Sashe 53
Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Tundaga lokacin da isma'il yarasu abubuwa suka fara tabarbarewa, nazama tamkar uwargijiya da baiwarta tsakanina da atika se'abunda tace nayi shinakeyi, kuma duk abunda zatayi nabadaidaiba ban isa na tsawatarmataba. Tarabani da yan'uwana dama ita nata bawani damunta sukayiba. yarama kowa abunda yakeso shiyakeyi babu me kwabarsu,bankuma isa natsawatar musuba. Alokacin ne kuma namanta da batun dukiyar mustapha cefa a hannuna ina juyata, senaji kawai tamkar damacan dukiyar tawace. Burin danake dashi na insanar da mustapha dukiyarsace da kuma burin komawa garin Niger domin nemomasa danginsa duk yakau daga kwakwalwata nama manta dashi gabadaya, sabanin da da kullum da tunanin hakan nake kwana nake tashi araina. kawaidai abunda nasan nayi duk wani harka ta kasuwancina ina saka mustapha akan gaba, sauran yayanama kowa yagama karatu zandorashi akan harkar kasuwancina. Wannan shine takaitaccen labarin dazan Baku, dakuma yanda muka samu mustapha." shiru dakin yadauka bakajin motsin komai se karar fanka da sassauke numfarfashi da kowa yakeyi. Gabadaya bakunansu sun musu nauyi sunkasa sarrafa harshensu balle susamu damar koda furta harafi dayane, saboda tsabar mamaki gami da al'ajabi da jimami. Mustapha kawai kallon daddy yakeyi tunda yafara bada labarin, wani irin yanayi yakeji ajikinsa me wuyar fassaruwa,yanda yakejin zuciyarsa tamkar ana rura masa wutar garwashi acikinta, gani yakeyi tamkar daddy kirkirar labarin yayi kawai ya basu. tayaya ze iya daukar wannan bakon al'amarin ace mominshi me kaunarsa meson ganin farincikinsa akodayaushe ba'ita ta haifesaba. ahankali ya yunkura idanunsa a lumshe tsabar damuwa ko gani bayayi ya mike yana layi ya karasa gaban mommy yadurkusa yakama hannunta, cikin wahalalliyar murya menuni da me ita shikadai yasan azabar dayakeji yace, "mommynah, nike nasani amatsayin mahaifiya kuma kenaso nacigaba da kallo amatsayin uwata dan Allah kimusantamun abunda daddy yafada konaji sanyin tafarfasar da zuciyata takemun,wlh kwakwalwata bazata iya daukar wannan lamarinba" wani irin kallo mommy tamasa me wuyar fassaruwa tana murmushin mugunta tace, "mustapha kada ka bata bakinka gami da wahalar dakanka akan abunda yake na gaskiya zuwa wanda bashi bane. ninan atika dakaganni banasonka bana kaunarka mesonkama bana sonshi imfact madai duk duniyarnan babu wanda na tsana sama dakai mustapha, saboda haryau zuciyata bata yarda da zancen sulaimanba, nafi yarda da ciki yayiwa wata a waje ta haifeka" mommy tafadi haka babu alamar nadama a tatattare da ita. Gabadaya yarannata ido suka zuba mata suna kallonta yanda take magana babu alamun rahama akan fuskarta. Aunty kuwa kanta nakasa tana karanto addu'ar samun nutsuwa domin kuwa yanda taji al'amarin a baibai waiba mommy ce tahaifi mustapha ba, kuma duk irin tarin soyyayar datake nuna masa ashe duk na muguntane,lallai mommy ta iya zagon kasa,kuma ta cika cikakkiyar makira. mustapha cikin fitar hayyaci yakara damke hannun mommy idanunsa nazubar da hawaye yace, "mommy meyasa bakya sona wanne lefi namiki arayuwa, please and please mommy kisoni sona gaskiya nike kadai nasani amatsayin uwata kome zakimun kuwa bazantaba canza matsayinkiba,domin banida kamarki" dagowa aunty tayi tana kallonsa cike da tausayawa idanunta nazubar da hawaye, yanda yake kuka yana rokon mommy, abunda ta manta rabon dataga kukansa, domin shi mutum ne mejuriya akan komai. tabbas akwai tashin hankalin da idan yazowa mutum duk jarumtarsa be isa ya jure masaba. daddy ma cike da tausayawa yake kallon dannasa abun kaunarsa, duk da daddy yasamu wasu yayan amma bayajin kaunarsu kamar yadda yakejin ta mustapha,kaunar mustapha daban take acikin zuciyarsa. Faruqne ya matso yakama mustapha yarungumeshi ajikinsa. shima idanunsa nazubar da hawaye yace, "yaya mustapha dama nine kai, domin kai kayi sa'ar mahaifiya sabaninmu dabayi sa'artaba, mahaifiyarka tazabi mutuwa kaikuma karayu saboda tsananin kaunar datake maka,amma mu mommy da kanta take cutar damu duk dan akan duniya tabbas nasan idan kaji irin abubuwan da mommy tamaka na cutarwa zaka tsaneta, kuma bakaikadai ta cutarba harda wasu bayin Allah dabasujiba basu ganiba duk domin dukiyarka ta zamo mallakinta ita yayanta,inama ana canza uwa dase nazanca mommy wlh, domin bata da imani kokadan" yakarashe zancen yana fashewa da kuka meban tausayi. mommy ce ta amshe zancennasa da fadin, "bana nadama kodanasani arayuwata tunda nafarata, kuma ayanzuma banyiba kuma bana fiddaran zanci nasara akan abunda nasa gaba,domin duk abunda na kudura arayuwata sena cimma nasara akansa komeneshi kuma komun wuyarsa ko....." "ba'aiwa Allah izgili kada kiga kinsamu nasara abaya kiyi zaton zaki kara samu nangaba, insha Allahu alkadarinki ya karye daga yanzu, kuma da sannu zaki girbi *abunda kika shuka* da hannunki" daddy yakatse mommy da fadin haka cikin tsananin bacin rai gamida takaicinta tare da danasanin kasancewarta matarsa. Mommy batabi takan maganar daddyba. tadubesu duka tace, "bari na baku kadan daga cikin labarin irin abubuwan dana aikata duk domin nasamu biyan bukatar raina" gabadaya ido suka zuba mata akaro nababu adadi amma banda sadiq dakansa yake a sunkuye tunsanda daddy yafara bada labari. Mikewa mommy tayi tai taku uku sannan ta fara magana kamar haka:..........✍️
*BY*
*zeey kumurya*
*ABUNDA KASHUKA*
_*(shizaka girba)*_
*3️⃣8️⃣*
*Bismillahirrahmanirrahim*
*BY*
*zeey kumurya*
*ABUNDA KASHUKA*
_*(shizaka girba)*_
*3️⃣8️⃣*
*Bismillahirrahmanirrahim*