsa?yasan tana bashi tausayi saboda cikinsa da take dauke dashi ganin ya tsaya kawai ta soma wani irin tari tasa hannunta a wuyanta da sauri ya dawo cikin dakin "kingani ko?kinga abinda nake fada miki muneeba meyasa kikeso ki kashe kanki ne akan abinda Allah ya halarta?husnah fa matatacw kuma kece kika matsamun da bimcike yasa nafada miki abinda nafada miki har ya bata miki rai"ta sunkuyo kawai ta soma kwara amai a wajen ya dafe kansa daya dau zafi,ya furgar da iska mai zafi daga bakinsa ya dafe kansa ya runtse idonsa husnah ya tuno yadda ta mike tana d'ingisa kafa ko wani hali take ciki oho,tambayar da yayiwa kansa kenan sam bayason nisa da ita matsowa yayi ya zubawa muneeba ido yadda take kwara amai tana gamawa ta durkushe ta soma myrkususun ciwon ciki hankalin yaseer yayi mugun tashi nan ya tube rigarsa kasantuwar weekend ne ba aiki ya soma gyara wajen sanan ya dawo ya ciccibeta ya nufi toilet da ita da kansa ya tube mata kayan jikinta ta faki idonsa tayi murmushi dikda tsananin kishin dake cin ta tayi hakan ne dan ta d'aga masa hankali tsuru yayi da ido yana kallonta fuskarta ce take masa gizo tana komawa husnah yasan ba husnah bace tsabar tunanin husnah da yakeyi ne ya janyo hakan ko taci abinci ma bai saniba yayi mata wanka ya fito da ita ya nad'eta a towel sanan yana kokarin fita cikin murya mai tsananin Jin jiki tace "sweetheart karka tafi kabarni nasan nibaka sona dama husnah kakeso"cak ya tsaya badan ransa yaso ba ya dawo cikin dakin ya zauna gefen gado ya cije lebe yana kallon kiran momy ya kasa dauka tsoron me zata fada masa yakeyi haka kawai yake jin kansa cikin fad'uwar gaba....
******
daga kitchen ta fito tana jin fitsari nusrah tace "Anty husnah ina zakijene naga har yanzun kina dingisa kafa"murmushi tayi "fitsari nakeji nusrah yanzun zan dawo ai naji sauki"ta fito daga kitchen din yusrah na ganin ta fita ta matso kusa da yar uwarta tace "nifa a tsorace nake da Antu husnah gani nakeyi kamar ba ita bace kinsan aljanun nan"nusrah tayi ajiyar zuciya tace "haka ne amma fa yau kam tabbas itace saidai alamunta sum nuna tana cikin damuwa"suka girgiza kai dukkansu suka cigaba da aikinsu,
tana shiga dakin kofa ta rufe cikin sauri take kokarin shiga toilet din taga mutum kwance kan gadonta ta murza idonta "wanene waye wanan kwance akan gado na"a sanyaye tayi maganar d'agowa yayi daga kwanciyar da yayi kafin kiftawar ido har ta gansa a gabansa cikin fargaba da faduwar gaba take kallonsa ta tsaresa da Ido shima ita yake kallo saidai baizo mata a kamar ban tsoroba a kammanninsa ta gansa fad'awa jikinsa tayi ya tureta gefe tsananin tausayinsa yasa batasan lokacin data fada jikinsa ba kallomsa takeyi cikin tsananin mamaki ya girgiza kai ya cije baki fuskarsa tayi bakin kirin yace"Babu sauran soyayyarki a cikin zuciyata husnah"dam gabanta ya fadi tayi masa wani kallo ta kauda kanta gefe bugun zucuyarta ya tsananta yace"kinci amanata husnah dama ku bil'adama haka kuke amma zan koya miki hankali zakisan kin cutar dani husnah inaji ina gani jiya kika mikawa d'an uwanki bil'adama jikinki ya kwanta dake lokacin da kike tsananin kaunata kin mance yadda naso in kusanceki kika hanani?"hawaye ke zubowa a idanuwansa yana kallonta jikinta a sanyaye momy ta turo kofar ta shigo ganinta tsaye cak yasa tace"lafiya?"girgiza kai tayi bata gansa ba yana cikin dakin kuma cikin jin haushinta yake kawai ya shige jikinta, momy tace "husnah zan fita zani gidansu innah daga nan zan wuce gidanku can akwai maganar da zamuyi"jinjinawa momy kai kawai akayi ta fice dikda jikinta bai bataba tasan wanan ba husnah bace saidai ta kasa gasgata hakan tana fita ya fita daga jikin husnah dakin ne ya shiga jujjuya mata cikin minti biyar kawai taga ko ina ya zama kogi ruwa nayo kanta ta fito aguje nusrah tana kokarin riketa ta bankadeta ta fadi kasa waje tayi tana gudu kamar zararriya nusrat ta window ta leka tana kwalawa mai gadi kira "karka bar Anty husnah ta fito"
Abraham harde hannuwansa yayi a kirjinsa daga gefe yana kallon yadda ta fita a hayyacinta tsananin tsoro da furgici ta kalli gidan sauyawa gidan ya shigayi wasu dogayen bishiyoyi take ganinta wajen,yacev"husnah saina koya miki hankali sai kinsan baacin amanar aljani sanan wanan abun dake cikin mararki saina rabaki dashi"yana kallonta cike da tsana,
maigadi yace"ina zakije husnah?"fuskar mai gadin ce ta koma mata Abraham fadi takeyi "nidai karabu dani kabarni in fita karka sake maidani duniyar Aljanu kaji ina tsananin sonka bazan iya rayuwa dakai ba jinsin mu daya ba kalli yadda muke cikin daji nida kai ka maidani wajensu momy"sakin baki mai gadi yayi yana kallonta yusrah kuka takeyi ta kasa matsawa wajen husnah wadda ta runtse idi ihu kawai takeyi tana fuzge fuzgen zata gudu....