← Book details Addininmu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 67

Sashe 42

Addininmu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana zaune a kan gadon ta suna chatintg da Nana yayin da Nana ta sanar mata da cewar mamarta ce ta ce wai idan suka yiwa Abdalha haka to ko anyi auran zai dinga ganinta da mutunci shi fa yasa muka masa wannan cin mutuncin. Ita dai Maryam bata ce komai ba alokacin, sai daga baya Nana ta sake kiran Maryam wai har yanzu Abdalha bai dawo bafa? Ita kuwa Maryam ta dinga mata dariyar, to shine fa yanzu take sanar mata da cewar ai Abdalha ya dawo da Zainab yanzu hk ma tana gidan uban ta, hakanne yasa Nana rikicewa sosai domin tana son Abdalha sosai.

Suna cikin hira da Nana taji ana buga mata ƙofar ɗaki. A ɗan tsorace ta ce "Waye? Shiru babu amsa sai ta sake cewa "Wai waye ne cikin darannan ke haka ta nufi ƙofar tana surfa masifa Walhi Nusaiba kin cika taƙurawa mutum ke babu dama a ɗauki aron abun ki sai kin hana mutum sakew"...Ai bata ƙarasa ba sukayi ido biyu da Abdalha dake tsaye yana sakar mata harara. Cikin tsoro ta ƙara sa buɗe masa ɗakin tana sun kuyar da kai. Ɗakin ya shiga ya zauna a bakin gadon yana bin ɗakin da kallo cikin nuna ƙyama,. A hankali ta kalleshi ganin yanda yake ya tsine fuska yasa ta saki tsaki wanda yasa Abdalha ɗin jin ta. Suna haɗa ido ta rufe baki tana girgiza kai. "Ina wayarki? Ya jefo mata tambayar da sauri ta ƙaraso gurin da yake ta miƙa masa. Ya ƙarɓa ya shiga gurin numbobi ya dawo gurin hotuna. Ganin ya rasa yanda zaiyine kuma baisan mai zaicemata ba ya miƙa mata wayar, kafin ta ƙarɓa kiran Nana ya shigo. Yana son ya tambayeta numbar Zainab ne amma ya kasa.

"Wacece mai kiranki cikin dare?

"Ƙawata ce" Bai ƙara cewa komaiba ya kama hanya zai fita Maryam ta ce "Yaya wani abun kake sone? Bai ce komai ba ya bar gidan gaba ɗaya izuwa nasa gidan duk ransa a ɓace.

Washe gari cikin garin Kano da ma kewayanta gaba ɗaya suka tashi da labarin dawowar Zainab Ambato. Hausawa suka ce wai gani da ido shine sheda. Ai kuwa dai sai ga Zainab da kanta tana bada labarin komai da ya faru cewar ba Abdalha bane ya saceta shine ma ya cetota daga gurin su. Cikin ƙanƙanin lokaci saƙon yazo ko ina, ƴan jarida da gidajen rediyo dana tv duk sun saka hirar, kasan cewar ƴan jarida ne da kansu sukayi hira da ita. Tofa ana wata sai ga wata. Bayan samun wannan labinrin ne kuma Mlm Adamu ya ce shifa sai an masa iyaka da shek Kabir kabuga, saida ɗan sa Isa ya tsaya sosai kafin abun ya lafa. Ƴan gari kuwa kowa yana jajanta abun, to meyasa Abdalha zai ceceta kodai yana sonta ne. Aliyu kuwa tuni ya nemi da iyayensa akan a saka ranar bikinsa da Zainab domin jikinsa nabashi cewar zai iya rasata. Ai kuwa babu wata-wata a ka saka rana wata uku masu zuwa. Labarin bikin ya bazu ko ina.

Lokacin da Nana da mamarta sukaga wannan labarin na dawowar Zainab sunyi ta kaici sosai, domin kuwa sunsan yanzu Abdalha ya musu nisa.

Abdullah kuwa Daddy ya haƙura da duk abunda ya faru, amma har yanzu babu shi babu Mlm Adamu. Sannan ya sake umartar Abdalha ya koma gurin Nana amma ya ce ina shi dai yanada wacce ya keso, idan aka ce wacece sai ya ce ai basu gama dai-daitawa, yayinda shima isa ya tsunduma soyayar Maryam sosai da sosai, hakanne yasa ya sanarwa da Zainab, ita kuma da yake yanzu suna waya domin tinda ta dawo ta kira ta kuma kusan kullum sai sunyi waya, ta bashi numbar Maryam kuma cikin ikon Allah itama ta ƙware masa, amma soyayar ta kasa baiyana. Soyaya ya ce mai ƙarfi ta ƙullu tsakanin Maryam da Isa wanda ta wuce katance. Nusaiba da Sadiya kuma dukkansu kowacce ta fitar da zaɓinta har an saka rana nan da wata biyu masu zuwa. Zainab kuwa daga dawowarta ta sake yin wata ƙasidar mai zafi wanda yasa kowa hawaye saboda tayi ƙasidar ne akan tarihin Manzan Allah Sallallahu alaihi Wasallama, tayi bayanin yanda yake zamantakewar sa da al'umma. Tabbas ƙasidar ta karɓo a gurin bayin Allah.

Amma ai masu iya magana sunce ranar wanka ba'a ɓoyan cibi. Isa da kansa ya tun kari Abdalha da zancen soyayar sa da Maryam, ai kuwa Abdalha yaji daɗi domin wannan hanyar itace mafi dacewa da zasubi su gano ko dai wani abun ya taɓa faru ne a baya. Abdalha nason ya masa maganar Zainab amma yasan babu kyu nema a cikin nema, domin kuwa an saka ranar Zainab,. Amma haka ya daure ya sanar masa da cewar yana son Zainab. Cikin mamaki Isa ya ke kallon Abdalha domin bai taɓa kawo haka a ransa ba. Abdalha ya sanar masa da irin sonsa yake mata tun ba yanzu ba, Isa ya gamsu amma ya ce kasan dai auranta yanzu bai huce wata biyu ba. Haka dai suka sanarwa da Mama ita kuma ta ce ya fara tuntubɓar Zainab domin kuwa itace ta kawo Aliyu kuma Aliyu ɗan gidane, ga kuma an kusa, ita dai batasan abun yi ba.

Bai samu Zainab sunyi mgn ba ya tunkari mahaifinsa da maganar? Zaune suke a palon harda su Maryam da Nura wanda ke karatu a gaban Nusaiba ya na bada hadda. "To muna sauraronka wacece kuma ƴar gidan waye a ƙasar nan tamu? Shek Kabir kabuga ya faɗa yana washe baki domin jin ƴar gidan wani shahararren malamin a cikin malaman sunnha ya samo. Itama Momy murmushi ta keyi tana jiran jin sunan surukar tasu. Ita kuwa Maryam da tasan kwanan zancen domin kuwa Isa ya sanar mata da komai, sai rintse ido takeyi kamar itace zata sanar musu ɗin.

Abdalha ya ce "Am am damafa fa kowa bace sai sai sai amma Zainab Ambato ce ƴar ƴar gidan mlm Adamu. Ya faɗa yana shafa ƙyeyarsa Tsint palon yayi harda Nura dake karatu domin sunji sunan wacce ya kira, ita kanta Momy saida ta tsorata, Sadiya kuwa ido ta ƙwalalo waje, Maryam kuwa rintse idon ta sakeyi tana karanto addu'o'in da suka samu damar isowa gareta. Shi kuwa Abdalha ɗagowa ya yi domin ganin fuskar Daddy...📝

*Please comment É—inku shine zaisa mugama da wuri*

*S REZA ✍️*
[10/21 22:06] Aliyu Makko: *ADDININMU*

*S REZA... ✍️*

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

*PAGE3️⃣3️⃣*

..... Daddy ya haɗe fuska babu a lamar wasa ko sakin fuska tsanar ɓacin rai ne kawai ke yawo a kan fuskarsa, tashi yayi ya bar palon ba tare da ya tanka wa kowa ba. Daddy na fita Momy ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Abdalha wanda idonsa duk sun cika da ruwan hawaye ganin yanda Daddy ya ƙi tamka masa. "Abdalha me kake nufi da wannan batun na ka? Kanada hankali kuwa? Kana ganin yanda tsakanin ku da ita babu jituwa amma zaka bijiro da wannan zancen har kana iya kallon ƙwayar idon Daddy ka ce wai ƴar gidan Malam Adamu kakeso, to ko ni ban aminceba domin wannan abun zai iya haifar da rikici mai tsanani wanda dukkanmu ba zai mana daɗi ba. Cikin karyewar murya ya ce "Sorry Momy amma gaskiyar kenan na faɗa muku, kune kuka tambayeni wacce na ke so kuma ni ita nakeso kuma ita zan auura, sannan kuma yayan ta wato Isa shima sun dai-dai ta Maryam, saboda haka Momy dan Allah ki goyi bayan wannan abun domin mu kawo ƙarshen wannan matsalar. Maryam najin abunda Abdalha ya ce ta miƙe tsaye da gudu ta bar palon, su kuwa sauran kallon ikon Allah sukeyi wai Maryam da Isa, to ya zatayi da wanda ta ce shi takeso. Abdalha na faɗar haka ya tashi ya bar Momy sake da baƙi ta hanci tana kallonsa.

"Abdul" Abdul" Momy ke zabga masa
kira amma ya sakai ya bar gidan cikin jin haushin wannan ƙiyayyar da ke tsakanin iyayen nasu. Motarsa ya shiga da niyar zuwa gidan sa, sai ya tuno da zancen Mama "Su iyaye ba abin wasa bane, Addinimu bai amince da ƴaƴa su dinga tsaurara kalamamsu a kan iyayeba koda kuwa suɗin suna aikata abinda Addini bai yarda da shiba, ba'a kace kamusu biyeyya akan abunba, sannan ba'ace ku tausasa kalamanku agaresuba. Shiru ya yi yana tabbatar da wannan zance sai kawai ya fito daga motar ya koma cikin gidan. A zuciyarsa yana cewa yau wa'azi na zai fara daga gida, kuma in sha Allah sai kowa ya fahimceni.

Momy ku wa mamakin jin abunda Abdalha ya ce ta ke yi, wai Maryam ma sun dai-daita da Isa. Kallon Nura Momy tayi ta ce "Nura kira min Anty Maryam yanzu. Da sauri ya miƙe yana ɗan sakin dariya. Kafin Nura da Maryam su zo Abdalha ya shigo cikin palon kai a sunkuye. Yana zama saiga Maryam ta re da Nura ta sakoshi gaba yana kuka.

Da sauri Nura ya nufi gurin Abdalha ya na share hawaye domin kuwa yasan shikaɗaine zai rama masa. Kafin Abdalha ya ce wani abu Sadiya ta ce "Yanzu-yanzu daga shigar sa ɗakinki har kin sa kashi kuka, kawai dan ya je ya miki wasa, kinji kunya walhi. Cikin rashin kunya ta ce "To ni abokiyar wasar sa ce da zaije har ɗakina yana min dariya, ko ni ɗin mahaukaciyar ce? Maryam ta faɗa tana ji kamar ta ɗauke Sadiya da mari. Momy ta kai kallonta ga Maryam ta ce "Kin kyuta Maryam, kici gaba da cin zalin ƙaninki karki fasa. Momy na faɗa ta dawo da kallonta izuwa ga Abdalha. Maryam da Sadiya kuwa sai hararar juna sukeyi, Sadiya tana jin cewar yau da Abdalha baya gidannan da sai ta saukewa wannan yarinyar abunda ke kanta. Abdalha ya sharewa Nura hawaye yana kallon Maryam. Momy ta ce...
Chapter 42 · 0% Book details