Sashe 87
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nayi shiru kawai ina sauraronshi. A en kwanakin nan kwata-kwata zuciyata a wuya na take, abu da wanda ya kai da wanda bai kai ba sai inji raina ya baci, akwai ranar da ina jan jagira hannuna ya kubce ta bata mun fuska, wani irin bacin rai ya ziyarce ni a lokacin, duk abubuwan da suke kan dresser din sai dana yi wurgi dasu suka fado kasa, abin zai baku mamaki da dariya idan kuka ga yanda na tsaya a kansu ina wani huci kamar tsohuwar macijiya, sai daga baya da fushin ya tafi kuma na dawo ina dariya da tu'ajjibi. Akwai kuma ranar da kadan ya hana in mazge Hafsy saboda nayi abinci tace gishiri yayi yawa, bayan a hakikanin gaskiya taste din bakina ya bace nayi ta zabga uban gishiri a cikin abincin ni da kaina dama sai dana yi tunanin haka amma data fada sai naji haushi.
Abbu ya dan tabo ni tare da juyo ni ina fuskantar shi, shiru nayi ina kallon kyakkyawar fuskar shi, ina so in gano laifi ko aibu a cikin abubuwan daya fada amma na kasa. Ban san abinda yasa nake fada dashi akan maganar aikin nan ba, lokacin da nake gida har addu'ah nake yi akan Allah ya kawo min miji wanda zai tsaya min akan komi kamar yadda Daddy yayi wa mommy, gashi yanzu na samu amma kuma na rasa abinda yasa na kasa yarda da hakan, m behaving really strange kwana biyun nan, wasu bakin halaye dana kasa gane su.
“Nafeesah??! Talk to me mana uhm?? Bana so muyi fada akan maganar nan please, kin dai san babu abinda zaki nema a duniyar nan da ba zan kasa miki shi ba, ba zan gazawa hidimomin ki ko kadan ba kin ji? Kuma In shaa Allah ba zan taba bari kiyi dana sanin kin yin wannan aikin ba, ok?" kai na gyada mishi a hankali, yayi murmushi a hankali, “uwww thanks my baby..." ya sadda kanshi saitin fuskana zai yi rewarding dina da kiss, naja wata doguwar shakuwa data sa ya dakata yana kallona, daga haka kuma ba sai kakarin amai ba? Na tashi da gudu na shige bandaki, sai dana amayar da duk abubuwan dana ci a take, Abbu yana tsaye a gefena yana dan bubbuga bayana har na gama aman, ya taimaka min na wanke bakina ya kaini kan gado ya kwantar ya koma toilet din.
Kafin ya fito na dukunkune cikin bargo ina rawar sanyi sosai, hankali tashe ya tarairayo ni jikin shi yana taba wuya na, waya ya dauko ya kira family doctor dinmu, Doctor Salmah. Bayan kamar mintuna arba'in ta iso, lokacin zazzabin ya sauka sai jikina da yayi wani irin sanyi kamar an min duka, kasala duk ta lullube ni. Tayi duk wasu gwaje-gwaje da zata yi, daga karshe dai ta bani wata kwalba tace inje inyi fitsari a ciki, na dafa kafadar Anty Mubeenah muka shiga toilet, ta fita ta bar ni nayi fitsarin ina gamawa ta shigo muka koma dakin, Docta ta amsa kwalbar ni kuma na koma kan gado na kwanta, muka yi zuru-zuru muna kallonta tana saka strip a cikin kwalbar fitsarin.
Bayan kamar minti goma ta dago abin yadda duk zamu gani, bamu fahimci komi ba sai da muka ji tace “mashaa Allah!! Farfesa matar ka na da juna biyu!!" a rikice na kamo hannun Abbu na rirrike kamar zan tsinke mishi shi, ya kamo wuyana ya hada fuskata da tashi waje guda yana furta wasu addu'o'i da ake son mutum ya dinga furta su cikin halin tsananin farin ciki. Anty Mubeenah ta dafa kafadata ko ban fada ba nasan tana murna da abinda taji ne. Docta tayi er dariya ta fara tattara kayanta tana fadawa Abbu bata bincika ko watan nawa ba saboda haka ya kaini asibiti washegari a duba da kuma lafiyata data jaririn yace toh. Nan ta mana sallama ta tafi bayan Abbu ya mata kyautar da bai san adadinta ba don hannu kawai ya saka a cikin aljihun shi ya damko kudi ya mika mata.
Ranar kam naga tattali da kulawa ba daga mijina ba ba daga 'ya'yan mijina da en uwanshi ba, ba daga kishiyata ba ba daga Iyayena ba kada ma dai Daddy yaji labari. A ranar ya kirani shi da Mommy ban ma san wanda ya sanar dasu zancen cikin ba suka taya ni murna da addu'o'i iri-iri Mommy kuma yadda zan kula da kaina take fada min tana nanatawa kamar karatu.
Cikin wata hudu ne lokacin da muka je aka duba, babu wata damuwa ko matsala a tare dani sai hawan jini wanda ba wani damuwa bani tunda dama it's a normal thing a wajen mata masu ciki, an dai bani abubuwa da zan dings ci da kuma abubuwan daya kamata inyi da wanda ba zan yi ba domin rainon cikina cikin sauki da kwanciyar hankali. A cikin mota a hanyar mu ta dawowa daga asibitin Abbu ya riko hannuna yana shafawa a hankali yace “ya zancen aiki ya tafi koh?" na gyada mishi kai ina murmushi. Yayi er dariya tare da cewa “ai Doctor Salmah ta fada min cikin jikin ki ne yasa kika zama short tempered woman, haba! I was wondering dalilin da yasa mutum mai sanyin hali irin ki ya zama mai fada da zuciya cikin dan kankanin lokaci, amma tun da na gano kan abin, zamu dinga kiyayewa bacin ranki don tace hakan zai iya sawa jinin ki ya hau..... Allah ya sauke min ke lafiya baby" nayi murmushi nace “Ameeen Abbu nah..!".
Cikina sai daya shiga watanninshi na bakwai sannan ya fara girma saboda da babu wani girma kuma babu laulayi ba komi sai fresh da nayi da kuma cin abinci da shan tatacciyar madara. Kafin in shiga watan haihuwa ta kuwa na zama shirgegiya, zama da kyar tashi da dabara. Kullum na kan zagaye gidan sau hudu ko biyar don ance hakan yana da kyau sosai. Yanzu dai haihuwa kadai muke jira, komi is ready, hatta da cokalin da za a ba baby ruwa dashi ranar da aka haife shi an siyo an ajiye, komi unisex Abbu yake siyowa kuma guda biyu, duk da dai naki yin scanning amma Abbu da Anty Mubeenah har ma da sauran mutane suna cewa wai girman cikina irin na en biyu ne, don Abbu ma cewa yayi wai yana mafarkin ya ganni ina wasa da yara biyu ina miko mishi su, ni dai fatana kawai Allah ya sauke ni lafiya.
Ranar wata Talata na tashi da matsananciyar nakuda, nan muka kwasa Zuwa asibiti. Nakuda nayi mai tsawo da wahala kusan yini daya ina abu daya, abin ya gigita ni. Ban taba sanin cewa zafin nakuda nake yi ba. Abbu da yayi jan ido ya shigo labour room din sai waje aka yi dashi saboda dana shiga mood din “ duke kai ne ka janyo min wannan wahalar..." abin bai yi kyawu ba. Sai zuwa bayan Maghrib Baby ya fito, nan na fara ajiye numfashi, sai dai me? Wani ciwon ne ya sake turnike ni kafin kace me?! Wani yunkurin sai ga wani babyn. Na maida kaina kan gadon asibitin na kwantar ina ajiyar numfashi da karfi, nurse din data karbi haihuwar ta duba yaran tace “Masha Allah!! Maza ne Allah ya raya miki su!!". Tuni yaran suka hade dakin da kukan da aka san lafiyayyun jarirai nayi. Nan dai aka shirya mu muka fito tsaf damu. Throughout lokacin babu abinda nake furtawa fili da ciki sai ‘Rabbir-ham huma kamar Rabbiyaani Swigaara...!!' wa Mommy na da duk wasu matan duniya, haihuwa is really not a simple thing.
Ana fito damu Abbu da yara suka shigo, nan fa suka lullube yaran suna murnar samun kanne, Abbu dai ya samu ya lallabo yazo inda nake ya tallabo ni a cikin jikin shi ya rungume yana shafa bayana. Ya dago goshina ya bani peck a kumatuna, “well-done Baby, kinyi kokari really! Allah ya albarkace ku ke da ‘ya‘yanki" nace “ameen... Wani irin baby kuma? Ga babies dinka can" ya juya ya kallesu ya juyo ya kalleni yana murmushi, “me na fada miki? You were going to give me twins, next year ma haka, n the other year, n the other too...!" na zaro ido ina cewa “mutuwa kawai kake rokar min!" yayi dariya tare da saki na yaje ya dauki yaran, Anty Mubeenah kuma ta matso tana jera min sannu.
Sai washegari aka bamu sallama muka wuce gidanmu muka cigaba da karbar barka har zuwa ranar suna inda yara suka ci sunan Abdul-Qadir da Mukhtar (Sunan Daddy na) muna kiran Abdul-Qadeer Ameer shi kuma Mukhtar Daddy. Aka yi taron suna aka watse aka bar mu da yara da Dattijuwa Hanne daga Malumfashi muna wankan jego.
Cikin dan tsakanin Abbu ya bude min babbar plaza wadda Daddy na ya cike min rabin shagunan plazar da kaya ana kula min dasu, rayuwa ta ko wani fanni tana gara mana cikin dadi da kwanciyar hankali babu abinda zamu ce da Ubangijin mu sai dai Godiya....
*****
“Ameer!! Daddy!!!" na fito falo ina kwalawa yaran kira, Anty Mubeenah dake kicin tana dambun nama duk da ba girkinta ba ne, tana taya ni hada abubuwan motsa baki da muka saba yi saboda baki da kuma emergency food. Ta leko tace “ya aka yi ne ake neman dears haka?" naja tsaki, “yaran nan daure su zan fara yi a jikin gado gaskiya, kullum jan magana da barna kamar wasu beraye? Kwalbar turare na mai kyau fa kawai suka dauka daga kan mirror suka hada ta da bango, shine da suka ga ta fashe suka tsere" Anty tayi Dariya tace “aikuwa yanzu suka bi su Qaseem garden wai suna tennis" nayi kwafa, “I'll just go and register them a makarantar su Qaseem ma kawai ko na samu sawaba da sanyin zuciya" Anty tayi dariya tana girgiza kai tace “ke da yaran nan naki koh?" ni kuma na juya zuwa dakina.
Abbu ya dan tabo ni tare da juyo ni ina fuskantar shi, shiru nayi ina kallon kyakkyawar fuskar shi, ina so in gano laifi ko aibu a cikin abubuwan daya fada amma na kasa. Ban san abinda yasa nake fada dashi akan maganar aikin nan ba, lokacin da nake gida har addu'ah nake yi akan Allah ya kawo min miji wanda zai tsaya min akan komi kamar yadda Daddy yayi wa mommy, gashi yanzu na samu amma kuma na rasa abinda yasa na kasa yarda da hakan, m behaving really strange kwana biyun nan, wasu bakin halaye dana kasa gane su.
“Nafeesah??! Talk to me mana uhm?? Bana so muyi fada akan maganar nan please, kin dai san babu abinda zaki nema a duniyar nan da ba zan kasa miki shi ba, ba zan gazawa hidimomin ki ko kadan ba kin ji? Kuma In shaa Allah ba zan taba bari kiyi dana sanin kin yin wannan aikin ba, ok?" kai na gyada mishi a hankali, yayi murmushi a hankali, “uwww thanks my baby..." ya sadda kanshi saitin fuskana zai yi rewarding dina da kiss, naja wata doguwar shakuwa data sa ya dakata yana kallona, daga haka kuma ba sai kakarin amai ba? Na tashi da gudu na shige bandaki, sai dana amayar da duk abubuwan dana ci a take, Abbu yana tsaye a gefena yana dan bubbuga bayana har na gama aman, ya taimaka min na wanke bakina ya kaini kan gado ya kwantar ya koma toilet din.
Kafin ya fito na dukunkune cikin bargo ina rawar sanyi sosai, hankali tashe ya tarairayo ni jikin shi yana taba wuya na, waya ya dauko ya kira family doctor dinmu, Doctor Salmah. Bayan kamar mintuna arba'in ta iso, lokacin zazzabin ya sauka sai jikina da yayi wani irin sanyi kamar an min duka, kasala duk ta lullube ni. Tayi duk wasu gwaje-gwaje da zata yi, daga karshe dai ta bani wata kwalba tace inje inyi fitsari a ciki, na dafa kafadar Anty Mubeenah muka shiga toilet, ta fita ta bar ni nayi fitsarin ina gamawa ta shigo muka koma dakin, Docta ta amsa kwalbar ni kuma na koma kan gado na kwanta, muka yi zuru-zuru muna kallonta tana saka strip a cikin kwalbar fitsarin.
Bayan kamar minti goma ta dago abin yadda duk zamu gani, bamu fahimci komi ba sai da muka ji tace “mashaa Allah!! Farfesa matar ka na da juna biyu!!" a rikice na kamo hannun Abbu na rirrike kamar zan tsinke mishi shi, ya kamo wuyana ya hada fuskata da tashi waje guda yana furta wasu addu'o'i da ake son mutum ya dinga furta su cikin halin tsananin farin ciki. Anty Mubeenah ta dafa kafadata ko ban fada ba nasan tana murna da abinda taji ne. Docta tayi er dariya ta fara tattara kayanta tana fadawa Abbu bata bincika ko watan nawa ba saboda haka ya kaini asibiti washegari a duba da kuma lafiyata data jaririn yace toh. Nan ta mana sallama ta tafi bayan Abbu ya mata kyautar da bai san adadinta ba don hannu kawai ya saka a cikin aljihun shi ya damko kudi ya mika mata.
Ranar kam naga tattali da kulawa ba daga mijina ba ba daga 'ya'yan mijina da en uwanshi ba, ba daga kishiyata ba ba daga Iyayena ba kada ma dai Daddy yaji labari. A ranar ya kirani shi da Mommy ban ma san wanda ya sanar dasu zancen cikin ba suka taya ni murna da addu'o'i iri-iri Mommy kuma yadda zan kula da kaina take fada min tana nanatawa kamar karatu.
Cikin wata hudu ne lokacin da muka je aka duba, babu wata damuwa ko matsala a tare dani sai hawan jini wanda ba wani damuwa bani tunda dama it's a normal thing a wajen mata masu ciki, an dai bani abubuwa da zan dings ci da kuma abubuwan daya kamata inyi da wanda ba zan yi ba domin rainon cikina cikin sauki da kwanciyar hankali. A cikin mota a hanyar mu ta dawowa daga asibitin Abbu ya riko hannuna yana shafawa a hankali yace “ya zancen aiki ya tafi koh?" na gyada mishi kai ina murmushi. Yayi er dariya tare da cewa “ai Doctor Salmah ta fada min cikin jikin ki ne yasa kika zama short tempered woman, haba! I was wondering dalilin da yasa mutum mai sanyin hali irin ki ya zama mai fada da zuciya cikin dan kankanin lokaci, amma tun da na gano kan abin, zamu dinga kiyayewa bacin ranki don tace hakan zai iya sawa jinin ki ya hau..... Allah ya sauke min ke lafiya baby" nayi murmushi nace “Ameeen Abbu nah..!".
Cikina sai daya shiga watanninshi na bakwai sannan ya fara girma saboda da babu wani girma kuma babu laulayi ba komi sai fresh da nayi da kuma cin abinci da shan tatacciyar madara. Kafin in shiga watan haihuwa ta kuwa na zama shirgegiya, zama da kyar tashi da dabara. Kullum na kan zagaye gidan sau hudu ko biyar don ance hakan yana da kyau sosai. Yanzu dai haihuwa kadai muke jira, komi is ready, hatta da cokalin da za a ba baby ruwa dashi ranar da aka haife shi an siyo an ajiye, komi unisex Abbu yake siyowa kuma guda biyu, duk da dai naki yin scanning amma Abbu da Anty Mubeenah har ma da sauran mutane suna cewa wai girman cikina irin na en biyu ne, don Abbu ma cewa yayi wai yana mafarkin ya ganni ina wasa da yara biyu ina miko mishi su, ni dai fatana kawai Allah ya sauke ni lafiya.
Ranar wata Talata na tashi da matsananciyar nakuda, nan muka kwasa Zuwa asibiti. Nakuda nayi mai tsawo da wahala kusan yini daya ina abu daya, abin ya gigita ni. Ban taba sanin cewa zafin nakuda nake yi ba. Abbu da yayi jan ido ya shigo labour room din sai waje aka yi dashi saboda dana shiga mood din “ duke kai ne ka janyo min wannan wahalar..." abin bai yi kyawu ba. Sai zuwa bayan Maghrib Baby ya fito, nan na fara ajiye numfashi, sai dai me? Wani ciwon ne ya sake turnike ni kafin kace me?! Wani yunkurin sai ga wani babyn. Na maida kaina kan gadon asibitin na kwantar ina ajiyar numfashi da karfi, nurse din data karbi haihuwar ta duba yaran tace “Masha Allah!! Maza ne Allah ya raya miki su!!". Tuni yaran suka hade dakin da kukan da aka san lafiyayyun jarirai nayi. Nan dai aka shirya mu muka fito tsaf damu. Throughout lokacin babu abinda nake furtawa fili da ciki sai ‘Rabbir-ham huma kamar Rabbiyaani Swigaara...!!' wa Mommy na da duk wasu matan duniya, haihuwa is really not a simple thing.
Ana fito damu Abbu da yara suka shigo, nan fa suka lullube yaran suna murnar samun kanne, Abbu dai ya samu ya lallabo yazo inda nake ya tallabo ni a cikin jikin shi ya rungume yana shafa bayana. Ya dago goshina ya bani peck a kumatuna, “well-done Baby, kinyi kokari really! Allah ya albarkace ku ke da ‘ya‘yanki" nace “ameen... Wani irin baby kuma? Ga babies dinka can" ya juya ya kallesu ya juyo ya kalleni yana murmushi, “me na fada miki? You were going to give me twins, next year ma haka, n the other year, n the other too...!" na zaro ido ina cewa “mutuwa kawai kake rokar min!" yayi dariya tare da saki na yaje ya dauki yaran, Anty Mubeenah kuma ta matso tana jera min sannu.
Sai washegari aka bamu sallama muka wuce gidanmu muka cigaba da karbar barka har zuwa ranar suna inda yara suka ci sunan Abdul-Qadir da Mukhtar (Sunan Daddy na) muna kiran Abdul-Qadeer Ameer shi kuma Mukhtar Daddy. Aka yi taron suna aka watse aka bar mu da yara da Dattijuwa Hanne daga Malumfashi muna wankan jego.
Cikin dan tsakanin Abbu ya bude min babbar plaza wadda Daddy na ya cike min rabin shagunan plazar da kaya ana kula min dasu, rayuwa ta ko wani fanni tana gara mana cikin dadi da kwanciyar hankali babu abinda zamu ce da Ubangijin mu sai dai Godiya....
*****
“Ameer!! Daddy!!!" na fito falo ina kwalawa yaran kira, Anty Mubeenah dake kicin tana dambun nama duk da ba girkinta ba ne, tana taya ni hada abubuwan motsa baki da muka saba yi saboda baki da kuma emergency food. Ta leko tace “ya aka yi ne ake neman dears haka?" naja tsaki, “yaran nan daure su zan fara yi a jikin gado gaskiya, kullum jan magana da barna kamar wasu beraye? Kwalbar turare na mai kyau fa kawai suka dauka daga kan mirror suka hada ta da bango, shine da suka ga ta fashe suka tsere" Anty tayi Dariya tace “aikuwa yanzu suka bi su Qaseem garden wai suna tennis" nayi kwafa, “I'll just go and register them a makarantar su Qaseem ma kawai ko na samu sawaba da sanyin zuciya" Anty tayi dariya tana girgiza kai tace “ke da yaran nan naki koh?" ni kuma na juya zuwa dakina.