← Book details Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 128

Sashe 64

Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

...........A tare zuciyoyinsu suka buga da karfin gaske, kallon cikin ido matar take yiwa Maryam. Ita kuwa Maryam dasauri tayi kasa da idonta bugun zuciyarta na tsananta. a ranta tana fadin, "tsarki ya tabbata ga Ubangijin da yayi wannan kyakkyawar halitta." ita kuwa matar kara kafe Maryam tayi da ido, zuciyarta nacigaba da bugawa saboda mamakin abunda tagani a tare da Maryam. mama dabata lura da halin da Maryam da matar suke cikiba ta fadada fara'a tana duban matar tace. "Wannan matar yayansu ce daya rasu, shine babban dana, lokacin da akayi hatsarin tana Saudiya ne ta kaiwa mahaifiyarta da kaninta ziyara se jiya ta dawo" kallon matar daddy yayi a karo na biyu zuciyarsa na kissima masa wani abu akanta, muryarta ta masa dadi bakadanba, yayi mamaki daya kalli fuskarta yaga ta manyanta dan muryartata tamkar ta wata matashiyar saboda dadinta da sanyinta. ga muryartata ta sanya masa wani abu a cikin zuciyarsa wanda yakasa gane ko menene, hakan yasa yaji yanakuma son yakarajin muryartata. numfashi matar ta sauke, tana kokarin daidaita nutsuwarta. maida kallonta tayi ga Aunty datake gaisheta. Amsa mata tayi cikin sakin fuska. tana kokarin zama akan hannun kujerar da mama take, tamkar ance ta dago kanta idanunta yasauka akan Mustapha,daya kafeta da ido yana kallonta. wata mahaukaciyar bugawa zuciyarta tayi cikin tsananin razani tafasa zaman datake kokarinyi, ilahirin jikinta ne yadauki rawa tamkar mazari, hannunta na rawa take nuna Mustapha tanason tayi magana amma takasa, wani dimmm taji kanta yayi juwace ta kwasheta kawai segani akayi tayi kasa zata fadi. Dasauri matar da daddy yakade da mama sukayi kanta saboda sunfi kusa da ita, gaba-daya mutanen falon sukayi kanta, banda Mustapha dayakasa koda motsi, da Maryam. "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un" abun bakunansu kawai suke iya furtawa kenan. "Zuhura kikira Saddam, maza yazo mukaita asibiti jibifa jikinta yashika ko numfashi batayi" cewar matar da dady kayade cikin tsananin tashin hankali. "Nashiga uku, ni salamatu, dan Allah kutaimakamun mukaita mota, base munjira wani Saddam ba, semunje ta mace mana" mama tafadi haka tana hawaye. Aunty ce tace, "dama tanayin haka, kotana da wani ciwonne" "wlh bata da ciwon komai yarnan, bamu taɓa ganin tayi haka ba, seyau" mama tabawa Aunty amsa da fadin haka. "Ina ganinfa kamar suma tayi, a kawo ruwa mugwada watsa mata,zata farfaɗo insha Allah" daddy yafadi haka cikin son ya kwantar musu da hankali, ganin yadda gaba-daya hankulansu yatashi, zuhura da kanwar matar da daddy yakade harsun fara kuka. zuhurance tayi sauri taje ta dakko ruwa a fridge ta kawo, zuba mata ruwan aka shigayi a fuskarta zuwa kirjinta. kusan mintuna biyu ana zuba mata ruwan kafin taja wata doguwar ajiyar zuciya. Numfargashi tafara saukewa akai,akai. ganin ta farfaɗo sukayo kanta da mata sannu zukatansu cike da Murna. "Babu shakka familinnan suna matukar son matarnan" Aunty ta fadi haka a cikin ranta.

A hankali ta bude idanunta tana kallon mutanen dake zagaye da ita, hannun matar da daddy yakade ta kama, cikin sanyin murya me cike da rudani tace mata. "A'isha bani ruwa insha, guntun ruwan da'aka tsiyaya mata, A'ishan ta taimaka mata ta bata tasha. Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon mama tace, "mama wani mafarki nayi me rikitarwa" "wanne irin mafarki kuma diyar kirki" maman tatambayeta cike da mamaki. "Mama tunda natashi yau, nakejin wata irin faduwar gaba, jikina duk babu dadi kamar wadda wani mugun abun zesama, sekuma yanzu nayi mafarki A'isha tashigo dakina tasameni wai inzo mugaisa da mutanen dasuka bugeta, shine naga wani a zaune a falonnan, wlh yanda kikasan mijina na farko daya rasu babu abun daya banbantasu nakamanni, shine abun ya matukar firgitani" dammmm! Zuciyar daddy ta buga, jin muryar matar, a yanayin datayi magana yanzu babu banbanci da muryar matar data bashi Mustapha, shikanshi yana mamakin yanda amon muryar matar yakasa bacewa daga kwanyarsa duk kuwa da tsayin shekarunnan da aka dauka, a lokuta da dama idan yana zaune shikadai kalaman matar suna masa amsa kuwwa a cikin kwakwalwarsa. gabadaya falon tsit yayi dama Mustapha da Maryam basusan me'akeba. Sukuwa su mama, basu wani dauki zancen matar da mahimmanciba sun dauka zafin ciwon daya sametane lokaci daya ya firgitata. Aunty kuwa kallon matar kawai takeyi, ta kalli Mustapha ta kalli maryam. nuna Mustapha tayi tana kallon matar tace, "ko wancanne wanda kika gani ɗin?" dasauri matar ta kalli inda Aunty ta nuna mata, tozali idanunta suka mata da Mustapha wanda idanunsa suke a lumshe yanzu saɓanin dazu dayakafeta da tsumammun idanunsa shiyasama ta tsorata sosai harta sume. gani kawai sukayi ta mike tsaye zumbur, kura masa ido tayi na wasu sakanni kafin ta fara murza idonta dan tabbatar da ba gizo yake mataba. cikin karaji da matsananciyar rudewa muryarta na rawa tace, "sh...sh..shi..ne wlh, shineeeee!." takarashe zancen da jan maganar.
Chapter 64 · 0% Book details