Sashe 91
Wata Kishiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
sun hadu a wani restaurant ne ita da hajiya saude da hajiya Abullen, hajiya lubah na ganin hajiya saude ta gane itace matar babban dan siyasarnan wato Abdoljalal nan take hajiya lubah ta isa garesu ta musu magana daganan suka zama kawaye, itama hajiya lubah daman mazauniyar kaduna ce, a nan suke zaune da mijinta da kishiyar tata. Byn sun kulla alaka , hajiya lubah tace zatazo har gida in hajiya saude ta koma nigeria domin ta bata sirrin yadda za ayi ta fidda kishiyarta saboda kowa yasan yadda hajiya saude ta rike mijinta gam AAsaraki ta hanashi aure, sannan se yadda tayi dashi. ita kuma hajiya lubah yanzu ba abinda ya tsole mata ido kamar kishiyarta wadda ta haifo yan shida tashin farko kuma duka maza, gashi yanzu ma hankalin mijin nata gabaki daya be kanta yana kan matarshi me y'ay'a, duk yadda hajiya lubah ta kaiga bita da kullenta dole seda mijinta Alhaji me-nasara ya mata kishiya, kaf shige da ficenta ya kare a banza, tinda abarda take gudu seda aka mata ita. Hajiya lubah dake cikin motar ta kasa isa packing space ta tsaya ta zubowa Abdoljalal da Almuqri'ah ido, nan take ta gane abdoljalal a fili domin tasha ganinsa a TV sosai, sannan dasuka hadu da hajiya saudema taga kaf kan screens din wayoyin hajiya sauden photonta ne ita da Abdoljalal din, seda hjya lubah ta rufe ido ta sake budesu a kan Abdoljalal da Almuqri'ah a bayyane tace"shine AAsarakin wallahi...." Mamaki ya rufe hajiya lubah ganin Almuqri'ah da ciki, sannan gata rike a hannun Abdoljalal, kuma gata kyakyawa dagani ma balarabiya ce, nan take hajiya lubah tashiga tunanin anya ba matarshi bace, ganin yadda ya riketama ya bata mamaki dagani de cikinnan na jikinta nashi ne, sannan dagani akwai so a tsakani sbda rikon dayayi mata ma naso ne da zallar kauna,, a karshema se hajiya lubah taga abdoljalal ya dauketa kmr jaririya ya wuce da ita, tanata kallonsu har suka bace mata, jikin hajiya lubah yayi sanyi "toh kode yayi Aurene shima A.Asarakin? Matarshice kenan wannan farar balarabiyar kou?'' Hajiya lubah ta fadi, tana nuna hanyar da Abdoljalal ya nufa da yarinyar a hannunsa. "Anya AAsaraki ze iya Aure hajiya saude na raye kuwa?'' Hajiya lubah fa jikinta ya kuma la'asar, tashiga thinking, kanta ya kwance gabaki daya, tayi losing control gabaki daya....tafi karfin 10mnt nan tsaye tana tunani tunani, kana ta isa da motarta packing space tayi packing ta fito kafafuwanta sanye da takalmi fari sol hannunta rike da farar hand bag me tsananin kyau, Sanye take da doguwar rigar danyar super dagani nan kayan kudine sosai a jikinta, ko mayafin jikintama abin kallo ne, hajiya lubah chocolate color ce tanada matsakaicin tsawo tanada kiba amma ba sosai ba, tanada kyau dai-dai nata sam bata da muni jikinnan nata lugub lugub abinka da jikin hutu sannan jikin wadda bata haihuwa, ko bari bata taba yiba, anyi magani amma ina, ba kasar da bataje ba neman mgni, ba gun bokan da bataje ba neman mgnin haihuwa amma Allah be nufa ba. Dai-dai hajiya luba ta fito daga motarta hajiya saude ta kira wayarta ta zuge bag dinta ta dakko wayar tata kirar samsung ta daga muryarta tayi sanyi karai, yadda taga Abdoljalal da Almuqri'ah ya kasa gogewa a cikin kanta. "Hajiya saude gani a cikin gidanki..." Cewar hajiya lubah da jikinta yayi sanyi. Cikin shewa Hajiya saude tace "okay gashinan na turo me aikina a miki iso zuwa falona qawata..." Hajiya luba tace "Okay...." Suka ajiye wayar, dai-dai larai ta iso inda hajiya luba take ta tsugunna ta gaidata kana suka nufa falon hajiya sauden, hajiya lubah ta matukar kosa taga hajiya saude su zanta a kan abinda idanuwan Hajiya lubah suka ganar mata..... Larai da hajiya lubah Suka isa falon hajiya sauden, hajiya lubah ta zauna kan kujera me zaman mutum biyu, ba kowa a falon hajiya saude na sama. Larai ta nufa saman ta sanar da hajiya sauden ta shigo da bakuwar falonta, kana larai ta dawo ta sanar da hajiya lubah hajiya sauden na zuwa,...hajiya lubah tace "okay..." sebin ko ina takeyi da kallo, musammanma picture din hajiya saude da Abdoljalal, ta kure Abdoljalal da ido, ta kara tabbatar da eh shidinne, Abdoljalal din data gani a waje da wata mace me ciki. Ajiyar zuciya hajiya lubah ta sauke zuciyarta taki mata dadih sam-sam. Larai ta cika table din gabanta da abubuwan motsa baki, hajiya lubah ta kasa ko shan ruwa zuciyarta da tunaninta sunki nutsuwa Allah-Allah kawai takeyi suyi 4eyes ita da hajiya saude, tanaso taji ko itama mijinta ya mata kishiyarne irin nata.. "Kai da kamar wuya gaskiya...domin kuwa ko a tsarin Aurema Hajiya saude bata dace da Abdoljalal ba sede dan tasirin Tsafi kawai, kuma nasan tasirin asirin baze taba barin Abdoljalal yima Hajiya saude kishiya ba....to wacece wannan me cikin dana ganshi da ita?'' Hajiya lubah ta rabka uban tagumi zuciyarta cike da tunani iri daban-daban... A haka hajiya saude ta sakko ta sameta, ta zauna kujerar dake facing dinta hajiya lubnah ta dago ta kalleta ta sakar mata murmushi. Hajiya saudenma murmushi ta sakar mata tace "maraba hajiya lubnah, barka da zuwa se yau de Allah ya kaddara zamu hadu nida ke Aminiyata..." Da fara'ah hajiya saude tayi maganar. Hajiya lubah dake kallan hajiya saude ganin nishadi a kan fuskar hajiya sauden yabawa hajiya lubah mamaki ita tinda mijinta ya kara aure bata kara fara'ah ba a rayuwarta. "Wallahi kuwa kawata, ya iyalinki?'' Cewar hajiya lubah kwata-kwata bata cikin hayyacinta. Hajiya saude ta amsa da "Alhamdulillahi..." Ta kure lubah da ido tinda ta shigo falon ta kula hajiya lubah na cikin matsananciyar damuwa, yadda ta ganta yau ba haka ta ganta ba a first time.. "Hajiya lubah bakisha ko ruwan sanyi ba, ko zamu karasa dinning ne kici abinci, tini nasa an shirya miki abincin ci dana sha..." Cewar hajiya saude datayi mgnr tana kallan table din gaban hajiya lubah.. "Aah hajiya, ruwan kawai nake ganin zansha domin makoshina ya bushe sosai,, " lubah ta fadi hakan hadi da bude bottle wata ta zuba a glass cup ta fara sha tana me karewa tsarin falon kallo, ita fa se yanzuma tasamu damar ganin kyaun falon hajiya sauden. "Wai akwai kudin a nan ba karya..."hajiya lubah ta fadi a ranta. Hajiya saude ta kula da yadda lubnah ke kallan falonta, seta karajin kanta wata, tana alfahari da abu daya, kaf frnds din da takeyi bata tabayin kawar dakeda arzikin da mijinta Abdoljalal yakeda shi ba. "Toh shikenan hajiya tinda baza kici abincin gidanaba ba damuwa.." Cewar hajiya saude, hajiya lubah tayi murmushin yake hadi da ajiye glass cup din ruwan hannunta, seda ta shanye gorar ruwa daya amma sam ji takeyi ma makoshinta be koshi ba. "Ba hk bane hajjaju, Ai nida ke tini muka zama daya..." Cewar lubah. Saude tace "Hakane.....sena ganki kamar a damuwa hajjaju..." Hajiya lubah ta sauke ajiyar zuciya tashin hankali, nan da nan kuma bayyana a kan fuskarta tace "Bari , ai damuwar ce tazamar min biyu hajiya,..." Hajiya saude ta gyara zamanta a kn kujerarta me zaman mutum uku tace "Dole ki shiga damuwa hajjaju ai kishiya bala'i ce kishiya matsifa ce, ke nifa da amin kishiya kwara ace uwata ta mutu wallahi..." Saude ta karashe mgnrta tana sauke nishin azabar kishi. Hajiya lubah ta xaro ido jin klmn dasuka fito daga bakin hajiya saude, nan take ta kara jinjina wacece hajiya saude "uwa fa kika ce hajiya saude?'' Cewar hajiya lubah data fadi maganar mamaki ya cikata tako ina. "Uwar mana, wallahi hajiya ban hada mijina da uban kowa fa, nifa ko masu aikina sun sanni da azabar kishi a kan mijina, kai nifa dan in kashe mutane dubu a kan mijina wallahi banyi kini ba inde a kan mijinane..... In takaice miki hajiya lubabatuh da ace da yadda zanyi dana kashe kaf matan duniya harda uwata saboda banasan mijina ya kalli mace, koda macen mata maza ce..." Saude ta fadi a zafafe, kai kace wanin ne ya kallar mata mijin yanzu haka, se gumi takeyi sbda azabar kishi. Hajiya lubah ta zaro dara-daran idanuwanta a kan saude, mamaki ya kashe mata jiki lubus, tana ganin tanada azabar kishinnan datake ganin ma duk duniya ba macen data kaita kishin bala'i, amma fa sam bata wasa da uwarta, mamaki biyu ne suka tarunma lubah, kalaman hajiya saude, toh kuma ita gashi taga mijin sauden da wata , kuma wallahi dagani tasan Akwai san yarinyar a kwayoyin idanuwansa,, mamaki mara misaltuwa ya kuma kashe lubnah. "To wacece wannan danaga AA saraki da ita? Kenan de ba matarshi bace kou? lubah ta tambayi kanta da kanta wannan tambayoyi tama kanta su sunfi a kirga a zuciyarta a halin yanzu. Kasa daurewa tayi ta kalli saude daketa faman jijjiga kafa daya itama lubah take kallo. Tace "Hajiya kenan baki da kishiya ne kou?''. "Har abadan abidina kuwa,,,,ni Hajiyasauden saraki ina raye amin kishiya ai har abadan wlhi, ko a hanya bansan inganta.." Cewar hajiya saude datayi mgnr a zafafe ita fa sam ko mgnr kishiyama bataso. Hajiya lubah tayi shiru hadi da bending a kan kujera ta sauke numfashi , nan da nan brain dinta tashiga thinking,jijiyoyin jinin jikinta suka motsa. "To ina kuka samo me ciki? Ko kinada kishin sauri ne a gidan, dan naga girman gidan ya baci..." Hajiya lubah ta kasa daurewa ta fayyace abinda ke cikinta, fuska dauke da mamaki. Saude tabi lubah da kallan rashin fahimta jin tace wai taga me ciki a gidanta, ta girgiza kai tace "Aah babu me ciki a cikin gidannan, ni kadai nake zaune bani da wasu kishin sauri, hajiya sede masu aiki kilan ko tumbi kika gani kike tunanin ciki ne gaskiya, dan shegun duk sunyi kiba...." Lubah ta tsaya tana nazarin kalaman saude tana me kara tunano yadda taga Abdoljalal da yarinyar ya rungumo bayan yarinyar jikinsa, wato duwawuknta, har ma fa yana kara danna duwawukan yarinyar jikinta duk hajiya lubah na gani. "Kai hajiya anya...wannan kuwa anya me aiki ce?, fara cefa sol nagani, yarinya karama ce ma dagani baza tafi 16yrs ba zuwa 17yrs wlhi,,,, sannan kai hajiya wannan cikine wallahi a jikin yarinyar bade tumbi ba ,, maganar Allah ciki ne na haihuwa bade tumbi ba, dukda ban taba