Sashe 76
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina shiga muka hada idanu da ita kamar wadda take jiran isowa ta, ni da ita muka yi stilling a waje guda, ni na fargabar abinda zai je yazo ni yayin da a nata 6angaren ban san dalili ba.
Ta janye idanunta a kaina, yayin dana daga kafa da kyar na karasa shiga cikin dakin. Gefen gado kusa da maijego na zauna nesa da inda Anty Mubeenar ta zauna ita da kanwar ta Shakirah wadda sai dana zauna na kula da ita a wajen hakan ya kara min fargabata, a tunani na ko taron dangin cin kaniyata suka yi.
Da dan murmushina cike da yake na dubi inda take zaune nace “Anty Mubeenah ina yinin ku?" ta dage kai sama yadda kasan ba da ita nake ba, sai Shakirah ce ta amsa da er fara'arta har da cewa “su amare ne?, Ai naso lekawa har gidan naki mu gaisa Allah bai nufa ba tunda bamu samu zuwa biki ba, Allah ya sanya alkhairi!" na amsa da “Ameen" a hankali kuma a dan kunyace ina satar kallon inda Anty Mubeenah take a zaune koma ince a hakimce, to ta dare kan gado tare wani baje-baje yadda kuka san kan gadonta tana kallon kowa daya bayan daya kamar wasu bayinta ko irin en duniya dinnan da daurin kallabinta ture-ni-kaga-tsiya dinnan wanda ya fito da daddagaggiyar keyar ta gashi duk a cunkushe, sosai matar take bani mamaki. Kamar ta ace tana da saloon guda amma gashinta bashi da maraba da wata Inna ko Goggo a kauye wadda bata san menene ma'anar Relaxer, Shampoo ko Stretcher da stuffs dinnan ba.
Tashi tsaye tayi tana jan hannun Shakira tana magana kamar mai gunaguni, “Malama tashi mu tafi koh?" Shakirar ta maida ta ta zaunar tace “haba ke kuwa, ba mu jima da zuwa ba fa! Bari mu dan jima mana" ta koma ta zauna tana wasu guna-guni, fuskar nan tayi wani sha6ar babu kyawun gani, na kauda kallona daga gun su kafin cibi ya zama kari kuma.
Anty Ameenah ta shigo dakin, “Nafeesah kin ci abinci kuwa?" na dan girgiza mata kai, “A'ah Anty, bana jin yunwa ne" ta dan hade fuska, “a‘ah ban yarda ba, maza-maza tashi ki nemo abinci.... Ko don ma ina zuwa" ta juya ta fita daga dakin.
Tana fita su Hafsy su duka ukun suma suka shigo, dama kai tsaye Hafsy wajena ta taho, su kuma biyun sai da suka matso kusa sannan suka lura dani. Qaseem ne yayi tsallen murna ya karaso wajena shima yayin da Abdullahi yayi gefen mahaifiyar shi. Yaran suka zauna a gefena muka gaisa da Qaseem, na kalli inda Abdullahi yake zaune cikin er tsokana nace “su Abdullahi babu magana ne??" ya kalleni sosai kafin ya dauke fuskar shi ba tare da yayi magana ba. A take na sha jinin jikina, tun ranar da suka je gidana na kula da wasu canje-canje a tare dashi dama kawai ban yi tunanin wani abu bane mai girma amma yanzu kam, na hangi babban lamari a tare da yaron.
Muna nan Anty Ameenah ta dawo dakin hannunta dauke da plate shake da fried rice, coleslaw, da naman kaza a sama ta miko min plate din, na zare ido cike da mamaki na kalleta nace “Anty ina zan kai wannan abincin?" tace “cikin ki mana! Ni anya ma kuwa kina cin abinci yadda yakamata Nafeesah?" na sadda kaina kasa ina dan murmushi kawai. Ta zauna a gefen gado sai a lokacin ta kula dasu Mubeenah a zaune, Shakirah ce ta fara gaida ta, tayi dan murmushi ta amsa ta dauke kanta ga mayar da bakin da suke cikin dakin. Na jijjiga kai a hankali ina kara jinjina halin Mubeenah a cikin raina.
Ni dasu Hafsy muka fara cin abincin, har ga Allah turawa kawai nake yi. Ga rashin jin yunwa, ga tunanin sauyawar dabi'un Abdullahi a gare ni, abin ya daure min kai sosai. Muna cikin cin abincin naga ya tashi ya fita daga cikin dakin, da sauri na tashi na bi bayan shi.
A can bayan gidan wajen wasu shuke-shuke na same shi a zaune, ya kurawa shukokin idanuwa very lost in his thought, sai dana zauna a gefen shi sannan ya kula dani. Yayi saurin dauke kanshi ya sadda shi kasa. Dan murmushi nayi tare da gyara zama na sosai. Muka yi shiru muna kallon shukokin, can nace mishi.,
“Ka tsane ni koh Abdullahi?" da alamun tambayar tawa ta bashi mamaki sosai, da sauri ya dago ya kalleni yana girgiza kai alamun a'ah, sai dana sake ajiyar zuciyar relief a hankali kafin nace “kar ka boye min komi Abdullahi. Nasan cewa dama dole zaku tsane ni, nazo na aure muku mahaifi na zama kishiyar mahaifiyar ku, ko ba haka ba?" nan ma ya girgiza kai da sauri.
Nayi shiru tare da kura mishi idanu, idan ba haka bane ba to menene? Na juya na fuskance shi sosai tare da riko hannayen shi nace “to idan ba haka bane ba Abdullahi menene? Me yasa kake avoiding dina? Last time da kuka zo gidana dama haka kake sakewa kamar ni bakuwar ka ce wadda baka taba gani ba, you hurt my feelings you know... Now, gaya min, ni ce koh?" ya sake girgiza kai, a hankali kamar mai tsoron yin maganar yace “Abbu ne!!".
Na zaro ido cike da mamaki ina kallon shi, “Abbu da kan shi? Me ya maka? Fada min zan mishi magana kaji??" ya kura min idanu kamar ba zai yi magana ba, can kuma yayi maganar da tasa na kusa sakin fitsari a wando saboda tsananin mamaki. “cewa yayi baya son Mommyn mu!!" ya fada muryar shi na dan rawa yayin da idanun shi suka cika da hawaye.
Da gaske gabana ya fadi, duk wata kalma ta bace daga cikin kaina. Cikin sanyin jiki na kura mishi idanu nace “shi Abbu din ne ya fada maka haka da bakinsa?" yayi saurin girgiza kai, “a'ah, Mommy ya fadawa. Ni kuma lokacin naje dakin shi ince ya kai mu gidanki mu yini, shine naji yana gaya mata cewa baya son ta ke yake so!" na dafe saitin zuciyata dake bugawa, ba wai na jin dadin maganar ko fluttering ba, na takaici da wani dan tsillin jin haushin abinda Abbu yayi. A tunani na sai mazajen da basu san inda yake musu ciwo bane suke irin wadannan halaye, ashe ba haka bane.
A lokacin na fahimci cewa wasu iyayen su suke sa ‘ya‘yan su su tsani kishiyoyin iyayen su. Babu yadda za ayi ace a yabi wata ba uwar yaro ba, ko a fifita wata akan uwar yaro bai ji haushin abin ba koda uwar tashi bata da kyawun hali kuwa. Kamar dai abinda yake faruwa yanzu, wanda ba zan taba bari hakan ya faru ba. Mun gina amintacciyar rayuwa ni da yaran, they trust me, suna so na, suna girmama ni, ba zan taba bari hakan ya taba amintar mu ba.
Nace “shi yasa ka tsane ni kenan?" yayi shiru kan shi a kasa, “lokacin da naji labarin zaki auri Dad dinmu, frankly naji haushi. Me yasa muna kallon ki a matsayin yaya a gare mu zaki buge da auren Abbu? Daga baya kuma sai na fara tunanin hakan ai ba laifi bane ba, kuma zamu zama muna tare dake a koda yaushe saboda believe me muna son ki wallahi. Har lokacin da muka zo gidanki ina cikin confusion, daga karshe dai nazo nayi concluding cewa Kaddarar ki ce hakan don haka na kauda tunanin komi a cikin raina nayi niyar rungumar ki da zuciya daya. Saboda haka ne ma nayi niyar sa Abbu ya kaimu gidan ki mu yini in kuma baki hakurin abinda ya faru ranar farko da muka je gidan ki. Sai kuma na kare da jin maganganun dasu Abbun suke yi..., I was afraid! Naji tsoron cewa zaki iya sa wa Abbu ya tsani Mommy ya daina kula ta, muma yazo ya tsane mu ya daina son mu sai ke da baby idan kin haihu..., irin yadda Daddyn su abokina Ameer ya musu lokacin daya kara aure!".
Na fahimci irin tsoro da fargabar da yake ciki, na matsa tare da kamo hannun shi sosai. Nace “look Abdul, ni ba irin matar Baban su Ameer abokin ka bace kaji? Ba zan taba bari wani abun cutarwa yazo kusa da ku ba balle in cuce ku da kaina. Sannan Abbun ku yana son Mommyn ka kaji?" yaron ya kalleni sosai with so much hope in his eyes sai da naji kamar zan yi kuka. Fuskar shi ta washe da murmushi, “da gaske Anty Nafeesah?" na daga mishi kai da sauri, “sosai ma. Yafi son ta akai na ma. Kawai ranar ai ya fada min, yana so ne yaga abinda zata yi ne shi yasa yace haka. Wasa yake mata!!" na karasa maganar cikin cije baki.
Yayi ajiyar zuciya, “har naji dadi wallahi, da har na fara ji Abbu ya fara bani haushi!" da sauri nace mishi “kul! Kar ka sake maimaita irin haka kaji Abdul? Ko me iyayen mu suka mana bamu da damar jin haushin su a cikin ranmu kana jin mu? Duk abinda zasu yi suna da dalili don haka mu dinga musu uziri ka gane?" ya gyada kai cikin fahimta, “na gane. Nagode sosai Anty Nafeesah! Kiyi hakuri kuma" na shafa tattausar tattaurar sumar kanshi ina murmushi, “are we good now?" shima ya gyada kai yana murumushi. Nace “zo mu koma cikin gida kaga yamma tayi kila su Mommyn ka suna neman ka. Kada fa ka sanya damuwar komi a cikin ranka kaji?" ya gyada kai. Naja hannun shi muka tafi.
Aikuwa su Anty Mubeenah na waje suna neman shi, ganin mu tare fuskar ta ta danyi frowning da ban san ko na menene ba. Na daure duk da sanyin da gwiwa ta tayi muka karasa har gaban motar su, wanda kafin muje sun shige ciki, Abdullahi ya bude baya ya shiga na leka ta jikin taga ina musu Allah ya kiyaye hanya, Anty Shakira da yaran suka amsa cikin fara'ah yayin da mai gayya Mubeenah ta dauke kai gefe, ni dama nasan za a rina. Suka ja motar suka tafi, na sauke ajiyar zuciya a hankali na juya zuwa cikin gidan, lokacin an fara kiran Sallar Magriba.
Ta janye idanunta a kaina, yayin dana daga kafa da kyar na karasa shiga cikin dakin. Gefen gado kusa da maijego na zauna nesa da inda Anty Mubeenar ta zauna ita da kanwar ta Shakirah wadda sai dana zauna na kula da ita a wajen hakan ya kara min fargabata, a tunani na ko taron dangin cin kaniyata suka yi.
Da dan murmushina cike da yake na dubi inda take zaune nace “Anty Mubeenah ina yinin ku?" ta dage kai sama yadda kasan ba da ita nake ba, sai Shakirah ce ta amsa da er fara'arta har da cewa “su amare ne?, Ai naso lekawa har gidan naki mu gaisa Allah bai nufa ba tunda bamu samu zuwa biki ba, Allah ya sanya alkhairi!" na amsa da “Ameen" a hankali kuma a dan kunyace ina satar kallon inda Anty Mubeenah take a zaune koma ince a hakimce, to ta dare kan gado tare wani baje-baje yadda kuka san kan gadonta tana kallon kowa daya bayan daya kamar wasu bayinta ko irin en duniya dinnan da daurin kallabinta ture-ni-kaga-tsiya dinnan wanda ya fito da daddagaggiyar keyar ta gashi duk a cunkushe, sosai matar take bani mamaki. Kamar ta ace tana da saloon guda amma gashinta bashi da maraba da wata Inna ko Goggo a kauye wadda bata san menene ma'anar Relaxer, Shampoo ko Stretcher da stuffs dinnan ba.
Tashi tsaye tayi tana jan hannun Shakira tana magana kamar mai gunaguni, “Malama tashi mu tafi koh?" Shakirar ta maida ta ta zaunar tace “haba ke kuwa, ba mu jima da zuwa ba fa! Bari mu dan jima mana" ta koma ta zauna tana wasu guna-guni, fuskar nan tayi wani sha6ar babu kyawun gani, na kauda kallona daga gun su kafin cibi ya zama kari kuma.
Anty Ameenah ta shigo dakin, “Nafeesah kin ci abinci kuwa?" na dan girgiza mata kai, “A'ah Anty, bana jin yunwa ne" ta dan hade fuska, “a‘ah ban yarda ba, maza-maza tashi ki nemo abinci.... Ko don ma ina zuwa" ta juya ta fita daga dakin.
Tana fita su Hafsy su duka ukun suma suka shigo, dama kai tsaye Hafsy wajena ta taho, su kuma biyun sai da suka matso kusa sannan suka lura dani. Qaseem ne yayi tsallen murna ya karaso wajena shima yayin da Abdullahi yayi gefen mahaifiyar shi. Yaran suka zauna a gefena muka gaisa da Qaseem, na kalli inda Abdullahi yake zaune cikin er tsokana nace “su Abdullahi babu magana ne??" ya kalleni sosai kafin ya dauke fuskar shi ba tare da yayi magana ba. A take na sha jinin jikina, tun ranar da suka je gidana na kula da wasu canje-canje a tare dashi dama kawai ban yi tunanin wani abu bane mai girma amma yanzu kam, na hangi babban lamari a tare da yaron.
Muna nan Anty Ameenah ta dawo dakin hannunta dauke da plate shake da fried rice, coleslaw, da naman kaza a sama ta miko min plate din, na zare ido cike da mamaki na kalleta nace “Anty ina zan kai wannan abincin?" tace “cikin ki mana! Ni anya ma kuwa kina cin abinci yadda yakamata Nafeesah?" na sadda kaina kasa ina dan murmushi kawai. Ta zauna a gefen gado sai a lokacin ta kula dasu Mubeenah a zaune, Shakirah ce ta fara gaida ta, tayi dan murmushi ta amsa ta dauke kanta ga mayar da bakin da suke cikin dakin. Na jijjiga kai a hankali ina kara jinjina halin Mubeenah a cikin raina.
Ni dasu Hafsy muka fara cin abincin, har ga Allah turawa kawai nake yi. Ga rashin jin yunwa, ga tunanin sauyawar dabi'un Abdullahi a gare ni, abin ya daure min kai sosai. Muna cikin cin abincin naga ya tashi ya fita daga cikin dakin, da sauri na tashi na bi bayan shi.
A can bayan gidan wajen wasu shuke-shuke na same shi a zaune, ya kurawa shukokin idanuwa very lost in his thought, sai dana zauna a gefen shi sannan ya kula dani. Yayi saurin dauke kanshi ya sadda shi kasa. Dan murmushi nayi tare da gyara zama na sosai. Muka yi shiru muna kallon shukokin, can nace mishi.,
“Ka tsane ni koh Abdullahi?" da alamun tambayar tawa ta bashi mamaki sosai, da sauri ya dago ya kalleni yana girgiza kai alamun a'ah, sai dana sake ajiyar zuciyar relief a hankali kafin nace “kar ka boye min komi Abdullahi. Nasan cewa dama dole zaku tsane ni, nazo na aure muku mahaifi na zama kishiyar mahaifiyar ku, ko ba haka ba?" nan ma ya girgiza kai da sauri.
Nayi shiru tare da kura mishi idanu, idan ba haka bane ba to menene? Na juya na fuskance shi sosai tare da riko hannayen shi nace “to idan ba haka bane ba Abdullahi menene? Me yasa kake avoiding dina? Last time da kuka zo gidana dama haka kake sakewa kamar ni bakuwar ka ce wadda baka taba gani ba, you hurt my feelings you know... Now, gaya min, ni ce koh?" ya sake girgiza kai, a hankali kamar mai tsoron yin maganar yace “Abbu ne!!".
Na zaro ido cike da mamaki ina kallon shi, “Abbu da kan shi? Me ya maka? Fada min zan mishi magana kaji??" ya kura min idanu kamar ba zai yi magana ba, can kuma yayi maganar da tasa na kusa sakin fitsari a wando saboda tsananin mamaki. “cewa yayi baya son Mommyn mu!!" ya fada muryar shi na dan rawa yayin da idanun shi suka cika da hawaye.
Da gaske gabana ya fadi, duk wata kalma ta bace daga cikin kaina. Cikin sanyin jiki na kura mishi idanu nace “shi Abbu din ne ya fada maka haka da bakinsa?" yayi saurin girgiza kai, “a'ah, Mommy ya fadawa. Ni kuma lokacin naje dakin shi ince ya kai mu gidanki mu yini, shine naji yana gaya mata cewa baya son ta ke yake so!" na dafe saitin zuciyata dake bugawa, ba wai na jin dadin maganar ko fluttering ba, na takaici da wani dan tsillin jin haushin abinda Abbu yayi. A tunani na sai mazajen da basu san inda yake musu ciwo bane suke irin wadannan halaye, ashe ba haka bane.
A lokacin na fahimci cewa wasu iyayen su suke sa ‘ya‘yan su su tsani kishiyoyin iyayen su. Babu yadda za ayi ace a yabi wata ba uwar yaro ba, ko a fifita wata akan uwar yaro bai ji haushin abin ba koda uwar tashi bata da kyawun hali kuwa. Kamar dai abinda yake faruwa yanzu, wanda ba zan taba bari hakan ya faru ba. Mun gina amintacciyar rayuwa ni da yaran, they trust me, suna so na, suna girmama ni, ba zan taba bari hakan ya taba amintar mu ba.
Nace “shi yasa ka tsane ni kenan?" yayi shiru kan shi a kasa, “lokacin da naji labarin zaki auri Dad dinmu, frankly naji haushi. Me yasa muna kallon ki a matsayin yaya a gare mu zaki buge da auren Abbu? Daga baya kuma sai na fara tunanin hakan ai ba laifi bane ba, kuma zamu zama muna tare dake a koda yaushe saboda believe me muna son ki wallahi. Har lokacin da muka zo gidanki ina cikin confusion, daga karshe dai nazo nayi concluding cewa Kaddarar ki ce hakan don haka na kauda tunanin komi a cikin raina nayi niyar rungumar ki da zuciya daya. Saboda haka ne ma nayi niyar sa Abbu ya kaimu gidan ki mu yini in kuma baki hakurin abinda ya faru ranar farko da muka je gidan ki. Sai kuma na kare da jin maganganun dasu Abbun suke yi..., I was afraid! Naji tsoron cewa zaki iya sa wa Abbu ya tsani Mommy ya daina kula ta, muma yazo ya tsane mu ya daina son mu sai ke da baby idan kin haihu..., irin yadda Daddyn su abokina Ameer ya musu lokacin daya kara aure!".
Na fahimci irin tsoro da fargabar da yake ciki, na matsa tare da kamo hannun shi sosai. Nace “look Abdul, ni ba irin matar Baban su Ameer abokin ka bace kaji? Ba zan taba bari wani abun cutarwa yazo kusa da ku ba balle in cuce ku da kaina. Sannan Abbun ku yana son Mommyn ka kaji?" yaron ya kalleni sosai with so much hope in his eyes sai da naji kamar zan yi kuka. Fuskar shi ta washe da murmushi, “da gaske Anty Nafeesah?" na daga mishi kai da sauri, “sosai ma. Yafi son ta akai na ma. Kawai ranar ai ya fada min, yana so ne yaga abinda zata yi ne shi yasa yace haka. Wasa yake mata!!" na karasa maganar cikin cije baki.
Yayi ajiyar zuciya, “har naji dadi wallahi, da har na fara ji Abbu ya fara bani haushi!" da sauri nace mishi “kul! Kar ka sake maimaita irin haka kaji Abdul? Ko me iyayen mu suka mana bamu da damar jin haushin su a cikin ranmu kana jin mu? Duk abinda zasu yi suna da dalili don haka mu dinga musu uziri ka gane?" ya gyada kai cikin fahimta, “na gane. Nagode sosai Anty Nafeesah! Kiyi hakuri kuma" na shafa tattausar tattaurar sumar kanshi ina murmushi, “are we good now?" shima ya gyada kai yana murumushi. Nace “zo mu koma cikin gida kaga yamma tayi kila su Mommyn ka suna neman ka. Kada fa ka sanya damuwar komi a cikin ranka kaji?" ya gyada kai. Naja hannun shi muka tafi.
Aikuwa su Anty Mubeenah na waje suna neman shi, ganin mu tare fuskar ta ta danyi frowning da ban san ko na menene ba. Na daure duk da sanyin da gwiwa ta tayi muka karasa har gaban motar su, wanda kafin muje sun shige ciki, Abdullahi ya bude baya ya shiga na leka ta jikin taga ina musu Allah ya kiyaye hanya, Anty Shakira da yaran suka amsa cikin fara'ah yayin da mai gayya Mubeenah ta dauke kai gefe, ni dama nasan za a rina. Suka ja motar suka tafi, na sauke ajiyar zuciya a hankali na juya zuwa cikin gidan, lokacin an fara kiran Sallar Magriba.