← Book details Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 128

Sashe 25

Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Aliya nazaune a bakin hado ta rafka tagumi nashigo dakin da sallama ciki_ciki, tsayawa nayi kawai ina kallonta daga ganinta itama jikinta yayi week. Ahankali tadago da kanta ta zubamun ido, karasawa nayi bakin gadon nazauna agefenta dafa kafardarta nayi nace, "aliya Ashe yau zakutafi shine baki sanarmunba, seyanzu aunty take sanarmun" numfashi aliya tasauke tace, "kiyi hakuri maryam,aunty ce tace karna fada miki seyau,dantasan seki tashi hankalinki kikasa bacci." "Yanxu idan kuka tafi seyaushe?" Natambayeta idona nacikowa da kwalla, kwanaki ukunnan damukayi tare dasu jinta nake tamkar mundau wasu shekaru tare, yanzu idan suka tafi shikenan rayuwar kuncin danake agidannan zata dawo,tunda sukazo ko kallon banza babu Wanda yamun agidan se ranar da abunnan yafaru saboda ganin idon aunty. Na lura duka yaran gidan suna Shakkar aunty. Banmasan hawaye yafara zuba daga idonaba seda naji hannun aliya tana sharemun, itama idonta duk yayi kwal_kwal kamar zatayi kukan. gabadaya tausayin maryam yacika mata zuciya,tasan halin yan'uwanta sarai ba kirkine dasuba,tasan maryam zaman hakuri kawai takeyi agidannan. Rungumeta tayi tsam ajikinta ganin taki dena kukan, cikin rarrashi take bubbuga bayanta. Magana tafara mata cikin rarrashi da lallami akan tayi hakuri, insha Allahu dazarar anmusu hutun school zatazonan tayi hutunnata gabadaya tare da ita. Dakyar aliya tasamu maryam ta hakura tadena kukan. Toilet nashiga nakara wanke fuskata,sannan nadawo nakarasa shirina, aliya nata bani labaran bandariya duk dan nasaki jikina. Nikuma se nuku_nuku nakeyi naki tafiya, harseda yaya sadiq yakira wayar aliya akan yana waje yana jirana. Dakin mommy naje, namata sallama,yau dakantama tace intafi karnayi latti base nayi serving dinsu ba. Kuku harya gama hada breakfast yau da wuri, diddibarmun aliya tayi na tafi dashi, dakin aunty na koma kamar yadda tace. Wani littafin addu'oi ta dakko ta bani har guda biyu, tace nadaure nadinga karantawa arana koda saudayane. Godiya na kara mata sosai, itakuma tanata kwararamun addu'oi. Har bakin motar da yaya sadiq yake ciki aliya ta rakani. Abincin dake hannunta ta mikomun tare da fadin, "to maryam segani nabiyu" karba nayi cikin sanyin jiki nace, "nagode aliya,kugaida gida Allah yakiyaye hanya" "ameen" cewar aliya tana maida hankalinta akan yaya sadiq dake zaune acikin mota amma ya bude murfin, kafafunsama suna waje. yatsaya kawai yana kallonmu da sauraronmu. "Yaya sadiq ga maryam nan, dan Allah kakularmun da ita amana karka bari ko kuda yatabata, balle kuma wani Abu yabata mata rai." Murmushi mukayi nidashi saboda yanda aliya take maganar, yace, "baki da damuwa yarkanwata indai maryam ce zankula miki da ita fiye da yanda kike tunani." "Yawwa yayana, maryam bye bye, semunyi waya, insha Allah zandinga kiran wayar yaya sadiq muna gaisawa, I will miss u over" da kai kawai nabata amsa, saboda ina bude baki tsaf zan iya saka kuka, daurewa kawai nakeyi. Zagayawa nayi na shige cikin motar, daga mun hannu aliya tayi ta juya tatafi,ina binta da kallo. Tada motar danaji yaya sadiq yayi yasani dauke ido daga kanta,ina sauke ajiyar zuciya. Kallona yayi dasauri sekuma yadauke kansa yayi yaja motar muka tafi. Hawayen dake makale a idonane yasamu damar zirarowa, nikuma haka kaddarata take arayuwa, duk Wanda nakejin dadin zama dashi, sena rabu dashi..... "Yasalam, maryam! Kuka kuma, kiyi hakuri pls nasan kunyi sabo da aliya Wanda dole zakiji zafin rabuwarku, amma kukan bashine mafitaba, kidena kinji" murya yaya sadiq ta katsemun tunani. Daga masa kainayi ina share hawayena. "Yawwa kokefa, duk sanda kikeson ganin aliya na miki alkawari zankaiki, ammafa idan kindena kuka" dasauri nace, "nadena yaya sadiq Allah" murmushi yayi yace toh shikenan kyakkyawa" shiru nayi bance masa komaiba, shima yaya sadiq shirun yayi har muka karasa school din. Yau kam sukuku nayi a makarantar har zee seda tatambayeni ko bani da lafiya, nace mata lpy ta klu. Koda aka tashi nadawo gida, duk senaji gidan babu dadi, saboda su aliya suntafi kamar yadda aunty tace, zama nayi bayan nayi sallah na rafka tagumi ina tunanin rayuwata, ganin tunanin babu abunda ze karamun se damuna sena tashi na dakko littafin addu'ar da aunty ta bani, na karanta, cikin ikon Allah se zuciyata tayi sanyi,damuwata duk ta ragu. Haka rayuwa take Allah baya barin wani Dan wani yaji dadi. Bayan na gama karantawa na tashi naci gaba da ayyukana.........

*BAYAN KWANA UKU*

Rayuwata ta koma kamar tada agidan alh. Menasara,rayuwar kadaici da kunci da tsangwama agurin yaran gidan, a gurin yaya sadiq kawai nake samun sauki, bayan tafiyar su aliya munyi waya da ita har sau biyu, a wayar yaya sadiq, aunty ma haka. Harda yayantama mungaisa, yacemun aliya tanata damunsa da zancena. Dadin abunma ina zuwa makaranta, tanadaukemun kewa sosai, nasaba da zee sosai da sauran kawayenta, su salma da humaira. Kullum yaya sadiq ne yake kaini, driver kuma ya dakkoni. Yanzuma bana gamuwa da yaran gidan sosai, dan dasafe kafinma su fito natafi makaranta da rana idannadawo basanan sai dare muke haduwa.

Abangaren suhailat kuma, cin karanta take babu babbaka tunda aunty tatafi, kullum setaje gurin kamal sun sheke ayarsu, kuma ta dawo zuwa part din mustapha, danma yanzu kotaje bawani kulata yakeyi sosaiba sedai tagaji da zama da tatafi, babban abun dayake kara tada hankalinta yanzu ko hannunsa baya bari tataba. Ko zuwa tayi da niyyar tabashi kamar da, bata iyawa saboda babu fuska. Shikuma mustapha ayan kwanakinnan aiki yakeyi tukuru, gashi a week dinnan zeyi promotion na ma'aikata a companynsu dole ne ya nutsu yamaida hankali danganin yayi adalci ya'ajiye kowa a inda yadace dashi.

Yanzu kam yagane babban kuskuren daya tafka arayuwarsa na barin suhailat tana hugging dinshi da abubuwan dabasu daceba,ada baya daukar hakan amatsayin lefi saboda ganin suhailat cousin dinsace. Zuwannan da aunty tayi shiya kara tunatar dashi abunda yamanta, nasiha aunty tamasa sosai akan illar hakan,yasan aunty bata taba ganinsu a hakanba, kawaidai ta masa wa'azinne akan tunatarwa irinta da da uwa. shine dalilin dayasa yayiwa kansa alkawari idan ba aure sukayiba insha Allahu hakan bazata kara faruwa atsakaninsuba,sedai bisa kuskure. Mommy amatsayinta na uwarsu yakamata ace ita tafara nuna musu illar hakan, tunda sometimes agabanta suhailat din take hugging dinsa. Amma sedai tanuna jindadin hakan. Yana matukar son mommynsa amma bayason wasu halayennata, da first halinta dabayaso shine kyamar talaka, tana nuna musu takala bakowa bane, tana nuna musu talaka tamkar ba cikakken mutum bane. Alhalin Allah dakansa yafada shiyake bada wadata da arziki ga wanda yaso. Kuma badon yafisansa yabasaba, sedon ganin damarsa. kuma aduk sanda yaso ze iya kwacewa. To meyasa ita mommy bata tunanin wata rana suma zasu iya rasa tasu dukiyar, kokuma talakan datake rainawa yamusu ranar wani abun, domin kowa da irin baiwar da Allah yamasa. Sekuma hali na biyu na mahaifiyarsa dabayaso,macece ita me mugun son kanta da yayanta, kome yayanta zasuyi badaidaiba bazata musu maganaba, balle ta kwabesu. Komai sukayi nuna musu take daidaine, gashu kuma batadamu da musu wata kyakyakkyawar tarbiyyaba, ilimin addini kuwa duk basu dashi yanda yakamata, shima dan ya taba zama agurin auntyne lokacin su mommy dukansu suna america, shikadaine a naija, shiyasa yasamu ilimin addine sosai. Sekuma abu na uku, yanda mommy take juya mahaifinsu sekace wani danta, se'abunda tace yayi sannan zeyi, bayajin maganar kowa setata. Wadannan halaye na mahaifiyarsa bayasonsu kokadan, dandai babu yanda zeyine uwa, uwace tafi karfin wasa, sedai addu'a dabaya gajiyawa dayi mata akodayaushe akan Allah yaganar da ita gaskiya.....✍️

```BA EDITING YAU🤤😔```

*By*
*zeey kumurya*
*ABUNDA KA SHUKA*.........
_*(shizaka girba)*_

*MALLAKIN*
👇
*ZAINAB USMAN KUMURYA*

*FARIN JINI WRITERS ASSO.....*📚

~*Free novel*~

*Bismillahirrahmanirrahim*

2️⃣1️⃣

*BA EDITING YAU🤤😎*

........Yau asabar babu school hakan yasa bantashi da wuriba se wajen goma na tashi, ayyukana nayi duka, saboda yau ina gida. Amma kwanakin da suka shude bakomai nakeba nake tafiya school cikin abunda banayi harda gyaran dakin suhailat da mommy, senadawo nakeyi. Yau time din dana shiga dakinta bacci takeyi bata tashiba, ko agurin break ma banga tafitoba. Se bayan la'asar nagama aikina, saboda har wanki nayi. Ina gamawa nayi wanka nashirya cikin wata doguwar riga mara nauyi da hijabi karami irinna makannan, acikin siyayyar kayan da yaya sadiq yasiyomun jiyane. Duk wani Abu na amfanin mata seda yasiyomun jiya har kayan unders yasiyomun dasu pad, siyayya yamun sosai ta bajinta, duk a kokarinsa na ganin narage damuwa, ga wani tattali da kulawa dayake bani na musamman. nikam nikadai nasan halin danake ciki saboda rashin ganin mustapha, zuwa yanzukam nafara tunanin akwai wani Abu dayake faruka dani akansa, tunaninsa da wani abu dabansa komeneba ya yawaita araina, kullum bana iya bacci sena dauko rigarsa dake gurina nashaki kamshinsa sannan nake samun nutsuwa. Yau kwanana biyar banganshiba tun ranar da abunnan yafaru, wata mahaukaciyar kewarsa naji tacikamun zuciya. Duk wannan abun dake damun maryam akan mustapha kokadan batayi tunanin so bane, dan ita bama tasan menesodinba, anata shirmen kawai burgeta yakeyi. Bayan na idar da sallane, nadakko addu'ar da aunty tabani nakaranta.
Chapter 25 · 0% Book details