← Book details Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 128

Sashe 49

Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Rayuwa tasauyamun sosai nasamu budi da nasara aharkar kasuwancina sosai, nasamu rufin asirina daidai gwargwado. abokina sa'idu shine yasamun sunan *menasara* daganan sunan yabini wasuma idan kace musu sulaiman bazasu sugane nikake nufiba sekace musu *menasara* watanmu shida dakomawa nijer dazama nida atika, Allah ya'aiko mana da wani iftila'i, kayana na shago sunkare kaf, natattara kudadena a buhu, zanzo gida nayi siyayya, lokacin account beyi yawaba, dama tafiyar dare mukayi yan fashi da makami suka tare motarmu akan hanya,suka kwace komai namu dagamu se tufafin jikinmu sukabarmu, se juyo damu driven yayi domin dama yawancinmu sare_sare zamu kuma gashi ankwace kudin sarin, dayawa daga cikin wadanda muke a motar kusan zaucewa sukayi,manyan maza magidanta segamu da kuka shabe_shabe da hawaye. wannan fashin da'aka mana bakaramin talautamu akayiba, danseda takai ta kawo naira biyarma gagararmu takeyi, dan abincin da sauran kudin da'akabarwa mata agida duk ancinyesu. Nashiga cikin tsananin tashin hankali bakanba a wannan lokacin narasa ina zantsoma kaina, gashi ko kudin motarma dazan mana mudawo gida Nigeria nida atika kozan samu abunyi anan babu. Alokacinne kuma atika ta fitomun da ainihin halinta na rashin imani da tausayi, kullum cikin yimun tijara da rashin mutunci take, akan rashin da Allah yadoramun, bata ganin nima bayin kaina bane. Kaddarace Allah yadoramun dakuma jarrabawar rayuwa. Watarana da daddare ina zaune a tsakar gidanmu ranar munwuni bamuciba nayi tagumi ina tunanin yanda rayuwa tazomun atika tafito daga daki ta tsayamun aka cikin masifa tafaramun magana, "sulaiman yanaganka anan kazauna, wato bazakaje kasamomun abunda zanciba, mekake nufine, sedai inyi tazama da yunwa ta takasheni" janye tagumin danayi, nayi cikin rarrashi nafara mata magana da fadin, "dan Allah atika kiyi hakuri, kinga yanzu dare yayi bansan inda zannufa insamo miki abunda zakiciba,amma kibari zuwa safiya insha Allahu zannemi koda wankaune domin inbaki abunda zakici" rike kugu atika tayi tace, "wlh baka isaba sulaiman yau bazaka kwana agidannanba seka nemomun abunda zanci, danbazan zauna yunwa tamun lahani abanzaba" cikin takaicin halin atika na rashin tausayi nace, "haba atika amma kinsan nima babuce Allah yadoromun lokacin da ina dashi aina baki abincin" "kaga sulaiman nifa babu ruwana da wani babunka nidai kawai kanemomun abunda zanci, tunda kai kakawoni nan ka'ajiyeni danhaka dole kasamarmin abunda zanci, dankasan shi ciki besan wani babuba ehe" bancemata komaiba namike nafice daga gidan, lokacin goman darema ta kusa. Duk inda nasan zanje insamo wa atika koda biscuit ne amma naje bansamoba, haka nadawo gida jikina asabule lokacin dare yafarayi dan 12 saura, atika harta rufe gida, kwankwasamata nayi ta bude, koda taga hannuna babu komai seta maida kofar gidan tarufe tana fadin wlh bazan shigoba matukar bansamo mata abunda zataciba. wani bakin cikine yaziyarceni nida gidana amma ahanani shiga, meyasa atika bata tausayinane nimafa yunwarnan nakeji amma tunsafe nake yawon nema mata abunda zataji amma bata gani. Wata shawara zuciyata tabani akan naje unguwar masu kudi mana, inrokesu su sanmun koda danyen abincine inkawowa atika tadafa, ko tunanin dare banyiba nakama hanya natafi dukda nisan dake tsakaninmu dasu. ina tafe nakadai tunkis tunkis harna shigo wata unguwa dako sunanta bansaniba amma dai ta masu kudice, kowanne layima da gate dinsa kuma duk an rurrufesu,tsayawa nayi ajikin wata bishiya ina maida numfashin wahala, tunaninma tayanda zan iya komawa gida nakeyi dannagaji likis ga kishirwa dake damuna. ahankali nafarajin taku daga bayana alamar ana gudu, cikin tsoro najuya ina karanta addu'a acikin raina, mutum na hanyo yana gudu da dukkan karfinsa, seda ya matso kusa naga Ashe macece goye da yaro hannunta kuma dauke da wata jaka. Cike da mamaki da tsoro nake kallonta kamar yadda itama ta tsaya cak tana kallona. Cikin karfi hali nace, "baiwar Allah mutum ko aljan?" Cikin hausarta dabata fita sosai tana haki tacemun. "bawan Allah mutum ce ni kamarka" bata jira mezancemataba ta hau kici_kicin kunce dan bayanta bayan ta ajiye jakar hannunta akasa. niko tsayawa nayi kawai ina kallonta cike da mamakin meya fito da ita daga gida cikin darennan, gata yarinya karama danko atika batayiba gata fara jajur kyakkyawa da ita kana ganinta kaga cikakkiyar buzuw..... Katsemun tunani tayi ta hanyar mikomun jaririn hannunta tana kuka tana fadin, "bawan Allah, dan Allah kataimakeni kagudarmun da jaririnnannawa,wlh kashemunshi zasuyi,kuma yanzu suna dubawa basu ganniba zasu biyo bayanane, nikuma dasu kashemun dana gwara ni sukasheni shiya rayu, kataimakeni kagudarmun dashi shikadai Allah yabani, banaso narasashi,wlh dana dan halak ne da ubansa, shima babannasa sun kasheshi shine shima yanzu sukeson kasheshi" takarasa zancen tana fashewa da kuka, tsayawa nayi kawai ina kallonta zuciyata namun wasi_wasi akan abunda tace. "Kataimakeni, sunkusa karasowa, karikemun dana da amana dan Allah,kagudarmun dashi karsu karaso su kashemunshiiiiiiii!..............✍️

*By*
*zeey kumurya*
*ABUNDA KA SHUKA.........*
_*(shizaka girba)*_

*3️⃣6️⃣*

...........Tsayawa nayi kawai ina kallonta cikin kura ido, domin tabbatar da abunda take fada har cikin zuciyarta gaskiyane. Kasancewar gurin da wadatar hasken kwayayan gidan mutane ina ganin yanda hawaye yake zuba daga idanunta tamkar ankunna fanfo se shatata yakeyi. Cikin tsananin tausayawa nakai hannu nakarbi yaron daketa bacci abunsa, duk wannan uban gudun da mahaifiyarsa tasha amma be farkaba. "Suwaye zasu kashe miki danki, kuma akanme?" Na tambayeta ina kallonta bayan na karbi yaron. girgizamun kai tahauyi cikin kuka tace, "babu ishashshen lokaci dazan makama bayanin kosu suwaye,amma dai su mugayene azzalumai wadanda san duniyarsu yamantar dasu Allah, sun kashemun mijina, nima basu kyaleniba Neman rayuwata sukeyi data dana,duk akan abun duniya." wani numfashi taja tare da runtse idanunta tace, "kagudu karsu karaso,domin ni nasan duk inda nashigama agarinnan,sesun nemoni sunkasheni,kadauki wannan jakar zata taimakeka arayuwa" batajira amsataba ta bude idonta takurawa danta idanunta dasuke zubar hawaye, sumbatar goshinsa tayi gami dayin magana da yarensu cikin kuka me karya zuciyar mesaurare. Har cikin zuciyata nakejin kukan matarnan, tsabar tausayinta ita da danta nama kasa magana, se kwalla data cikamun idona. Ina shirin kara mata magana najiyo taku alamun ana tahowa inda muke, dasauri muka juya dukanmu nida matar daga inda ta bullo daganan takun yake tahowa, nikaina ba itaba bakaramin tsorata nayiba domin ga dukkan alamu wadanda take fadane suka biyo bayanta bisa ga yadda naga duk ta firgice. Rungume yaron nayi a kirjina da hannun haguna, hannun damana kuma na rarrafa nahaye kan bishiyar damuke tsaye akasanta, domin nanne kadai gurin dazan iya buya bazasu ganniba. cikin ikon Allah kuwa nahaye bishiyar tamkar dan biri ina maida numfashi, ninama manta da jakar datacemun indauka seda naga tadauketa ta ziramun acikin wani kurmin bishiyar. Sannan ta ruga da gudu ta miki wata hanya, ko minti 4 bata cika da tafiyaba wasu mutane guda hudu suka karaso gurin, hannayensu dauke da fitilu hanyar da matar tabi nan suka mika suma da gudu, naji sunyi magana cikin yarensu na buzaye amma banfahimci mesukaceba ga dukkan alamudai hango matar sukayi.

wata nannauyar ajiyar zuciya nasauke bayan sunbar gurin,wani matsanancin tausayin matarne yakamani,lallai mahaifiya, mahaifiyace tazabi danta yarayu ahannun wanda bata saniba,batasan daga inda yakeba akan akashemata shi, tazabi ita tarasa rayuwarta danta yarayu. wasu zafafan hawayene suka shiga kwaranyomun inajin dama zan iya danaje nataimaki matarnan daga hannun azzaluman mutanen data ambata. rokon Allah nashigayi akan Allah ya kubutar da ita, insha Allahu bazasu samu nasara akantaba. Nakai kusan minti talatin akan bishiyarnan ina sakawa da kwancewa sannan nadiro jikina asanyaye. Jakar data ajiyemun nadauka senaji jakar da nauyi,mamakine yakamani ganin yanda matarnan ta iya gudu da ita ga kuma goyon yaro abayanta, kodayake gudun ceton rai bazataji nauyin komaiba. Goyo yaron nayi abayana nadauki jakar naruga da gudu zuwa gida, domin nima a matukar tsorace nake, gani nake kamar mutanennan zasu iya dawowa su riskeni. yunwa da gajiyar danakeji ada gabadaya yanzu sunbar jikina,burina kawai inganni acikin gidana na tseratarwa da matarnan da danta.

Cikin ikon Allah, nakarasa gida lafiya alokacin tsakiyar darene gari yayi shiru, se haushin karnuka da kukan tsuntsaye. Nadade ina kwankwasa kofa kafin atika tazo tabudemun kofar. nasan bacci tafara, aiko ko tsayawa batayiba ta juya takoma dakinta, ni dadin hakanma naji,danbansan yanda zamu kareba idan taga yaron bayana. Dakina nashiga na kunce yaron nashimfideshi akan tabarmar dake dakin bayan na kunna light haske ya gauraye dakin. kurawa yaron ido nayi cikin tsananin tausayinsa, gashi kyakkyawa dashi fari kal harwani pink_pink yake tsabar fari. hannuna nakai nashafa kwantacciyar sumar kansa baka sidik, so da kaunar yaron nashiga cikin raina afili na furta. "Ya Allah, karaya wannan bawannaka, kabani abunda zan iya rikeshi,kakuma bani ikon rikeshi bisa amana batare dana cutar dashiba" badon nagaji da kallonsaba na mike nabude wata tsohuwar jakata danake ajiye abubuwa nasaka jakar da matarnan tabani aciki na mayar na zuge na ajiye. kamar ance injuyo naga yaronnan ya bude idonsa yana wawure_wawure da hannunsa yana kaiwa baki dasauri nanufeshi nadaukeshi, aikuwa yabude baki yacanyara kuka, jijjigashi nahauyi cikin son yayi shiru amma ina tamkar kara zugashi nayi se ihu yake da dukkan karfinsa abun tausayi. Se'alokacin nayi tunanin watakila yunwace take damunsa,nanfa hankalina idan yayi dubu yatashi domin banda abunda zanbashi acikin gidannan. Yana hannuna nafita dashi domin nabashi ruwa ko Allah zesa yayi shiru kafin safiya nanemo abunda zanbasa. Atsakar gidan nayi kicibus da atika tafito a hargitse. Gabanane yayanke yafadi danbansan yanda atika zata dauki maganar yaronnanba, tsayawa tayi cak tana kallona cike da tsananin mamaki kafin naji ta lailayo wani uban ashar gami dacewa, "sulaiman mezan gani haka, jariri ahannunaka ina kasamoshi, ina cikin baccina naji kukan yaro yacikamun kunne kamar amafarki, shine nafito inleka waje inga tsinannen yaro daya hanani bacci, kuma se'inganshi acikin gidana" bance mata komaiba harna debo ruwan akofi nazauna nakafawa yaron abaki, nandanan kuwa yakama wawurar kofin da baki abun tausayi yahau kukkutar ruwan, sedayasha kusan rabin kofin sannan nacire kofin daga bakinsa kuka yasaka alamun ruwan be'isheshiba. kara mayarmasa nayi yakarasha, atikadai tana tsaye tana kallon ikon Allah.
Chapter 49 · 0% Book details