Sashe 49
Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
40
tun daga kofar gate ta ke jiyo muryar daddy cikin gidan hakan yasa ummah hadiza ta shiryawa dik wani makirci da hajiya rabi zata kulla da sallamarta ta shiga yana tsaye hajiya rabi na rusa kuka tana sharar hawaye cike da kissa wani kallo Alhaji badamasi ya watsawa ummah hadiza yace "dama iskancin daya kawoki gidana Kenan?abinda kuke kullawa dik be ishekuba har sai kun hada ma hajiya rabi da duka?"kallon hajiya rabi ummah hadiza tayi tace "amma yaya ta..."tsawa daddy ya daka mata tayi shiru yace "tou Bari kiji dik abinda kukeyi kuna ganin bansaniba ko nasani tsaf kuma wanan da kuke ganin na aura babu Wanda ya isa ya rabani da ita dan haka a matsayinta na matar yayanki ki tsugunna har kas ki bata hakuri"cikin tsawa daddy yake bawa ummah hadiza umarni ta girgiza kai tace "ke rabi wallahi baki isa na tsugunna na baki hakuri ba kinyi kadan koda kike matar yayana ai na girmeki ko ban girmeki ba bokanki beyi nasara akainaba"ta watsa mata harara daddy ya daga hannu ya zabgawa ummah hadiza mari "a gaban nawa ma kin sake maimaitawa?ya tabbata sharrin da kuka kulla mata gaskiya ne Kenan hardake idan zainab tayi ai ita kishiyarta ce kedin kishiyarta ce?"ummah hadiza ta dafe kumatunta tana kallon hajiya rabi idanuwa jajir cike da takaici take kallonta "kuma ki ficemun daga gida inhar bazaki daraja matata ba karki sake zuwa inda nake kinji nafada miki"hajiya zainab hawaye ne ya wanke mata fuska kallon yadda daddy yake ciwa ummah hadiza mutunci sabida hajiya rabi yasa kai yabarsu tsaye cike da haushi,.....ummah hadiza ta girgiza kai tana kallon hajiya rabi cikin takaici da tsana tace "yau kinsa d'an uwana ya mareni ko?"hajiya rabi tayi juyi tace "kwarai dagaske kuwa ninafi karfin in mareko da hannuna saidai insaka wanki ya mareki kuma burina ya cika babban burina ma ya sake cika tunda ya haramta miki zuwa gidan"wata yar kwalla ce ta cicciko a idon ummah hadiza,momy ta rukota "kiyi hakuri hadiza ninaja miki dik abinda dan uwanki yayi miki sanadina ne kika mareta amma ki kwantar da hankalinki Allah Baya bacci"ummah hadiza ta jinjina kai tace "karki damu zainab ta tsokalowa kanta tsuliyar dodo ne sai tayi danasanin saka d'an uwana ya mareni a kumatuna yadda ya mareni a kumatuna nayi miki alkawarin sai ya mareki nan bada jimawa ba dan nida kike ganina bakisan ko waceceni ba ko?fada da aljani babu dadi anzo inda nakeso amma sai na tabbatar da na rama abinda kikaimun sai nayi sanadin da kikabar gidan nan tare da tonuwar asirinki sai alhaji badamasi ya dakeki a tsakiyar titi a gaban kowa"hajiya rabi kallon ummah hadiza takeyi shekeke kamar zautacciya rike da kumatunta tayi wata dariya,
"wanan dariyar sai ta zame miki kuka yan uwanki da kika kora kika gujesu saboda talakawa ne su zaki koma wajensu ki kwashi kashinki a hannu"hajiya rabi cikin zuciyarta wani tsoro ne ya kamata kallon yadda idanuwan ummah hadiza sukai jajir tayi ta kasa magana,muneeba ce ta fito daga sashenta taci kwalliya ta saka doguwar rigar abaya baka cikinta ya fito sosai yayi girma tana rike da kwankwaso daya hannunta rike da wayarta tana dannawa tana ganinsu ta sake canja tafiya tana yauki cike da yanga da kwarkwasa ta karaso wajen ta kalli ummah hadiza ta watsar sanan ta dubi hajiya rabi tace "meke faruwa a nan?kukai cirko curko kamar anyi mutuwa ummah?ko ana jimamin cusawa yaya yaseer matar aljan ne?"ta danyi dariya hajiya rabi ta sheke da dariya ummah hadiza tayi kwafa ta galla mata harara tace "ke kumafa?hardasu kaza acin danko an fada miki inba rashin husnah ba ke ance miki ko kallo kin ishi yaseer ne?me zaiyi dake?ina zai kaiki bayan ga wadda zuciyarsa ke mararinso da muradi?"muneeba ranta ya baci ta tabe baki zatayi magana hajiya rabi ta dakatar da ita tace "aiko soyayya ta kare akan muneeba tinda ga dansa nan a cikin muneeba yana girma idan baya sonta bazai bude kafarta ya shigeta ba"muneeba ta shafa cikinta tana sake turoshi ummah hadiza a kufule tace "wanan cikin da kuke takama dashi insha Allah sai kunyi kuka da hawayenku sai ta haifo dan aljani idan har husnah matar aljan ce ke kuma uwar aljani zaki zama"
"aniyarki ta biki"ummahn muneeba tana ruko muneeba dake shirin watso rashin kunya nan suka soma hayaniya daddy ya fito yana ganin ummah hadiza ya zaburo"wai ba nace idan masifa ce zata kawoki gidana ki ficemun ba karki sake zuwa mai kike jira"ummah hadiza tace "ki jira ramuwar gayya kijira ranan da zaa koreki da kanyanki akai"momy ta ruko ummah hadiza cikin damuwa tace "kije wajen aikin nan da akasaki karki damu zan shigo nima idan nayi sallah"ta rukota tana kokarin fita da ita daddy ya daga murya "kema kidawo ki dibi kayanki ki bita ku zama kashin awaki"ummah hadiza ta fice momy ta shigo dakyar take taka kafarta tsabar bacin Rai hajiya rabi tace "anji kunya dai ana korar mutum yana likewa"kallonta momy kawai tayi ta dauke kai hajiya rabi ta ruko hannun muneeba sukai sashenta...
******
sautin bude kofar shiga parlor hajiya saude taji ta dauko kofin data hado tea ta fito da sauri turus ta ga yaseer tsaye taba binsa da kallo ta saki cup din hannunta cike da tashin hankaki bakinta na rawa tace "yaseer?inasu husnah?lafiya hatsari kukayi da kuka fita?"yaseer cikin rashin fahimta yake kallon momynsa hawayene suka soma zubowa daga idanuwansa ta d'ora hannu akai ta fashe da kuka "yaseer kayimun magana ina kannenka daka fita dasu da husnah da kukaje siyayya dazun?ina suke kunyi hatsari ko?aljanin ya sake saka hatsari kenan nafadawa husnah dama kaine ba Abraham ba sai tacemun wai bakai bane aljani ne"durkushewa Yasser yayi yana kukan bakin ciki wato mahaifiyarsa da matarsa da kannensa da aljani suke rayuwa basu saniba?kuka yakeyi ya kalli kayan jikinsa yadda suka fita hayyacinsu dakyar ya motsa bakinsa dake karkarwa kamar ana watsa masa ruwa yace "momy nine yaseeer wanda ya fita dasu husnah banibane aljani ne"dafe kirji momy tayi cikin tsananin tsoro tad'anja da baya tana kallonsa cike da tuhuma da furgici 'Aljani fa kace ban yarda dakai ba kaiba yaseer bane kazo ne kawai ka zautar dani kaine aljani"momy ta juya zata gudu yaseer ya rukota ta runtse idanuwanta gamm jikinta sai rawa yakeyi tana karanto adduoi yaseer ya tsareta da ido yadda take gumi ya tabbatar masa a furgice take sai adduoi momy ke zubowa ta saki wanan ta kama wanan cikin sanyin murya da dasasshiyar murya yace "ki bude idonki nine d'anki yaseer dik adduoin nan da kikayi nida aljani ne aida kin konani momy danki ne yaseer wanda ya dawo daga duniyar aljanu"ya fashe da kuka ya rike kafafuwanta,a sanyaye momy ta bude idanuwa ta tsura masa ido cikin ido kallonsa takeyi tanajin wani yanayi mai wuyar misaltuwa ta tsugunna ta ruko kafadarsa ta dagosa ta tsayar dashi ta kalli kwayar idonsa take ta tabbatar da d'anta yaseer ne tabbas yaserr din da suke gani a matsayin sa ba haka kwayar idonsa take ba ta fashe da kuka tace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun wace irin masifa muke ciki?ace dama da aljani muke cudanya bamu saniba?yanzun gashi ya fita dasu husnah da su yusrah nashiga uku karya gudu dasu duniyar aljanu"hankalin yaserr ya tashi ya zube a kasa yana kuka kamar karamin yaro cikin damuwa momy kasa magana tayi takowa tayi ta karasa parlor ta zauna turus a kujera tana rera kuka.....
rungumo yusrah tayi jikinta ganin bata numfashi jikinta ya kama rawa ya kallesu ta jikin mirror yayi murmushi husnah ta watsa masa harara tace "mugu kawai"ya juyo ya kashe mata ido yace "nine mugu husnah ni mijin naki kike cewa mugu kanki daya kuwa?"nusrah dake gefensa zaune ta juyo ta kalli husnah dake rungume da yusrah ta kara kallonsu cikin mamaki "Anty husnah meyasamu yusrah?"ta jikin madubi ya kallesu husnah ta dago ido tayi tozali da yadda idanuwansa suke ta kalli nusrah ta girgiza Mata kai tace "bacci takeyi"tayi ajiyar zuciya gudu kawai yake shararawa Allah Allah yakeyi ya shiga ya saukesu sakamakon yasan akwai matsala ganin zuhraliyya na bin su suna tsayawa a kofar gidan husnah ta rasa ya zatayi cikin ikon Allah tana motsa yusrah ta zabura ta rubtse ido ta kwalla kara jikinta na rawa"Anty husnah a ina mukene?yana tare damu?"ta radawa yusrah a kunne"shhhhh ki daure kinji babu abinda zaiyi miki aibake yakeso ba bake ya biyo ba banaso ya Gane kinga halittarsa"gumi ke karyowa yusrah ta kasa Bude idonta a haka ta fito yace "yadai lafiya yusrah?"ta girgiza masa kai "zazzabi nakeji"
"zazzabi kuma?munfita lafiya kice kinajin zazzabi karmu shiga kisa momy taji haushina"ta kada kai kawai kirjinta bugawa kawai yakeyi,
ta jikin mirror momy ta hangoso suna kwaso kaya wani kulllll taji cikinta yayi mata ta kalli yaseer dake zaune zugum zatayi magana suka shigo a tare wani shock yan biyu sukayi suna kallon yaseer suna kallon Abraham babancinsu kayan jikinsu Abraham ya hadiyi wani miyau ya waske yace"momy wanan fa?karfa ki yarda aljani yazo ya yaudareki"jikin momy ya kama rawa ta kasa magana yusrah kuwa take kamanninsa ya dawo mata ta yanke jiki ta fadi yaseer ya zabura ya karasa yana girgiza ta Abraham yayi murnushi yana kallonsu momy yace "babu yadda zaayi d'an Adam ya kalli aljani ko yaya ne ya zauna lafiya inda a halittata gaba daya ta kalleni da na tabbatar saidai mudawo da gawarta,tare nake rayuwa daku bakusan wayeni ba toni aljani ne"zabura momy tayi ta ruga aguje tayi daki nusrah ta rufa mata baya suka rufe dakin gamm sai rawar jiki sukeyi,
mikewa yaseer yayi suna kallon kallo da Abraham murmushi yaseer yayi masa yace "muguntarka tana gab da zuwa karshe nayi maka alkawarin ni zan kasheka da hannuna"
tun daga kofar gate ta ke jiyo muryar daddy cikin gidan hakan yasa ummah hadiza ta shiryawa dik wani makirci da hajiya rabi zata kulla da sallamarta ta shiga yana tsaye hajiya rabi na rusa kuka tana sharar hawaye cike da kissa wani kallo Alhaji badamasi ya watsawa ummah hadiza yace "dama iskancin daya kawoki gidana Kenan?abinda kuke kullawa dik be ishekuba har sai kun hada ma hajiya rabi da duka?"kallon hajiya rabi ummah hadiza tayi tace "amma yaya ta..."tsawa daddy ya daka mata tayi shiru yace "tou Bari kiji dik abinda kukeyi kuna ganin bansaniba ko nasani tsaf kuma wanan da kuke ganin na aura babu Wanda ya isa ya rabani da ita dan haka a matsayinta na matar yayanki ki tsugunna har kas ki bata hakuri"cikin tsawa daddy yake bawa ummah hadiza umarni ta girgiza kai tace "ke rabi wallahi baki isa na tsugunna na baki hakuri ba kinyi kadan koda kike matar yayana ai na girmeki ko ban girmeki ba bokanki beyi nasara akainaba"ta watsa mata harara daddy ya daga hannu ya zabgawa ummah hadiza mari "a gaban nawa ma kin sake maimaitawa?ya tabbata sharrin da kuka kulla mata gaskiya ne Kenan hardake idan zainab tayi ai ita kishiyarta ce kedin kishiyarta ce?"ummah hadiza ta dafe kumatunta tana kallon hajiya rabi idanuwa jajir cike da takaici take kallonta "kuma ki ficemun daga gida inhar bazaki daraja matata ba karki sake zuwa inda nake kinji nafada miki"hajiya zainab hawaye ne ya wanke mata fuska kallon yadda daddy yake ciwa ummah hadiza mutunci sabida hajiya rabi yasa kai yabarsu tsaye cike da haushi,.....ummah hadiza ta girgiza kai tana kallon hajiya rabi cikin takaici da tsana tace "yau kinsa d'an uwana ya mareni ko?"hajiya rabi tayi juyi tace "kwarai dagaske kuwa ninafi karfin in mareko da hannuna saidai insaka wanki ya mareki kuma burina ya cika babban burina ma ya sake cika tunda ya haramta miki zuwa gidan"wata yar kwalla ce ta cicciko a idon ummah hadiza,momy ta rukota "kiyi hakuri hadiza ninaja miki dik abinda dan uwanki yayi miki sanadina ne kika mareta amma ki kwantar da hankalinki Allah Baya bacci"ummah hadiza ta jinjina kai tace "karki damu zainab ta tsokalowa kanta tsuliyar dodo ne sai tayi danasanin saka d'an uwana ya mareni a kumatuna yadda ya mareni a kumatuna nayi miki alkawarin sai ya mareki nan bada jimawa ba dan nida kike ganina bakisan ko waceceni ba ko?fada da aljani babu dadi anzo inda nakeso amma sai na tabbatar da na rama abinda kikaimun sai nayi sanadin da kikabar gidan nan tare da tonuwar asirinki sai alhaji badamasi ya dakeki a tsakiyar titi a gaban kowa"hajiya rabi kallon ummah hadiza takeyi shekeke kamar zautacciya rike da kumatunta tayi wata dariya,
"wanan dariyar sai ta zame miki kuka yan uwanki da kika kora kika gujesu saboda talakawa ne su zaki koma wajensu ki kwashi kashinki a hannu"hajiya rabi cikin zuciyarta wani tsoro ne ya kamata kallon yadda idanuwan ummah hadiza sukai jajir tayi ta kasa magana,muneeba ce ta fito daga sashenta taci kwalliya ta saka doguwar rigar abaya baka cikinta ya fito sosai yayi girma tana rike da kwankwaso daya hannunta rike da wayarta tana dannawa tana ganinsu ta sake canja tafiya tana yauki cike da yanga da kwarkwasa ta karaso wajen ta kalli ummah hadiza ta watsar sanan ta dubi hajiya rabi tace "meke faruwa a nan?kukai cirko curko kamar anyi mutuwa ummah?ko ana jimamin cusawa yaya yaseer matar aljan ne?"ta danyi dariya hajiya rabi ta sheke da dariya ummah hadiza tayi kwafa ta galla mata harara tace "ke kumafa?hardasu kaza acin danko an fada miki inba rashin husnah ba ke ance miki ko kallo kin ishi yaseer ne?me zaiyi dake?ina zai kaiki bayan ga wadda zuciyarsa ke mararinso da muradi?"muneeba ranta ya baci ta tabe baki zatayi magana hajiya rabi ta dakatar da ita tace "aiko soyayya ta kare akan muneeba tinda ga dansa nan a cikin muneeba yana girma idan baya sonta bazai bude kafarta ya shigeta ba"muneeba ta shafa cikinta tana sake turoshi ummah hadiza a kufule tace "wanan cikin da kuke takama dashi insha Allah sai kunyi kuka da hawayenku sai ta haifo dan aljani idan har husnah matar aljan ce ke kuma uwar aljani zaki zama"
"aniyarki ta biki"ummahn muneeba tana ruko muneeba dake shirin watso rashin kunya nan suka soma hayaniya daddy ya fito yana ganin ummah hadiza ya zaburo"wai ba nace idan masifa ce zata kawoki gidana ki ficemun ba karki sake zuwa mai kike jira"ummah hadiza tace "ki jira ramuwar gayya kijira ranan da zaa koreki da kanyanki akai"momy ta ruko ummah hadiza cikin damuwa tace "kije wajen aikin nan da akasaki karki damu zan shigo nima idan nayi sallah"ta rukota tana kokarin fita da ita daddy ya daga murya "kema kidawo ki dibi kayanki ki bita ku zama kashin awaki"ummah hadiza ta fice momy ta shigo dakyar take taka kafarta tsabar bacin Rai hajiya rabi tace "anji kunya dai ana korar mutum yana likewa"kallonta momy kawai tayi ta dauke kai hajiya rabi ta ruko hannun muneeba sukai sashenta...
******
sautin bude kofar shiga parlor hajiya saude taji ta dauko kofin data hado tea ta fito da sauri turus ta ga yaseer tsaye taba binsa da kallo ta saki cup din hannunta cike da tashin hankaki bakinta na rawa tace "yaseer?inasu husnah?lafiya hatsari kukayi da kuka fita?"yaseer cikin rashin fahimta yake kallon momynsa hawayene suka soma zubowa daga idanuwansa ta d'ora hannu akai ta fashe da kuka "yaseer kayimun magana ina kannenka daka fita dasu da husnah da kukaje siyayya dazun?ina suke kunyi hatsari ko?aljanin ya sake saka hatsari kenan nafadawa husnah dama kaine ba Abraham ba sai tacemun wai bakai bane aljani ne"durkushewa Yasser yayi yana kukan bakin ciki wato mahaifiyarsa da matarsa da kannensa da aljani suke rayuwa basu saniba?kuka yakeyi ya kalli kayan jikinsa yadda suka fita hayyacinsu dakyar ya motsa bakinsa dake karkarwa kamar ana watsa masa ruwa yace "momy nine yaseeer wanda ya fita dasu husnah banibane aljani ne"dafe kirji momy tayi cikin tsananin tsoro tad'anja da baya tana kallonsa cike da tuhuma da furgici 'Aljani fa kace ban yarda dakai ba kaiba yaseer bane kazo ne kawai ka zautar dani kaine aljani"momy ta juya zata gudu yaseer ya rukota ta runtse idanuwanta gamm jikinta sai rawa yakeyi tana karanto adduoi yaseer ya tsareta da ido yadda take gumi ya tabbatar masa a furgice take sai adduoi momy ke zubowa ta saki wanan ta kama wanan cikin sanyin murya da dasasshiyar murya yace "ki bude idonki nine d'anki yaseer dik adduoin nan da kikayi nida aljani ne aida kin konani momy danki ne yaseer wanda ya dawo daga duniyar aljanu"ya fashe da kuka ya rike kafafuwanta,a sanyaye momy ta bude idanuwa ta tsura masa ido cikin ido kallonsa takeyi tanajin wani yanayi mai wuyar misaltuwa ta tsugunna ta ruko kafadarsa ta dagosa ta tsayar dashi ta kalli kwayar idonsa take ta tabbatar da d'anta yaseer ne tabbas yaserr din da suke gani a matsayin sa ba haka kwayar idonsa take ba ta fashe da kuka tace "innahlillahi wa innah ilaihi rajiun wace irin masifa muke ciki?ace dama da aljani muke cudanya bamu saniba?yanzun gashi ya fita dasu husnah da su yusrah nashiga uku karya gudu dasu duniyar aljanu"hankalin yaserr ya tashi ya zube a kasa yana kuka kamar karamin yaro cikin damuwa momy kasa magana tayi takowa tayi ta karasa parlor ta zauna turus a kujera tana rera kuka.....
rungumo yusrah tayi jikinta ganin bata numfashi jikinta ya kama rawa ya kallesu ta jikin mirror yayi murmushi husnah ta watsa masa harara tace "mugu kawai"ya juyo ya kashe mata ido yace "nine mugu husnah ni mijin naki kike cewa mugu kanki daya kuwa?"nusrah dake gefensa zaune ta juyo ta kalli husnah dake rungume da yusrah ta kara kallonsu cikin mamaki "Anty husnah meyasamu yusrah?"ta jikin madubi ya kallesu husnah ta dago ido tayi tozali da yadda idanuwansa suke ta kalli nusrah ta girgiza Mata kai tace "bacci takeyi"tayi ajiyar zuciya gudu kawai yake shararawa Allah Allah yakeyi ya shiga ya saukesu sakamakon yasan akwai matsala ganin zuhraliyya na bin su suna tsayawa a kofar gidan husnah ta rasa ya zatayi cikin ikon Allah tana motsa yusrah ta zabura ta rubtse ido ta kwalla kara jikinta na rawa"Anty husnah a ina mukene?yana tare damu?"ta radawa yusrah a kunne"shhhhh ki daure kinji babu abinda zaiyi miki aibake yakeso ba bake ya biyo ba banaso ya Gane kinga halittarsa"gumi ke karyowa yusrah ta kasa Bude idonta a haka ta fito yace "yadai lafiya yusrah?"ta girgiza masa kai "zazzabi nakeji"
"zazzabi kuma?munfita lafiya kice kinajin zazzabi karmu shiga kisa momy taji haushina"ta kada kai kawai kirjinta bugawa kawai yakeyi,
ta jikin mirror momy ta hangoso suna kwaso kaya wani kulllll taji cikinta yayi mata ta kalli yaseer dake zaune zugum zatayi magana suka shigo a tare wani shock yan biyu sukayi suna kallon yaseer suna kallon Abraham babancinsu kayan jikinsu Abraham ya hadiyi wani miyau ya waske yace"momy wanan fa?karfa ki yarda aljani yazo ya yaudareki"jikin momy ya kama rawa ta kasa magana yusrah kuwa take kamanninsa ya dawo mata ta yanke jiki ta fadi yaseer ya zabura ya karasa yana girgiza ta Abraham yayi murnushi yana kallonsu momy yace "babu yadda zaayi d'an Adam ya kalli aljani ko yaya ne ya zauna lafiya inda a halittata gaba daya ta kalleni da na tabbatar saidai mudawo da gawarta,tare nake rayuwa daku bakusan wayeni ba toni aljani ne"zabura momy tayi ta ruga aguje tayi daki nusrah ta rufa mata baya suka rufe dakin gamm sai rawar jiki sukeyi,
mikewa yaseer yayi suna kallon kallo da Abraham murmushi yaseer yayi masa yace "muguntarka tana gab da zuwa karshe nayi maka alkawarin ni zan kasheka da hannuna"