Sashe 51
Abin Da Ka Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
..........Gwalagwalaine a duddunk'ule tamkar duwatsu se daukar ido da kyalli gami da walwali sukeyi. jikina na rawa nasaka hannu nadakko curi daya ina dubawa dannakara tabbatarwa. dan gani nake tamkar idonane kemun gizo,babu tantama gwalagwalaine acikin jakarnan. ahankali nadago ina kallon mustapha dake kwance yana bacci, ina tunanin wanne irin kudine da mahaifiyarsa haka dahar tabani wannan irin kayan dukiya haka, kamar kuma antsikareni sena mike dasauri nafice ina kwadawa atika kira domin tazo tatayani ganin abunda nagani ko idonane yake mun gizo. "Lafiya sulaiman kake kwadamun irin wannan kira haka sekace sabon makaho?" cewar atika tana yamutsa fuska. cikin rudu nace mata, "atika abun mamaki nagani, kema zokiga abunda nagani" banjira amsartaba najuya nakoma dakina tana biye dani abaya, da hannu nanuna mata jakar batare danace mata komaiba. tsugunnawa tayi tadakko *gold* din daya ahannunta tana dubawa. Zaro ido atika tayi waje cikin gigita tace, "sulaiman wannan ai gold ne ina kasamo su,waya baka,ko satowa kayi?" banbata amsaba se zama danayi agefenta ina kara fito da sauran ina dubawa. kara tambayata atika tayi akaro nabiyu da fadin"sulaiman tambayarkafa nake kamun shuru,kuma kana jina". Cikin daukewar tunani daga kwanyata nace mata. "Ranar da mahaifiyar mustapha ta bani shi aranar tabani acikin wannan jakar, ninama manta da ita seyau ina duba kaya naganta shine na dakko naga menene aciki senaga wannan abun nida farkoma nadauka nine bangani daidaiba,shiyasa nakiraki kitayani gan...." gani kawai nayi atika ta washe baki tatashi ta rangada guda gami da juyi tana rawa tana waka cikin tsananin farin ciki,batare data bari nakarasa zancenaba. sakin baki nayi kawai ina kallon ikon Allah. Surar mustapha tayi daketa baccinsa tahau yimasa rawa tana fadin. "Yaro ashe da arzikinka kake tafe, Ashe ta sanadinka mafarkina zecika inzama matar attajiri,kai amma Allah yayiwa mahaifiyarka albarka, nikam tagamamun komai arayuwata databawa sulaiman wannan irin dukiya metarin yawa" cikin tsananin mamaki nake dubanta baki bude, dakyar nayi dauriyar cemata, "atika mekikeyi hakane?" Bata kulaniba secigaba da juyi da mustapha datayi, aiko mustapha yace besan zanceba, yaji ana wujijjigashi tuni yafarka da kukansa. zama tayi tana lallashinsa abunda atika bata taba yimasaba tunda nakawoshi gidan. seda yayi shiru ta dubeni tace, "yanzu sulaiman semu dawo da tafiyarmu gida nankusa muje musaida wadannanan gwalagwalan muwataya mu fancakala muyi wadaka da dukiyar datazo mana, tsuntsu daga sama gashashshe" kallon mahaukaciya nayiwa atika sannan nace mata, "haba atika yadaga ganin dukiya hankalinki yabar jikinki gabadaya duk kinbi kin burkice, wannan dukiyar dakike gani bazan taba komai daga cikintaba, dukiyar marayan Allah ce, zan ajiye masa harzuwa sanda ze girma ya juya abarsa,kuma ni bana cire ran bazankara ganin mahaifiyar mustapha ba, ko wani nata, lokaci kawai nake jira dazannemomasa danginsa insha Allahu, kinga kuwa dazarar munhadu dole nabasu dansu da dukiyarsa" gabadaya fara'ar dake fuskar atika daukewa tayi hartana kokarin yarda mustapha dake kan cinyarta. Cikin takaici tace, "lallaikuwa sulaiman daka cika me bakin hali, mu raini yaron sannan kuma kace bazamuci dukiyarsaba salon inya girman yajuya mana baya, bayan mungama cin wahalarsa,wlh baka isaba abunda bazeyiyuba kenan,aka'idama wannan dukiyar tazama tamu tunda yanzu mune uwarsa mune ubansa,mune shansa da suturarsa"