Sashe 58
Wata Kishiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
sona ina baki dadih kou?shiyasa kika dena tsoronta..'' Al-muqri'ah tace "Dadin me?'' Da bebanci. Abdoljalal yace "Dadina mana, gashi nasha miki nonuwa, na mammatsa miki duwawuka..." Al-muqri'ah tayi kasa da knta, Abdoljalal yayi murmushi hadi da bude robar ruwa yayi kasa da glass din motar ya wanke fuskarta, saboda hawayen da yayi dazu, ya goge fuskarsa da tissue al-muqri'ah na kallonsa ta ajiye memo din data gama rubutunna ciki inda ta daukesa. Abdoljalal ya tada motar, suka nufa get din hotel din, Al-muqri'ah ta juyo ta kalleshi ganin ze shiga hotel din, ita tasha fa wasa yakeyi, Abdoljalal ya zuba mata ido shima, dai-dai yana hon a bakin get din hotel din.. Jikin Al-muqri'ah yayi laushi ganin an bude get ya danna motar cikin dankareren hotel din, zuciyarta tashiga dukan uku uku. Abdoljalal na kallan tsoro da firgice a kan fuskarta se dariya yakeyi a kasan zuciya, amma bece mata komi ba, ya isa packing space din hotel din yayi packing ya juyo ya kalleta dai-dai wayarsa tayi ringin ya dauki wayar ba tare dayayi picking call din ba. al-muqri'ah ta kuresa da ido zuciyarta se luguden tashin hankali takeyi, har zufa ke karyo mata dukda sanyin AC dake motar. Abdoljalal ya kara kureta da ido, zallar firgici ya kara bayyana a kan fuskarta, yayi murmushi hadi dacewa "Ina zuwa yanzu insha Allahu..." Ya bude yar jakarsa baka ya dauki wasu documents kana ya fice a motar zuwa cikin hotel din, Al-muqri'ah na kallonsa ta riga ta sadakar yau tata ta kare, kakarta ta taba gaya mata inde namiji yakai mace hotel to lalata mata gabanta zeyi, tashiga salatittika da sallallami a zuciyarta, da addu'ur'i. Befi mintuna goma sha biyar ba ya dawo cikin motar hannunsa rike da ledoji manya guda biyu, ya kalleta yaga duk ta jike da zufar tashin hankali, bayan kunne ya bar AC din motar. "Zufarnan duk ta mecece?'' Ya fadi yana mika mata ledojin daya shigo dasu, ta amsa still jikinta na rawa. Abdoljalal yayi yar dariya hadi da tada motar, yaja suka fice a hotel din. Tasaki nannauyar ajiyar zuciya bayan sun fice a hotel din., Abdoljalal dake ankare da ita yace "kinata wani zufa, knsha ko na kawoki hotel ne inci miki gindi ?'' Al-muqri'ah ta kalleshi tayi kasa da kanta, se yanzu ta dawo hayyacinta dasuka fice a hotel din. Abdoljalal yayi murmushin gefen kumatu, kana yace "Cool ur mine kyakyawata, ai ba a hotel zan ciki ba, malama kima kara kwantarda hankalinki na bada wasu takaddune... Kara natsar min da hankalinki bazan iya miki komi ba a hotel, a dakina zan miki duk abinda nakeso na miki saboda san da nake miki my love, kwata in ciki a inda zanyi alfahari dake..." Al-muqri'ah ta dago ta kalleshi, se kuma tayi kasa da kanta, tana mamakin wani irin Ci yake nufi sekace wata abinci. "Kici abincin dana siyo miki a restaurant din hotel din can, ci kiji in ba dadih se muje wani guri kici wani..." Cewar Abdoljalal. Al-muqri'ah tace "banjin yunwa..." Da bebanci. Abdoljalal yace "Aah kici nide so nakeyi ki kara gwabi gwabi kafin in tasaki gaba daci..." Al-muqri'ah ta kara dagowa ta kalleshi wai wani irin ci ne yake nufi oho. Ledar ta dakko ta duba taga white rise ce da soap wadda rabinta duk nama ne da vegetables, Se farfesun naman kaza, se drinks kusan kala hudu da ruwan gora, abincin ta dan tsakura tace masa shima yaci ta rage masa..." Abdoljalal yace "Aah ai inde ke knci shikenan,,,ni yanzu kin riga kin lalatani da abincinki, yafimin ko wanni abinci ddh..." Murmushin jin dadin yabon daya mata tayi. Direct office dinsa ya nufa da ita, ya kaita wani side wanda bame shiga seshi, ya fice zuwa office din nasa saboda yanada ayyuka dayawa. Nan ya barta tanata kallon kyaun tsaruwar side din nasa na hutu, an zuba masa komi na more rayuwa, ta rasa meyasa kwata kwata batajin tsoro a kan lamarinsa, harda karancin shekaru datake dashi. alwalar azahar tayi, ta tada sallah nan falon ta idar, nan ta kwanta tana kallon TV sanyin AC na ratsata, nan take tunanin kakarta ya fado mata rai, nan tashiga damuwa saboda batasan a wani hali take ciki ba zuwa yanzu, tana cike da kewar kakarta a kwanakinnan, har kwallah seda tayi saboda so takeyi kawai ta ganta, tana tunanin ne bacci yaxo yayi awan gaba da ita. Allah-Allah ya dingayi ya gama ayyuknsa 6;1pm ya nufo side din dake cikin kamfanin nasa , an tanaji bangaren ne dan hutunsa. Yana shigowa yaganta kwance kan kujerar 3ct har zuwa lokacin bacci taketayi, saboda baccin da bata samu sosai ba jiya, ko sallar la'asar bata san anyi ba. Karasowa yayi kanta ya tsaya ya tsura mata ido, ko a baccinma kyau takeyi bala'in kyau ma, ta gintse dan karamin bakinnan nata, kure dan bakin nata yayi da ido, a yadda take sauke numfashi ya bashi tabbacin ta jima tana baccin datakeyi, shi kansa yana mamakin yadda ta saki jiki dashi sam bata tsoro sosai a kansa. Yafi karfin 9mnt tsaye a knta, se lashe baki yakeyi kana ta farka saboda tsayuwar dayayi mata a kai, ta bude idanuwanta a kansa. "My beautiful angel..." Ya fadi yana kara kureta da ido. Mikewa tayi bakinta dauke da salati, ta kalli bangon dakin cikin hanzari ta mike ganin 6:11pm ta nufa toilet din falon ta dauro alwala nan da nan, ta dawo falon ya bita da ido yaga alwala ta dauro, shi yasha fitsari takeji dayaga ta wuce toilet a guje daga farkawarta daga bacci. Kan karfet ta hau ta tada sallah, Abdoljalal ya fahimci batai la'asar bane. "Kinsha bacci..." Ya fadi hadi da nufar bedroom dinsa, domin so yakeyi yayi wanka,. Wankan yayi ya chanza kaya domin yanada sabbin kayansa nasawa a nan. Fitowa yayi falon se zuba kamshi yakeyi, ta zuba masa ido, a kullum kara kyau yakeyi. "Tashi mu tafi gida ko mu kwana a nan kawai?'' Ya fadi hadi da karasowa ya zauna kusa da ita a kasan carpet,. Zumbur tayi ta tashi jin yace wai ko su kwana nan, itafa tsoron sake kebancewarsuma takeji har yanzu nonuwanta ciwo suke mata, sunma rure suna neman zamar mata gyambo, kawai daurewa takeyi. murmushi yayi , suka fice a side din, ya kulle side din, ya bude mata gaban mota tashiga, ya mayar ya kulle, shifa jinta yakeyi kamar sabon kwai me tsantsi. Zagayawa yayi ya shiga mazaunin dreva, Security din bakin get ya bude masa get ya fice da motarsa, ma'aikatan kamfanin nata mamakin ganin oga yau da mace, basu taba ganinsa da mace ba a duniya se yau, se wasu sukasha ko kanwarshi ce, wadanda suka sanshi sosai kuma sukace bade knwa ba, saboda beda kanwa, nan kamfaninsa ya kacame da tsegumi na zallar gulma, mutum daya biyu ne zuwa uku suka gansu sadda zasu isa side dinsa na hutu, a zuwansu kenan, wasu kuma suka gansu dasuka fito, su suka yadawa sauran ma'aikatan, aiko aka hau cece-ku-ce, (kunsan mutanenmu na yanzu basa hidimar gabansu, shegene keyi dame zina, mu kiyayi shiga abinda ba ruwanmu) Yana driving yana kallonta,, bame cewa wani kala, se kallonta kawai saraki keyi yana murmushi, ita kuma knta na kasa..seda suka tsaya a hanya yayi sallar magruba a wani masallaci, kana suka nufa wani babban dankareren Mall ya mata siye siyen kayayyaki na amfanin yau da kullum ga mace, aka kwaso masa kayan akasa masa a seat din baya, ya shigo ya kalleta, shi kadai ya shiga mall din, shifa yanzu kishinta yakeyi sosai. "Ana nan anata tsuke dan bakinnan kou?'' Ya fadi yana kure dan mitsilin bakinta da ido, gefe tayi da fuskarta ganin irin kallon da yake mata,, yayi murmushi inde yana tare da ita dadih yakeji a duniyarsa, wani haske ke lullubesa inde yana tare da ita. Tada motar yayi suka bar gurin, ya nufa inda ake saida kayan makulashe irinsu ice cream, yayi packing ya fito ya siyo mata abubuwa dayawa da kayan chocolates, dasu chocolate ice cream E.T.C. Ya dawo ya mika mata yace "ga ice creams da chocolates..." Al-muqri'ah ta amsa saboda tasan chocolate a rayuwarta, ta masa godiya, ya kalleta yace "Ki bar min godiya, kome fa kkci nima zanci a jikinki..." Kallonshi tayi ba tare data fahimta ba, ta bude daya daga ledojin daya miko mata ta fara cin chocolate din tanaci yana kallon dan bakinta me azabar kyau. Seda ya tsaya yayi isha'i a hanya. 8:30pm suka isa gida, a kofar kiching dinsa yayi packing saboda ba mutane a gun, ya firfito da kayayyakin dayase mata da kanshi ya kai mata side dinta, al-muqri'ah na tsaye tana kallon ikon Allah ya hanata daukar komi, harya gama kwashe kayayyakin ya kai mata side dinta, ya dawo tana tsaye a bakin kofar shiga kiching din side dinsa, ya iso inda take kmr ze wuceta se kuma ya rungumota jikinsa ya hadata da kofar shiga kiching dinsa,, sosai ya rungumeta ga jikinsa. "I love you, dake da kayan dadin jikinki..." Ya fada mata a saitin kunnenta yana sauke ajiyar zuciya. Al-muqri'ah tsoro ne ya kamata gudun kada wani yazo ya gansu haka a wannan yanayin, dan haka ta kwace kanta cikin hanzari, ta koma gefe, ya kuma matsawa ze sake rungumarta kmr maye, tayi hanzarin barin gurin, yace "Ki kawomin abinda zanci Mara nauyi fa ynzu...." Ya fadi hakanne gudun kada ta tafi taki dawowa, yi tayi kamar bata jishi ba taba ta nufa dakinta. Har wuraren 12:am yana jiran yaga ko zata kawo masa abincin dayace, amma yaji shiru, shi ba yunwar abinci yakeji ba yunwarta yakeji, tin breakfast din data bashi dasafe ne a cikinsa, amma sam bejin yunwa, so yakeyi yasha nono kuma ya taba laushin duwawu yunwarsu yakeji Ainun....har wuraren 2:am bata zo ba, Abdoljalal be rintsa ba, Seda yayi sallarh asubahi yasamu bacci ya kwasheshi... tin daga wannan ranar al-muqri'ah bata kuma bari sun kebance ba bata sake kuskuren kwana a dakinsaba, kullum da ita yake tafiya office saboda in be tafi da ita ba be iya ko zama yayi aikinsa yadda ya kamata, kuma ayyuka sun tarun masa wadanda dole shi zeyi, gashi anata kiransa ma abuja saboda meeting, da wasu manyan ayyukansa. duk yadda ya kaiga san ya taba mata jiki taki yadda