Sashe 124
Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
.........Kwance nake a k'irjin yaya nayi shiru ina jin yanda bugun zuciyata yake k'aruwa, tun jiya da daddare gabana yake ta fad'uwa wanda bansan dalilin hakan ba. Shafa kanta Mustapha yayi cikin tsananin tausayinta, jikinta yayi zafi zau alamar zazzaɓi, cikin tsantsar kulawa yace "princess d'ita" na dan d'ago na kalleshi amma bance komai ba, fuskarta tayi fayau ga damuwa ƙarara akan fuskartata, yace "Please tell me, what happened to you?" cikin sanyin murya ina ƙoƙarin b'oye damuwata nace "babu komai yaya, ka yarda dani" yayi shiru kawai yana kallonta, tun jiya yaga yanayinta gabad'aya ya sauya, ga damuwa a tattare da ita, ƴar girimar da take masa ma jiyan batayiba, tambayar duniya ya mata meke damunta ko inane yake mata ciwo amma tace babu, yayi fushi ya kyaleta tasa masa kuka tace ita dai kawai ya tofa mata addu'a, batajin daɗi ne, yau kuma tunda safe data tashi yaji jikinta da zazzaɓi, yace suje asibiti a dubata taƙi, wai ita kar a mata allura. Na shafi gefen fuskarshi ganin yanda yake kallona, ajiyar zuciya ya sauke ya kai hannunsa ya shafi cikina yace "baby'nmu na wahalar dake ko, sorry" nayi murmushi ganin yanda yayi maganar nace "um, um yaya baya wahalar dani" yace "Allah yasa" na marairaice nace "yaya dan Allah ka barni naje na taya su ammi aiki, ko zanji k'warin jikina" yace "A'a, ki barsu suyi ai suna da yawa, yanzuma kuma sun kusa gamawa, koma ba hakaba keba cikakkiyar lafiya ba inake ina aiki" na turo baki gaba nace "wai yaya ni haka zanta zama bazan dinga aiki ba" yace "a'a amma dai sai baby'nmu yayi k'wari zaki cigaba" nace "haka akeyi dama?" Yace "mu haka zamuyi" nayi shiru ina tunanin wai nice yau da ciki, nice zan haihu nanda wasu watanni, zan zama uwa nima, wata irin soyayyar cikin da kaunarsa ce take ƙara cikamun zuciya. Bayan sallar azhar Dr husnah ta ƙaraso gidan, tun safe mustapha ya kirata akan rashin lafiyar Maryam, tace idan ta taso daga aiki zata biyo ta dubata. Ina d'akin yaya a kwance shi kuma yana falo, ya shigo yana dubana yace "bacci kike ne?" na girgiza masa kai alamar a'a, ya ƙaraso kan gadon ya zauna a baki yana faɗin "ga Doctor nan tazo zata dubaki" na tashi zaune ina kwabe fuska nace "yaya dan Allah kace mata karta mun allura, wlh tanada zafin hannu" ya shafa fuskarta yana murmushi yana tuno darun da'aka sha da ita a asibiti time ɗin da za'a dibi jininta da yi mata allura, cikin kwantar da murya yace "dubaki kawai zatayi ta baki magani" na turo baki gaba nace "nifa lafiyata k'alau" becemun komai ba ya tashi ya fita, two minutes suka dawo ɗakin tare da Dr husnah da sallamarsu, bayan na amsa musu ta dubeni tana murmushi tace "maman biyu, me raki" nayi murmushi kaina a ƙasa nace "ina yini" tace "lafiya ƙalau, ya jiki_jiki?" cike da kunya nace "da sauƙi" ta ƙaraso kan gadon ta buɗe jakar ta ta fara dubani, bayan ta gama ta dubi Mustapha tace "zazzaɓi ke damunta, amma bayan shi babu matsalar komai, yanzu zan rubuta mata magani sai ka siyo mata tasha, tunda batason allura" Mustapha yace "ai gwara ayi mata allurar, dan maganin ma basha zatayiba" na marairaice nace "nidai nafison maganin kuma zansha" yace "shima basha zakiyiba na sani" ya maida dubansa ga Dr husnah yace "kimata allurar kawai" Dr tayi murmushi ta shiga haɗa allurar, na kalli yaya kamar zanyi kuka, ya ɗauke kanshi, bayan tagama haɗa allurar tace "saifa ka riketa" ya tako ya hawo kan gadon ya janyoni jikinsa, na riƙe shi gam dan har na fara jin kamar antsikaramun allurar ajikina, jin hannun Doctor a jikina tana ɗan yin ƙasa da skirt d'in jikina na runtse idona ina ƙara ruk'unk'ume yaya, tana tsikaramun nayi wani zillo hawaye na kwaranyomun, sosai naji zafin allurar gashi dama duk a tsorace nake, yaya ya shiga mulmulamun gurin yana hura mun iska a cikin kunnena, na cizeshi a gefen wuyansa, ya shafa gashin kanta a hankali yace "sorry baby nah" nayi masa shiru ina sauke numfashi tare da ƙara lumshe idona, wani irin bacci na fizgata, cikin abun da baifi 5 minutes ba bacci ya ɗaukeni, Mustapha ya kwantar da ita a hankali jin tayi bacci ya fita falo inda Doctor take jiransa, suka ɗan ƙara tattaunawa akan jikin Maryam ɗin, tace masa babu matsalar komai sannan sukayi sallama ta tafi.
Misalin ƙarfe uku da 'yan mintuna uncle ɗin Mustapha suka ƙaraso gidan su Ammi cikin k'oshin lafiya. Ammi tana harabar gidan tana jiransu, ganinsu yasa ta nufesu da sauri tana ƙara faɗaɗa fara'a akan fuskarta, mahaifiyarta ta fara rungumewa tana mata sannu da zuwa, sannan k'aninta MUHAMMAD mai tsananin kama da ita, sai matarsa kyakkyawa da ita da yaranta twins mace da namiji. Aunty ta jasu zuwa part d'in baƙi na gidan, wanda yasha gyara saboda zuwansu, bayan sun zauna aka ƙara gaggaisawa, Mama, Zuhura, mama Nafisa da Umaimah suma sun ƙaraso falon dan tarbarsu, UNCLE MUHAMMAD wanda yaranshi suke kiranshi da ABBU, sai baza ido yake yana son ganin ta inda d'anshi Mustapha zai ɓullo, mahaifiyarsu su ammi wadda suke kira da HAJJA itama haka dan dama ganin ɗan jikallennata ne ya kawo ta Nigeria. Da sallama ya shigo falon gabad'aya suka zubo masa ido zuciyoyinsu cike da d'okin ganinsa, shi kanshi a nashi a ɓangaren haka ne, fuskarsa ɗauke da murmushi ya ƙarasa ya rungume UNCLE d'insa, wanda ya k'ura masa Ido, cikin Muryar mai cike da zallar farin ciki yace, "welcome my dearest uncle" Abbu ya shafa kansa fuskarsa ɗauke da yalwataccen murmushi yace "welcome Son like no other, nice to meet you" cikin tsananin kaunar uncle d'innasa yace "me too" tare da sakinshi ya nufi gurin wadda yake da tabbacing itace grandmother d'insa saboda yadda take kama da Amminsa duk da ta manyanta, Hajja wadda ta saki baki da hanci tana kallonsa cike da tsananin mamaki ta fashe da kuka cikin hausarta da bata fita sosai "Allah k'adiran, mai girma da juya al'amari a duk yadda yaso, tabbas wannan babu tantama jininmune kuma jinin modibbo, lallai ikon Allah ya wuce gaban komai, yaro mai tsananin kama da ubansa, yanda kasan modibbo haka nake ganinsa" mustapha ya ƙarasa gareta ya rungumeta, ta rungumeshi itama tana cigaba da kuka tana faɗin "ashe da rabon zaka dawo garemu, Allah ya jikan mahaifinka adalin mutum mai farar zuciya wadda ke cike da alheri" Mustapha ya amsa da "ameen" tare da sakinta ya shiga share mata hawaye, yanajin wata irin kaunarta na ratsa masa zuciya, Ammi tayi ƙasa da kanta tana ƙoƙarin maida kwallar data taron mata a ido saboda tuno mata da mutumin da bata da kamarsa a duniya, Hajja ta ƙara ruk'unk'ume Mustapha a jikinta tana kuka, ya samu ya lallasheta tayi shiru, amma fa duk inda yayi idanta na kansa, gurin matar UNCLE d'insa wadda yaranta suke kiranta da Ummee yaje ya gaisheta, twins suka taho jikinsa gabad'aya suna gaisheshi, yara kyawawa 'yan kimanin shekara 7, sai larabci suke zuba masa, Mustapha ya ƙurawa macen ido saboda yadda take acting ɗinta sai yaga kamar Maryam ɗinsa, musamman idan ta waro manyan fararen idanunta ko kuma ta turo ɗan ƙaramin bakinta gaba idan, ya rungume yaran a jikinsa cikin kaunarsu. Su ammi suka cikawa su Hajja gabansu da lemuka nasha kala_kala da ruwa, Abbu kuma sanin da Ammi ta masa baya shan abu mai sanyi, sai ta kawo masa had'add'en shayin data masa na musamman. Ammi ta dubi Mustapha tace "ina ɗiyata kuwa, ko batasan sun ƙaraso bane" Mustapha ya ɗan shafi kansa yace "tana bacci ne, amma bari na taso ta" Hajja ta amshe zancen da faɗin "a'a, karka tasota barta tayi baccinta, abunda muna gidan ba yau zamu tafi ba, idan ta tashi ma gaisa" Mustapha yace "ai lokacin Sallah ma yayi kuma ta jima tana baccin" Ammi tace "katasota toh tunda ko abincin rana bata ciba" ya amsa tare da miƙewa, Umaimah ta bishi da kallo cike da kaunarsa, twins suka ce zasu bisa, umminsu ta hanasu.
Misalin ƙarfe uku da 'yan mintuna uncle ɗin Mustapha suka ƙaraso gidan su Ammi cikin k'oshin lafiya. Ammi tana harabar gidan tana jiransu, ganinsu yasa ta nufesu da sauri tana ƙara faɗaɗa fara'a akan fuskarta, mahaifiyarta ta fara rungumewa tana mata sannu da zuwa, sannan k'aninta MUHAMMAD mai tsananin kama da ita, sai matarsa kyakkyawa da ita da yaranta twins mace da namiji. Aunty ta jasu zuwa part d'in baƙi na gidan, wanda yasha gyara saboda zuwansu, bayan sun zauna aka ƙara gaggaisawa, Mama, Zuhura, mama Nafisa da Umaimah suma sun ƙaraso falon dan tarbarsu, UNCLE MUHAMMAD wanda yaranshi suke kiranshi da ABBU, sai baza ido yake yana son ganin ta inda d'anshi Mustapha zai ɓullo, mahaifiyarsu su ammi wadda suke kira da HAJJA itama haka dan dama ganin ɗan jikallennata ne ya kawo ta Nigeria. Da sallama ya shigo falon gabad'aya suka zubo masa ido zuciyoyinsu cike da d'okin ganinsa, shi kanshi a nashi a ɓangaren haka ne, fuskarsa ɗauke da murmushi ya ƙarasa ya rungume UNCLE d'insa, wanda ya k'ura masa Ido, cikin Muryar mai cike da zallar farin ciki yace, "welcome my dearest uncle" Abbu ya shafa kansa fuskarsa ɗauke da yalwataccen murmushi yace "welcome Son like no other, nice to meet you" cikin tsananin kaunar uncle d'innasa yace "me too" tare da sakinshi ya nufi gurin wadda yake da tabbacing itace grandmother d'insa saboda yadda take kama da Amminsa duk da ta manyanta, Hajja wadda ta saki baki da hanci tana kallonsa cike da tsananin mamaki ta fashe da kuka cikin hausarta da bata fita sosai "Allah k'adiran, mai girma da juya al'amari a duk yadda yaso, tabbas wannan babu tantama jininmune kuma jinin modibbo, lallai ikon Allah ya wuce gaban komai, yaro mai tsananin kama da ubansa, yanda kasan modibbo haka nake ganinsa" mustapha ya ƙarasa gareta ya rungumeta, ta rungumeshi itama tana cigaba da kuka tana faɗin "ashe da rabon zaka dawo garemu, Allah ya jikan mahaifinka adalin mutum mai farar zuciya wadda ke cike da alheri" Mustapha ya amsa da "ameen" tare da sakinta ya shiga share mata hawaye, yanajin wata irin kaunarta na ratsa masa zuciya, Ammi tayi ƙasa da kanta tana ƙoƙarin maida kwallar data taron mata a ido saboda tuno mata da mutumin da bata da kamarsa a duniya, Hajja ta ƙara ruk'unk'ume Mustapha a jikinta tana kuka, ya samu ya lallasheta tayi shiru, amma fa duk inda yayi idanta na kansa, gurin matar UNCLE d'insa wadda yaranta suke kiranta da Ummee yaje ya gaisheta, twins suka taho jikinsa gabad'aya suna gaisheshi, yara kyawawa 'yan kimanin shekara 7, sai larabci suke zuba masa, Mustapha ya ƙurawa macen ido saboda yadda take acting ɗinta sai yaga kamar Maryam ɗinsa, musamman idan ta waro manyan fararen idanunta ko kuma ta turo ɗan ƙaramin bakinta gaba idan, ya rungume yaran a jikinsa cikin kaunarsu. Su ammi suka cikawa su Hajja gabansu da lemuka nasha kala_kala da ruwa, Abbu kuma sanin da Ammi ta masa baya shan abu mai sanyi, sai ta kawo masa had'add'en shayin data masa na musamman. Ammi ta dubi Mustapha tace "ina ɗiyata kuwa, ko batasan sun ƙaraso bane" Mustapha ya ɗan shafi kansa yace "tana bacci ne, amma bari na taso ta" Hajja ta amshe zancen da faɗin "a'a, karka tasota barta tayi baccinta, abunda muna gidan ba yau zamu tafi ba, idan ta tashi ma gaisa" Mustapha yace "ai lokacin Sallah ma yayi kuma ta jima tana baccin" Ammi tace "katasota toh tunda ko abincin rana bata ciba" ya amsa tare da miƙewa, Umaimah ta bishi da kallo cike da kaunarsa, twins suka ce zasu bisa, umminsu ta hanasu.