Sashe 4
Addininmu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ai kuwa Daddy ya ce "Yes of course hakane ma. Samuel ya harareta yana jin kamar ya kamuta ya fara tattakata. Mommy ta ce "No inda shine da bazai zauna a d'akin ba tafiya zaiyi.
DADDY ya ce "Ya tashi ya dawo masa da kud'i kafin yasa sojojin waje su karkaryashi, Samuel de sai kuka yakeyi, shikuwa Daddy ya kafe akan dole shine ya d'auka.
Zahrah kuwa take taji ta daina jin yunwar tsabar tsoro, Daddy baya dukansu sai sun kaishi bango, yanzu da ita ya kama haka zaitama wannan dukun! Sai kuma ta fara tinaninn shimafa Samuel d'in tasan dole sukwaso riki dashi in ya warke. Take Kuma ta tuno da rabin ran nata tana jin in ta kai masa wannan kud'in ai za'a daina renashi tin da zai siya babbar waya. Take ta nemo number sa ta ai ka masa da Kira.
*ABDULLHA* *VOP*
Da sauri ya 'karasu gurin Abba yana mai d'an du'kawa kad'an ya ce "barka da yamma Abba gani?. Cikin sanyin murya da ta Saba da karanta ALQUR'ANI mai girma Abba ya ce "Abdullha kaga yanzu mutane suna ta magana a kanka akan zaman ka haka, kasan ba mutum baya cika mutam har sai ya ajiye iyali, yanzu fa kai ba 'karamin mutum bane, duk in da kashiga a 'kasar nann ansanka, kai harma wasu 'kasashien, kuma kaga kai ne mai yiwa mutane wa'a zi a kan aru'ke sunna a bar bidi'a, Amma kuma kai bakayiba shin hakan zai yu kuwa?...
Saboda haka abun da nakeso dakai shine kafitar da wacce kakeso ka yi sure domin al'umma su sake ganinn ka da kima. Abdullha ya dubi mahaifin nasa ya ce "Gaskiyane Abba, amma Abba duka-duka shekarata nawa da har zan fara maganar aure? Shekara tafa 26 zuwa da 27 Amma Zan fara zancen aure. Abba ya ce "Abdullha ka duba matsayin ka ba shekarunka ba, yanzufa mutane masu shekara. Arba'in ma girmamaka sukeyi, saboda haka nidai yanzu umarni zan baka akan ka fitar da wacce kakeso a cikin wannan shekarar.
Abdullha ya ce "Tom Abba tindadai kace umarnine in sha Allah Zan fitar. Abba wato shek kabiru kabuga, malimin sunna wanda yayi suna wajan ru'ko da sunna a fad'in duniya, wanda tin yaronsa wato abdullha Kabir yana 'karami yake tafiya dashi duk in da zashi kuma yake ja masa a'ya awajan wa'a zi. Har take yanzu shima abdullha yazama jigo ga al'umman dake tare da ma haifin nasa. Abba ya saka masa albarka sannan ya tashi ya tafi.
Abdullha kuwa gidan sa ya nufa yana shiga ya fad'a toilet yayi wanka sannan ya zauna ya fara rera karatun ALQUR'ANI mai girma cikin muryarsa mai sanyin dad'i, saida yayi izufi biyar (5) sannan ya shafa addu'a kafin ya zauna ya shiga tinanin maganar Abba...
To ni yanzu daba soyayya na keyiba ina ni ina wata budurwa! Nann take Aisha ta fad'o masa a rai, amma yayi tsaki yana cewa, wannan yarinyar batada kamun kai, haka dai ya dinga tufka da warwara, harma yayi banza da maganar ya kama har kokin gaban sa. Take yatina da cewa abokin safa ya gaiyace shi gurin bikin sa, amma ba wa'a zi zaiyiba zaije gurin walimar ne, walimar da uwar amaryar ce ta shirya, haka ya tashi ya shirya domin halartar gurin, kafin lokaci ya 'kure, domin kuwa abdullha yana kiyaye Al'kawari.
*ZAINAB*. *VOP*
Washe gari ta shirya tsaffff domin zuwa wani taro biki da a ka gaiyaceta zatayi qasida a gurin, Saida taje gurin Mama suka gaisa, sannan ta ce "Mama ina Aisha ne? Mama ta ce "Sun fita da Isa wai zata rakashi kasuwa. "Ok tom mu zamu je majalisi sai an jima zamu dawo, nann take Mama ta saka mata albarka sannan tamusu fatan nasara kafin ta fita, tabi d'akin mlm shima yasaka mata albarka kafin ta fita.
Tana zuwa waje taga halifiyar tata wato Maryam wacce duk wani taro ko mauludi in an gaiyaceta to tare suke zuwa, wani lokaci ma in Bata da time ita take turawa. Maryam tazama tamkar 'kawace ga Zainab sannan kuma yarinyar ta. In ana cikin hadaya na yabon Annabi Muhammad sallalahu a w s, girma take bata sosai, in kuma a zahirine ko a gida, zaka gansu acikin wasa da dariya.
Haka suka tafi cikin wasa da dariya. Suna isa gidan, matar da ta kirata tazo da gudu ta rungumeta tana kuka cike da mamaki wai yau gata ga Zainab Ambato. Ta ce "Zainab Ambato wallhi na kasance duk anguwarmu nafi kowa son ki da 'kasidunki, domin kuwa duk wata sabuwa gasidar ki in tafito sai na d'auko ta, tin kafin yarinyata ta samu mijin aure nayi Al'kawarin sai na gaiyatoki walimar auran kuma, gashi Allah yayi. Matar harda kuka, yayin da yarinyar matar ma tazo ta rungumeta sunata saka mata albarka.
Ita kuwa Zainab Ambato me take in banda mamaki cikeda farin cikin ganinn irin wannan tsan-tsar soyayyar. nann fa al'umma maza da mata suka fara murnar ganinn ta sai zuwa sukeyi ana hoto.
Da kyir aka samu a ka barta ta fara gabatar da majalusinta. Nann fa duk 'kasidar da ta fara sai kaji muryoyin al'umma tamkar sune sukayi, haka zatayi shiru al'umma sunayi kuma basa mantuwa, uwar amarya kuwa babu kunya ta ce yau ranar farin cikin tane, tafara rera 'kasidar Zainab Ambato kamar ita tayi. Ana cikin hakane a kazo kan 'kasidar da ta saka kwanannan wato *GANI ASO*. zokaga al'umma. Ana cikin ha sai ga ango da abokansa...
Angon shi kad'ai ne sai mutum biyu acikin abokannasa... Kana ganinn su kaga malamai aikuwa nannn al'umma suka hango Shek abdullha d'an gidan Shek kabiru kabuga. Nann fa suka fara mamakin mai ya kawoshi nann bayan bayason wannan wa'ke-wa'ken, tin daga nesa suka fara jin muryar mutane ana jin wa'kar Gani aso, dai-dai gurin da take cewa, ( *narantse da ilahumma ma'aiki bani da wani wanda nakeso ya maa'aiki Allah shine masanin zuci da baki, sanda nakemassa masoyin sa ma'aiki)*.
Nann take abdullha ya tsaya agurin ya kalli angon ya ce "Salim kace min walima za'a yi agurinnan? Salim ya ce "Sorry Shek wallhi nima bansan za'a gaiyato mawa'kiya ba, "Amma ai kasan yarinyar da ganima yar bidi'a ceko? Inji abdullha cikin tsananin b'acin rai. Salim ya ce "Kaga mutane na Kallon mu dan Allah muje muzauna sai muyi magana.
Abdullha ya ce nine zanje na zauna Ina kallon kad'e-kad'e da rare-rare? Salim ya ce "a'a za'a tsaya da shi yanzu please dan Allah? Saida abdalh yaga mutane sun fara kallon su kafin yabar maganar ya nufi gurin da a ka ware musu wato an kwaye.
D'aya daga cikin abokin angon me suna Yusuf ya ce "Wai ita wannan yarin yar ahaka zata 'kare rayuwarta da kad'e-kad'e da rare-rare bazatayi aureba? Abdalh ya ce "To waye zai auri wannan ai rashin wanda zai aurane yasa kaganta haryanzu. Salim ya ce "Haba kau wallhi wannan da kuke gani ba matar yara bace, ai ba kowane zai iya tin karar ta da batum aureba sai de manya malamai wallhi. dai-dai lokacin da abdallha ya bud'e baki zaiyi magana ita kuma Zainab Ambato ta kai idonta gurin take idinsu ya had'u a guri d'aya, Saida sukaiwa juna kallon minti d'aya kafin suka kawar da idonsu.
Yayin da abdullha yakejin mugun tsanar abun da takeyi kana take Mata kallon rashin kamunkai. Ita kuwa Zainab idonsu na had'uwa tamai kallon 'kiyayya kafin ta kalli halifiyarta ta ce "Jeki sakamin wa'kar bagudu bajadabaya, wato wa'kar da abdullha ya musu Randi a kanta jiya.
Ai kuwa dama wa'kar sabuwace kowa soyake a zo kan wa'kar domin kuwa WAQAR tayiwa mabiya shehu dad'i. Ai kuwa ana sawa al'umma suka d'auka, nann take suka fara fitowa da hoton shehu Mata damaza samari da 'yan mata, ko ganinn Zainab d'in ma bakayi. Saide kaji ana cewa... ( *BAGUDU BA JADABAYA KAN 'KWANAR SHEHU MAULANA).* ðŸ“
*PAGE* 👉4ï¸âƒ£
______________Muryoyin al'umma ne kawai ketashi agurin ana bin wa'kar kamar sune suka rerata, ita kuwa Zainab sai kallon gurinda Abdalh yake takeyi tana son ganin wani irin yanayi zai shiga. Abdullha kuwa yana ji tasaki wannan wa'kar ya kalli abokin nasa cikin tsananin b'acin rai ya ce "Nagode da abun da kamin sannan kuma in harkana so na cigaba da zama anann to sai an kori wannan mawa'kiyar. Angon ya kalli Abdalh sannan ya ce "Haba Shek abdullha kasanfa banine na gaiyatotaba uwar amaryar ce, kuma tana gurinnan kaga kuwa banida ikon korarr ta.
Abdullha najin haka ya mi'ke tsaye ya bar gurin cikin tsananin jin haushin abokin nasa. Tin da yake ba'a ta'ba cimasa fuska irin wannan ba, wato saboda ta ganshi agurin shena tasa a ka sake Mata wannan wa'kar ko!!? Haka Abdalh ya dawo gida cikin tsananin jin haushi, dama mukullen mutar na hannun sa, sai kawai ya tafi yabar su. Duk abun dake faruwa a kan idon Zainab, dama tasan bazai zaunaba hakanne yasa tayi amfaninn da wannan damar ta kore shi. Bayan ta gama rera 'kasidar ne kuma ta koma wa'a zi a kan zaman aure tsakanin ango da amarya. Tana musu tini da irin zan auran Nana fad'ima Yar ma'aikin Allah .s a w. Yanda tayi ha'kuri agidan mijin ta, sannan tamusu tinida da, rayuwar manzan Allah da yayi da iyalan sa, haka dai Zainab ta dinga kawo musu abubuwa da manzan Allah yayiwa matansa.
Daga 'karshe ta rufe da salatul fati. Abokin ango da ango sai mamaki sukeyi ganinn yanda ta dinga fad'ar irin abubuwan da ma'aurata ya dace da suyi domin koyi da sunnonin Annabi Muhammad sallalahu a w s azaman aure. Haka mutane suka dinga mata ihisani harda ango da kansa saida ya mata, haka uwar amarya ta rasa inda zata sakata tsabar murna.
*A.J POV*
Da sallama ya shigo gidan baki har kunne, ba kowa a tsakar gidan hakanne yasa ya sake doka wata sallamar, dai-dai lokacin Nana ta fito daga wanka, ta amsa sannan ta tsaya da bokiti a hannu tana kallon ledodin da suke hannun sa, cikin mama ta ce "Yaya wannan kumafa daga Ina? "Kafin ya bata amsa Innah ta fito daga cikin d'aki tana cewa "lafiya kuw... "Lafiya lau Innah kawai taga abun da bata saba gani bane shine ta tsaya sai tayi surutun nata da tasaba.
DADDY ya ce "Ya tashi ya dawo masa da kud'i kafin yasa sojojin waje su karkaryashi, Samuel de sai kuka yakeyi, shikuwa Daddy ya kafe akan dole shine ya d'auka.
Zahrah kuwa take taji ta daina jin yunwar tsabar tsoro, Daddy baya dukansu sai sun kaishi bango, yanzu da ita ya kama haka zaitama wannan dukun! Sai kuma ta fara tinaninn shimafa Samuel d'in tasan dole sukwaso riki dashi in ya warke. Take Kuma ta tuno da rabin ran nata tana jin in ta kai masa wannan kud'in ai za'a daina renashi tin da zai siya babbar waya. Take ta nemo number sa ta ai ka masa da Kira.
*ABDULLHA* *VOP*
Da sauri ya 'karasu gurin Abba yana mai d'an du'kawa kad'an ya ce "barka da yamma Abba gani?. Cikin sanyin murya da ta Saba da karanta ALQUR'ANI mai girma Abba ya ce "Abdullha kaga yanzu mutane suna ta magana a kanka akan zaman ka haka, kasan ba mutum baya cika mutam har sai ya ajiye iyali, yanzu fa kai ba 'karamin mutum bane, duk in da kashiga a 'kasar nann ansanka, kai harma wasu 'kasashien, kuma kaga kai ne mai yiwa mutane wa'a zi a kan aru'ke sunna a bar bidi'a, Amma kuma kai bakayiba shin hakan zai yu kuwa?...
Saboda haka abun da nakeso dakai shine kafitar da wacce kakeso ka yi sure domin al'umma su sake ganinn ka da kima. Abdullha ya dubi mahaifin nasa ya ce "Gaskiyane Abba, amma Abba duka-duka shekarata nawa da har zan fara maganar aure? Shekara tafa 26 zuwa da 27 Amma Zan fara zancen aure. Abba ya ce "Abdullha ka duba matsayin ka ba shekarunka ba, yanzufa mutane masu shekara. Arba'in ma girmamaka sukeyi, saboda haka nidai yanzu umarni zan baka akan ka fitar da wacce kakeso a cikin wannan shekarar.
Abdullha ya ce "Tom Abba tindadai kace umarnine in sha Allah Zan fitar. Abba wato shek kabiru kabuga, malimin sunna wanda yayi suna wajan ru'ko da sunna a fad'in duniya, wanda tin yaronsa wato abdullha Kabir yana 'karami yake tafiya dashi duk in da zashi kuma yake ja masa a'ya awajan wa'a zi. Har take yanzu shima abdullha yazama jigo ga al'umman dake tare da ma haifin nasa. Abba ya saka masa albarka sannan ya tashi ya tafi.
Abdullha kuwa gidan sa ya nufa yana shiga ya fad'a toilet yayi wanka sannan ya zauna ya fara rera karatun ALQUR'ANI mai girma cikin muryarsa mai sanyin dad'i, saida yayi izufi biyar (5) sannan ya shafa addu'a kafin ya zauna ya shiga tinanin maganar Abba...
To ni yanzu daba soyayya na keyiba ina ni ina wata budurwa! Nann take Aisha ta fad'o masa a rai, amma yayi tsaki yana cewa, wannan yarinyar batada kamun kai, haka dai ya dinga tufka da warwara, harma yayi banza da maganar ya kama har kokin gaban sa. Take yatina da cewa abokin safa ya gaiyace shi gurin bikin sa, amma ba wa'a zi zaiyiba zaije gurin walimar ne, walimar da uwar amaryar ce ta shirya, haka ya tashi ya shirya domin halartar gurin, kafin lokaci ya 'kure, domin kuwa abdullha yana kiyaye Al'kawari.
*ZAINAB*. *VOP*
Washe gari ta shirya tsaffff domin zuwa wani taro biki da a ka gaiyaceta zatayi qasida a gurin, Saida taje gurin Mama suka gaisa, sannan ta ce "Mama ina Aisha ne? Mama ta ce "Sun fita da Isa wai zata rakashi kasuwa. "Ok tom mu zamu je majalisi sai an jima zamu dawo, nann take Mama ta saka mata albarka sannan tamusu fatan nasara kafin ta fita, tabi d'akin mlm shima yasaka mata albarka kafin ta fita.
Tana zuwa waje taga halifiyar tata wato Maryam wacce duk wani taro ko mauludi in an gaiyaceta to tare suke zuwa, wani lokaci ma in Bata da time ita take turawa. Maryam tazama tamkar 'kawace ga Zainab sannan kuma yarinyar ta. In ana cikin hadaya na yabon Annabi Muhammad sallalahu a w s, girma take bata sosai, in kuma a zahirine ko a gida, zaka gansu acikin wasa da dariya.
Haka suka tafi cikin wasa da dariya. Suna isa gidan, matar da ta kirata tazo da gudu ta rungumeta tana kuka cike da mamaki wai yau gata ga Zainab Ambato. Ta ce "Zainab Ambato wallhi na kasance duk anguwarmu nafi kowa son ki da 'kasidunki, domin kuwa duk wata sabuwa gasidar ki in tafito sai na d'auko ta, tin kafin yarinyata ta samu mijin aure nayi Al'kawarin sai na gaiyatoki walimar auran kuma, gashi Allah yayi. Matar harda kuka, yayin da yarinyar matar ma tazo ta rungumeta sunata saka mata albarka.
Ita kuwa Zainab Ambato me take in banda mamaki cikeda farin cikin ganinn irin wannan tsan-tsar soyayyar. nann fa al'umma maza da mata suka fara murnar ganinn ta sai zuwa sukeyi ana hoto.
Da kyir aka samu a ka barta ta fara gabatar da majalusinta. Nann fa duk 'kasidar da ta fara sai kaji muryoyin al'umma tamkar sune sukayi, haka zatayi shiru al'umma sunayi kuma basa mantuwa, uwar amarya kuwa babu kunya ta ce yau ranar farin cikin tane, tafara rera 'kasidar Zainab Ambato kamar ita tayi. Ana cikin hakane a kazo kan 'kasidar da ta saka kwanannan wato *GANI ASO*. zokaga al'umma. Ana cikin ha sai ga ango da abokansa...
Angon shi kad'ai ne sai mutum biyu acikin abokannasa... Kana ganinn su kaga malamai aikuwa nannn al'umma suka hango Shek abdullha d'an gidan Shek kabiru kabuga. Nann fa suka fara mamakin mai ya kawoshi nann bayan bayason wannan wa'ke-wa'ken, tin daga nesa suka fara jin muryar mutane ana jin wa'kar Gani aso, dai-dai gurin da take cewa, ( *narantse da ilahumma ma'aiki bani da wani wanda nakeso ya maa'aiki Allah shine masanin zuci da baki, sanda nakemassa masoyin sa ma'aiki)*.
Nann take abdullha ya tsaya agurin ya kalli angon ya ce "Salim kace min walima za'a yi agurinnan? Salim ya ce "Sorry Shek wallhi nima bansan za'a gaiyato mawa'kiya ba, "Amma ai kasan yarinyar da ganima yar bidi'a ceko? Inji abdullha cikin tsananin b'acin rai. Salim ya ce "Kaga mutane na Kallon mu dan Allah muje muzauna sai muyi magana.
Abdullha ya ce nine zanje na zauna Ina kallon kad'e-kad'e da rare-rare? Salim ya ce "a'a za'a tsaya da shi yanzu please dan Allah? Saida abdalh yaga mutane sun fara kallon su kafin yabar maganar ya nufi gurin da a ka ware musu wato an kwaye.
D'aya daga cikin abokin angon me suna Yusuf ya ce "Wai ita wannan yarin yar ahaka zata 'kare rayuwarta da kad'e-kad'e da rare-rare bazatayi aureba? Abdalh ya ce "To waye zai auri wannan ai rashin wanda zai aurane yasa kaganta haryanzu. Salim ya ce "Haba kau wallhi wannan da kuke gani ba matar yara bace, ai ba kowane zai iya tin karar ta da batum aureba sai de manya malamai wallhi. dai-dai lokacin da abdallha ya bud'e baki zaiyi magana ita kuma Zainab Ambato ta kai idonta gurin take idinsu ya had'u a guri d'aya, Saida sukaiwa juna kallon minti d'aya kafin suka kawar da idonsu.
Yayin da abdullha yakejin mugun tsanar abun da takeyi kana take Mata kallon rashin kamunkai. Ita kuwa Zainab idonsu na had'uwa tamai kallon 'kiyayya kafin ta kalli halifiyarta ta ce "Jeki sakamin wa'kar bagudu bajadabaya, wato wa'kar da abdullha ya musu Randi a kanta jiya.
Ai kuwa dama wa'kar sabuwace kowa soyake a zo kan wa'kar domin kuwa WAQAR tayiwa mabiya shehu dad'i. Ai kuwa ana sawa al'umma suka d'auka, nann take suka fara fitowa da hoton shehu Mata damaza samari da 'yan mata, ko ganinn Zainab d'in ma bakayi. Saide kaji ana cewa... ( *BAGUDU BA JADABAYA KAN 'KWANAR SHEHU MAULANA).* ðŸ“
*PAGE* 👉4ï¸âƒ£
______________Muryoyin al'umma ne kawai ketashi agurin ana bin wa'kar kamar sune suka rerata, ita kuwa Zainab sai kallon gurinda Abdalh yake takeyi tana son ganin wani irin yanayi zai shiga. Abdullha kuwa yana ji tasaki wannan wa'kar ya kalli abokin nasa cikin tsananin b'acin rai ya ce "Nagode da abun da kamin sannan kuma in harkana so na cigaba da zama anann to sai an kori wannan mawa'kiyar. Angon ya kalli Abdalh sannan ya ce "Haba Shek abdullha kasanfa banine na gaiyatotaba uwar amaryar ce, kuma tana gurinnan kaga kuwa banida ikon korarr ta.
Abdullha najin haka ya mi'ke tsaye ya bar gurin cikin tsananin jin haushin abokin nasa. Tin da yake ba'a ta'ba cimasa fuska irin wannan ba, wato saboda ta ganshi agurin shena tasa a ka sake Mata wannan wa'kar ko!!? Haka Abdalh ya dawo gida cikin tsananin jin haushi, dama mukullen mutar na hannun sa, sai kawai ya tafi yabar su. Duk abun dake faruwa a kan idon Zainab, dama tasan bazai zaunaba hakanne yasa tayi amfaninn da wannan damar ta kore shi. Bayan ta gama rera 'kasidar ne kuma ta koma wa'a zi a kan zaman aure tsakanin ango da amarya. Tana musu tini da irin zan auran Nana fad'ima Yar ma'aikin Allah .s a w. Yanda tayi ha'kuri agidan mijin ta, sannan tamusu tinida da, rayuwar manzan Allah da yayi da iyalan sa, haka dai Zainab ta dinga kawo musu abubuwa da manzan Allah yayiwa matansa.
Daga 'karshe ta rufe da salatul fati. Abokin ango da ango sai mamaki sukeyi ganinn yanda ta dinga fad'ar irin abubuwan da ma'aurata ya dace da suyi domin koyi da sunnonin Annabi Muhammad sallalahu a w s azaman aure. Haka mutane suka dinga mata ihisani harda ango da kansa saida ya mata, haka uwar amarya ta rasa inda zata sakata tsabar murna.
*A.J POV*
Da sallama ya shigo gidan baki har kunne, ba kowa a tsakar gidan hakanne yasa ya sake doka wata sallamar, dai-dai lokacin Nana ta fito daga wanka, ta amsa sannan ta tsaya da bokiti a hannu tana kallon ledodin da suke hannun sa, cikin mama ta ce "Yaya wannan kumafa daga Ina? "Kafin ya bata amsa Innah ta fito daga cikin d'aki tana cewa "lafiya kuw... "Lafiya lau Innah kawai taga abun da bata saba gani bane shine ta tsaya sai tayi surutun nata da tasaba.