← Book details Yar Karuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 58

Sashe 4

Yar Karuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ina gama wanka na ɗaura alwala sannan na fito, ko mai ban shafa ba balle wani abun, humran da Mami ke sayamun kawai na shafa a inda ya kamata na sassan jikina, sannan na buɗe drawern kayana na ciro simple material riga da wando da mayafin sa wanda ɗinkin ke kama da Pakistan-dress, ina saka wa na ɗau hijab na tada sallahn magrib, ina idarwa na ɗauki Qur'ani na fara karatu, nice ban tashi akan darduman ba har sai da nayi sallahn isha'i na tabbatar hadda na ya zauna, sannan na naɗe na ajiye sa, da hijab ɗin jikina na fito palourn namu, amma mutumin da na gani zaune a palourn namu shi ya sanya ni juyawa da sauri wanda kamun ace na ƙarisa shigewa ɗaki Mami na da fitowan ta kenan ta ganni ta qwalamun ƙira, kuma ƙiran nata ne ya tsayar da ni, ban shige ɗaki ba kuma ban juyo ba ina dai tsaye a wajan cikin taƙaici da haushin mutumin da ya zo wajan Mamina.

Mami na kyakkyawa ce ta gasken-gaske, farar mace ce mai ƙaramin ruwa dan in ka ganta ba zaka ce ta haife ni ba, tana da dogon hanci da tsayin gashi wanda hakan ke sanya wasu mutanen mata kallon bafulatana, sannan tana da kyakkyawan ƙira, wanda har zuwa wannan lokacin da nima na zama budurwa amma ƙirjinta basu kwanta ba ko dan ni kaɗai ta shayar ne oho, kuma Mamina tana gyaran jikinta sosai, sannan tana da ƙugu wanda ke ɗaukan hankalin mutane dan nima a wajan ta na gado ƙugun da mazaunai, wasu in suka ganni ma har cewa suke nima na biyewa Uwata na fara bin maza dan kusan kallon da mutane ke mini kenan akan nima nasan maza na buɗe.

Jin muryan Mamina ta ƙara ƙiran sunana a karo na biyu, kuma nasan palourn take so na dawo, tura baki nayi dan kuwa na tsani wannan mutumin da ke zaune a palourn namu, saboda duk cikin masu zuwa wajan ta a manyan mutane shi yake ban haushi ganin babban mutum kaman sa ga kuɗi ga kyau amma yake biyewa bin mata dan na tabbata yana da yaron da zai kusa sa'an Mami na dan daga ganinsa ya bai wa shekaru hamsin 50 baya, saboda babban mutum ne sosai kyakkyawa har da furfuransa.

Wannan karon inajin muryan Mami na Juyo, cikin nistuwa nake tafiya kaman bana so, a haka na ƙariso cikin palourn fiskana a haɗe, sam-sam babu annuri ko kaɗan, kallon da Mamina ta jefo mini shi ya sanya ni tura baki ciki-ciki na ce, "Anwuni lafiya Alhaji?"

Alhaji mukhtar washe baki yayi dan sosai yake ƙaunar mahaifiyata, wanda wannan soyayyan da yake mata shi ya sanya nima yake ƙaunata tamkar ƴar cikin sa, kayayyaki ne menene duk idan ya tashi zuwa sai ya kawo min, kwanaki har ya sayamun waya babba mai kuɗi, amma kuma Mamina ta maida masa ta ce ba zan riƙe waya tun yanzu ba.

Amsa gaisuwan yayi yana ta saka mini albarka, amma ni fiska na ko Annuri babu balle batun amsa albarkan da yake sanya min, na tashi zan koma ciki sai ya tsayar da ni ta hanyar cewa "yarinyata Banafsha ga tsaraban ki taho ki amsa."

Cikin taqaici na juyo, ji nake kaman na shaƙesa ya mutu na huta, durƙusawa nayi na miƙa hannayena bibbiyu na karɓa abinda yake miƙa mini, na ce masa, "Nagode Alhaji, Allah ya ƙara arziƙi da ɗaukaka."

Yana murmushi da jin daÉ—in addu'a ta gare sa kullum, dan muddin zai min kyauta to ni kuma sai na suburbuÉ—o masa addu'a ko ban yi niya ba, cewa yayi, "Ameen ya Rabbi! yarinyar kirki Allah ya miki albarka ya albarkaci karatun ki ya baki miji na gari."

Amsa wannan addu'a sai Mami na ne tayi shi cikin fara'a dan tana ƙaunar mai ƙaunar gudan jininta, yarinyar ta gudan ɗaya tal kaman stoka a cikin miya, ni kuwa tuni na jima da shigewa ɗakina inda nayi jifa da ɗan ƙaramin jakan, dan abun hannunsa ba ya burgeni.

"Subhanallahi!" shi ne abinda baki na ya furta ganin wani haɗaɗɗen Qur'ani ɗan dai-dai ya faɗo ga carbin irge(counter), ga kuma sallaya ɗan ƙarami, ga kuma ruwan zam-zam duka suka faɗo daga cikin jakan.

Da sauri na sunkuya ina tattara su, wanda bansan lokacin da murmushi ya kuɓuce mini ba, dan a rayuwata sosai nake ƙaunar ganin anmin kyautan Qur'ani ko sallaya, nan na dinga tsalle da murna, inata jero masa addu'an Allah ya shirya shi yasa yabar bin mata, Mamina ma Allah shiryamun ita, tuni na mance da haushinsa da nake ji, na kama murna ina jiran Allah ya kai mu gobe na nunawa Umaima.

Ni da na shigo ɗaki da niyan bacci, amma ganin wannan kyauta bansan lokacin da na miƙe na ɗauro alwala na tada nafila ba, ina mai kai kuka na ga Allah na roƙawa waɗan nan bayin nasa shiriya.

Ɓangaren su Mamina, ina barin palourn ta dubi Alhaji Mukhtar da murmushi ta ce, "Mun gode sosai Alhaji, Allah ya saka da alheri, ya kuma ƙara arziƙi yawa zuri'a albarka."

Alhaji Mukhtar murmushi yayi ya ce, "Ameen summa ameen, Hajiya ta Amarya ta."

Hararansa Mami tayi ta ce, "Za ka fara ko? To Alhaji bana son wannan magana kabar kawo mini shi."

Cikin mamakin lamarin Mami ya kalleta ya c,e "Ramlatu wai me yasa kullum in nace miki ba lafiya a lamarin ki akwai wani abun sai ki musa min ki ce ba haka ba? Mutumin da yake lafiya ƙalau zai zaɓi irin rayuwar nan? In aka miki maganan aure kaman an kashe miki wani naki wai meyasa? Ramlatu ki sani ina sonki sonda ban taɓa yiwa wata ɗiya mace ba, amma dai ba komai zan barwa Allah duk wani lamari na ya iya min, ki sani kuma in anyi duniya dan Manzon Allah SAW, sai na aure ki dan na gaji da wannan rayuwa da muke yi mara fa'ida, da girmanmu da komai ga yara amma mu dinga saɓawa Allah bama tunanin abinda muke yi bashi ne, kuma za'a yi da yaranmu, wallahil Azeem Ramlatu dan ke naje Makka wannan karon dan duka addu'ata akan ki nayo sa, ina mai sa rai da fatan Allah ya amsa mini ya saita lamuranki, Insha Allahu wata shekara kema za kije dan ki ƙaro addu'an wa kanki, ni dai buri na na aureki muyi komai a inuwar sunna da lada, wannan ƙazamiyar rayuwan ta isheni."

Mami da zuwa yanzu ta cika tayi fam kaman za ta fashe cikin ɗaga murya ta ce, "Alhaji Mukhtar ina ganin girmanka da darajanka, ko ba komai dan soyayyan da kake nunawa yarinyata wacce ta fi mini komai a rayuwa to shi yasa nake shiru nake cigaba da sauraranka, amma karka yarda ka fara tunanin wuce gona da iri, ko an gaya maka bansan duk abinda kake aikata min ba ne? Bansan mai kake shiryamun ba akan jama'a na? To ka riƙe girmanka, idan ba haka ba na kusa daina sauraranka, maganan aure ka aje sa a gefe, nayi aure na gama yi haka nake son rayuwata in ba za ka iya ba ka fita a rayuwata ka ƙyale ni, ai akwai mata da yawa a duniya, to kaje wani wajan ka nemi ta aure, ni ba aure ne a gabana ba."

Alhaji dai kallon Mami yake kuma ba alaman ɓacin rai a fiskansa sai ma wani sihirtaccen murmushi da yake sakar mata, ga kuma fara'a wanda ako da yaushe in suka samu saɓani irin haka akan ya mata maganan aure tana bam-bami, to iya abinda yake yi kenan murmushi.
Ajiyan zuciya ya sauƙe ya ce, "Allah ya huci zuciyanki Hajiyata kuma amaryata, in Allah ya so ya yarda."

Cikin jin haushi Mami ta miƙe ta shige ɗakinta tare da banko ƙofa har da saka key, shi kuwa ganin haka sai yayi hamdala dan hakan yake so dama.
Tashuwa yayi ya shiga ɗaya ɗakin ya wasta ruwa ya ɗauro alwala yayi nafilfilu yana mai ƙara miƙa kukansa ga Allah akan wannan baiwar Allah da yake matuƙar ƙauna, yana idar wa ya kashe wutan ɗakin ya kwanta.

Washe gari da ya kama juma'a da sassafe na fito nayi shara da wanke-wanke da girki sharp-sharp, ina kammalawa na É—iba nawa naci na koma É—aki na shirya dan zuwa makaranta.
A bakin ƙofan ɗakin Mami na tsaya ina sallama, daga ciki Mami ta amsa mun ta ce na shigo, tura ƙofan nayi na shiga, na tarar da ita zaune a bakin gadonta, Alhaji kuma yana zaune akan kujeran zaman mutum biyu dake cikin ɗakin.

Durƙusawa nayi na gaishe da Alhaji, ina ƙara masa godiya sannan na gaishe da Mamina, ta amsa tana tambayan har na shirya kenan na ce mata, "Eh Mami na shirya class na 7:30 muke da."

Mamina ta ce, "To Banafsha Allah ba da sa'a, a dawo lafiya, ba dai akwai kuÉ—in mashine a hannunki ba?"

ÆŠaga kai kawai nayi na juya zan fice a dakin sai naji muryan Alhaji na cewa, "Daughter tsaya na ajiye ki a makarantar ko."

Kaman an bani saƙon mutuwa haka naji amma ba yanda na iya haka na fice na tsaya jiransa a qofan gidan mu.
Sallama Alhaji yawa Mami akan zai tafi kuma zai fi sati bai zo ba ta kula sosai sannan baison yawan kule-kulen mutane.

Kallon sa Mami tayi tana murmushi ta ce, "Alhaji kana son jan magana, kai ba mijina ba, ba komai ba kana bani doka to gaskiya sai dai kayi haƙuri dan yanda ka ganni ka biyo haka kowa ma, shiyasa na faɗa maka tun farko, ni dadiro ba shi ne abinda ya dame ni ba, kowa ya samu rabonsa yayi gaba."

Alhaji kaman zai yi kuka ya ce, "Ramla kibar faÉ—amun irin maganan nan kin dai sani tsakanina da ke daban da tsakaninki da sauran ko? Kuma idan maganan ban aure ki kike ba mai kike ci na baka na zuba? Ai in Allah ya yarda Mukhtar sai ya mallaki Ramla ba da jimawa ba, Allah raba mu da zaman dadironcin ma."
Chapter 4 · 0% Book details