← Book details Wata Kishiya Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 107

Sashe 95

Wata Kishiya Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alnustapha Yace "bata gaya mana ba..." "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!'' Jimmalo ta fadi yayinda kanta ya buga,, ta fice a gets din gidan cikin hanzari take tafiya ko zata ganta. "Allah yasa ba guduwa tayi ba..."jimmalo ta fadi hankalinta a tsananin tashe, tinda Almuqri'ah tazo gidan tanada tabbacin bata taba fita ba se yau, to tabbas yau din data fito tasan da wuya in ba guduwa tayi a gidan ba. "To ina taje? Gunwa zataje da tsohon cikin jikinta na megida?'' Jimmalo ke fadi a bayyane kmr zararriya, tazama kamar mahaukaciya, tunanin Abdoljalal kawai ya fado mata rai. Har wuraren 6:pm jimmalo nata yawo a gari a kafa, tafi gabas, ta dawo tabi yamma, tabi kudu, tabi arewa Amma sam bataga Almuqri'ah ba ko me kama da ita ma bata gani ba..se bayan isha'i jimmalo ta dawo gidan securities suka bita da ido. Direct jimmalo dakin Almuqri'ah ta nufa dan ganin kota dawo amma taga bata dawo ba. Cikin tashin hnklim dabaze misaltuba jimmalo takoma dakinta taci gaba da kiran kande amma shiru waya bata shiga. Jimmalo ta fashe da kuka me kunar da zuciya, yau ko ruwa batasa a cikintaba , batajin zata iyashan ko ruwan ne a cikinta,. Ranar sam kasa bacci jimmalo tayi, ta rasa waxata kira ta gayawa damuwarta, lmbr kande bata har zuwa yanzu, ta kirata yafi 1m amma shiru. *A asibiti* Kwana doctors sukayi da wuni a kan hajiya saude amma sam taki dawowa hayyacinsa,, likitoci ma sun fara cire rai dazata dawo hayyacin nata, Abdoljalal ya shiga tashin hankalin dabe taba shigarsa ba,babban tashin hankalinsa besan a wani hali Almuqri'ah take ciki ba, taci ko tasha, besani ba, shifa dmwar ciwon saude kadan ne a ransa, yanaso yabar asibitin yaje yaga Almuqri'ah dinsa da babyn cikinta dayayi kewarsu amma ba hali saboda baze yu ya bar asibitin ba dole se an tabbatar daya sauden ta kasance, ko tunanin shan ruwa Abdoljalal bayayi dukda yanajin kishi amma sam be damu da hakan ba, gashi ko waya bezo da ita ba balle ya kira yarinyar yaji dadih,. tin a daren ranar dasukaxo asibitin yayi wankan tsarki a toilet din dr umar Abokinsa ne tare sukayi scul, sanadin kawo saude asibitin yaga dr umar din, Ahamad ya dakko masa jallabiya blue a motar Abdoljalal din ya cansa, dmn baya rasa kayayyaki a motarsa. Abdoljalal ya gaji da kewar Almuqri'ah ya amshi wayar ahamad ya kirata amma bata daga ba, seda ya mata kira goma amma bata dauka ba, nan hankalinsa ya kara karkata zuwa gida, amma dole ya jure aga abinda hali zeyi a kan Saude, kaf 2days din da Abdoljalal da yayi a asibitin ko ruwa besha wa cikinsa ba yana tafiya iska na neman daukarsa, ahamad yayi-yayi yasha ko ruwan ne amma sam Abdoljalal besha ba, dmwarsa dayace Almuqri'ah, zuciyarsa na yawan bugawa a kanta,ji yakeyi santa na karuwa a zuciyarsa, yayi kewarta tmkar yayi 10yrs begantaba. Da kyar doctors suka samu kan hajiya saude bayan sunyi 3days a kanta, se cikin dare 2:am suka samu tadawo hayyacinta, suka mata Allurori aka bata daki, tare dasa mata drib. Da Asubahi Abdoljalal nayin sallar asubahi yayi lazimi a daddafe 6;am ya nufo gidansa ya bar Ahamad nan asibitin. se Allah-Allah Abdoljalal yakeyi ya isa gidansa domin ya ga Almuqri'ah d'an cikinsa, zuciyarsa na yawan bugu a kanta. Yana isa gidan yayi packing a tsakiyar gidan ko packing space bayajin ze iya isa saboda ya kagara yaganta. Ya fito ma'aikatan gidan se miko masa gaisuwa sukeyi ko amsasu beyi ba hankali da duk tunaninsa yana kan Almuqri'ah da bebynsa. Direct ya nufa dakin Almuqri'ah, securities dasuke kallanshi ko wannensu seda hankalinsa ya kara tashi, saboda sun san yau zasuci bura ubarsu daman tin tini suke cikin fargaba mara misaltuwa, su basusha cewa Almuqri'ah bazata dawo ba sunsha zataje ta dawo ne, shiyasa suka barta ta fita ba musu,suna tsoron dktr da ita sbda suna bata girma,, gabako daya de a lokacin basusan meya shiga kansu Ba suka barta ta fita. Da sallama ya shiga dakin. , idanuwansa suka sauka a kan gadonsu, yaganshi kace kace ba gyara,, nan take yaji jikinsa ya masa wani iri,zuciyarta tayi ba ddh, dayaga bata dakin seyasha tana toilet ne dan haka ya nufa toilet din ya Ganshi a rufe yashiga toilet din hadi da kwalo mata kira amma shiru, se yasha ko tana farfajiyarsa tashan iska, dan haka ya nufa can , yana kwalo mata kira, securities na kallansa duk suka sha jinin jikinsu dacewar yau zasuci durin uwarsu, tin tini basu shiga damuwa ba se yanzu. Jikin Abdoljalal har yana rawa ya isa farfajiyarsa tashan iska be gantaba. "To ko tana dakin wannan yarinyar .." Wato jimmalo yake nufi. dan haka ya juyo ya nufa part din ma'aikatan mata. da larai yaci karo, be taba zuwa part din masu aiki ba se yau,. sam larai batayi mamakin ganinsa a part dinsu ba, domin zuwa yanzu kaf ma'aikatan gidan mata sun san Almuqri'ah ta gudu a gidan,sun san komi dake gudana a gidan, amma suna nuna kmr basu sani ba, larai dake kawo musu labari ita ke daurasu a darasin su nuna kmr basu san meke faruwa ba a gidan,kaf komi sun sani, harda sanadin kai saude asibiti sun sani sude fatansu kada saude tadawo gidan domin inta dawo seta ci bura ubar kowa na gidan.. Da larai tasamu labarin Almuqri'ah ta gudu a gidan a gurin salisu tantiri taji, seda ta rabgada gudar farin ciki daman ita ta tsani yarinyar saboda san da saraki kemata da kuma daukakar da Allah yama yarinyar daga zuwanta gidan a gun saraki tinda gata da cikinsa ai tasamu daukaka. Tsugunnawa larai tayi ta gaida Abdoljalal hadi da tambayarsa ya jikin hajiya saude... Ba tareda Abdoljalal ya amsataba yace "kiramin wannan yarinyar, yasunanta ne wadda kuke aiki tare, me jikinnan..." Larai tace "Jimmalo..." "Kiramin ita yi sauri, in Almuqri'ah na dakin ki kirawomin ita seki bar ita waccan yarinyar..." Cewar jalalu. Larai tace toh hadi da mikewa ta nufi dakin jimmalo se murmushi larai takeyi a zuciya da zahiri. "Insha Allahu kaida ganin wannan me sunan larabawar har abadan, tanacan kilama ta afka gidan yankan kai..."larai tayi maganar a zuciyarta. A kofar dakin Jimmalo larai taga jimmalon ta kalleta taga idanuwainta sunyi luhu luhu tayi kuka tagaji. Larai ta tabe baki tace "ohh aiki yasamu gwari...aise ki tashi kije oga na kira.." Jimmalo taji gabanta ya yanke ya fadi jin abinda larai tace a karshe, ta mike tsaye hadi da gyara zaninta wanda ke kokarin kubce mata, tashin hankalin datake ciki baze misaltuba, ko sadda ubanta ya mutu bata shiga tashin hankalin datake ciki ba a halin yanzu, tin tana ganin yarinyar zata dawo yanzu ta cire raima da yarinyar zata dawo gidan yau kimanin 2days kenan bata gidan, jimmalo kullum kwana da wuni takeyi tana kuka, tunaninta daya ne ina yarinyar taje?'' Ta tabbatar in Abdoljalal yaji bata gidan tsawon 2days seya fi jimmalo damuwa "wane itama...." A jere jimmalo da larai suka iso inda Abdoljalal yake, jalalu yabisu da ido yaga bega Almuqri'ah ba sede jimmalon, kallo daya ya mata yagane bata cikin hayya cinta kmr yadda shima baya cikin hayyacin nasa lips dinsa duk yabi ya bushe rakayau se faman jikashi yakeyi da yawon bakinsa.. "Ina Almuqri'ah na?'' Abdoljalal yayi tmbyr idanuwansa na kan jimmalo, larai taji kmr ta kashe knta dayace Almuqri'ah na. Jimmalo kam gabantane ya yanke ya fadi, ta daburce ta rasama mezatace masa, kawai se yaga hawaye sharr a idanuwan ta..hakan ya bala'in jefa Abdoljalal a tsananin tashin hankali mara misaltuwa , ya tabbar da akwai babbar matsala.."nace ina Almuqri'ah da d'an cikina? Ina take? Ina d'an cikina? Kiyimin magana, ina cikina danayi mata? Ina cikina dake jikinta?!!!'' Abdoljalal yayi mata tambayoyinnan cikin tsawar data kada hantar cikin jimmalo ta kalleshi tayi kasa da kanta, duk yabi ya haukace, a hakama dan beji komi ba kenan. "Ina take nace?!!!! Ina cikina?!!!!" Abdoljalal ya kara tmbya cikin tsananin tsawar da har securities seda sukaji, dukkaninsu suka hada baki gun cewa "Anxo wajen..." Kaf jikinsu ya dauki rawa, suka kira masu gadin get din tsakiya dana farko duk suka dawo cikin gida sukayi tsuru tsuru, tini wasunsu sun fara zawo. "Ta gudu,tin washe garin ranar dakuka je asibiti, na nemeta bangantaba wlhi..." Jimmalo ta fadi cikin kuka, ta zube kasan guiwowinta hadi da kara rushewa da kukan tashin hankli me tambarin matsifa da bala'in dake tattare da ita ko kwatan Abdoljalal bata kaiba. Larai de na gefe. Jin abinda jimmalo tace yasa kunnuwan Abdoljalal daukewa na wasu dakiku, idanuwansa suka lumshe da yana, yaji wani luuuu kmr ze fadi, se kuma ya rike jikinsa sbda shi namijin duniya be yayan namijim zaki ne,sam ba a ganin tashin hnklinsa duka, dan hk yanzuma rabi aka gani a zahiri. "Banji me kikace ba? Ta gudu? Ita wa ta gudu? Almuqri'ah ta gudu? Ta ina tabi ta gudu? Ina taje? Ina cikina na jikinta??'' abdoljalal yayi maganganun kamar ze haukace saboda rudu da gigita, idanuwansa se lumshewa sukeyi yana kara budesu, tashin hnklinsa baze misaltuba har abadan, kai kace cewa akayi masa Almuqri'ah din ta mutu. Jimmalo ta kasa amsa masa tambayoyinsa se faman rusar kuka takeyi. Larai tayi carab tace "ta gudu ranka ya dade, wallahi ta gudu yarinyar nan, ta bakin get tabi ta gudu, suma kansu securities basu san guduwa zatayiba suka barta ta fita , ..." "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!!'' Abdoljalal ya maimaita 3ryms hadi da dafe kansa,, idanuwansa suka kara lumshewa. "Ta gudun min da ciki? Ina tajemin da cikina? Ku fada mata ta dawo ta bani cikina dan Allah...innalilla hi wa'inna ilaihirraju'un!!''' Abdoljalal ya fadi kmr saban hauka so yakeyi yayi kuka amma ya kasa, tashin hankali mara misaltuwa ya shiga, zuciyarsa tashiga, fuskarta ta bayyana Dmwar zuciyarsa,. Larai tayi lakur, tana hango bala'in dake tattare ga Abdoljalal. Jimmalo kam se kuka takeyi. "Karya kuke min bata gudun min da ciki ba wlhi,,, se kun nemomin ita tabani cikina wlhi..." Ya fadi yana girgiza kai, ji yakeyi kmr a mafarki yake,. ya juya cikin hanzari ya nufo bakin get securities na ganinsa sukayi kasa da kansu, dmwa da tashin hankalin dake kan face dinsa basu taba ganin makamancinsa ba a tattare dashi se yau. "Da gaske ne Almuqri'ah
Chapter 95 · 0% Book details