Sashe 52
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read
Na kasa tantance abinda ke zane akan fuskar Abbu a lokacin, murmushi yake yi sosai, amma zan iya rantsewa akan cewa na hango alamun moistness a cikin idanunshi, ban san me zai faru ba nan gaba, ban san ya zamu kare da Mommy ba sai dai irin farincikin dana gani a tattare da Abbu yasa naji duk wata fargabata ta barni, idan dai har zan dinga ganin irin wannan kallo daga Abbu to ban damu da duk abinda zai faru ba, nasan cewa murmushin Abbu ya ishe ni. Ya dauki mintuna da dama bai yi magana ba ina jin yana containing farin cikin dake cin shi ne, yayi gyaran murya yace "nagode sosai Nafeesah, amincewar ki da yardar ki a gare ni sun dadada min sosai you have no idea, in shaa Allah na miki alkawarin ba zaki yi nadamar aurena ba, Mrs. Ibrahim Galadanchi!" na kai hannuna biyu na rufe fuskata dasu ina dan murmushi yayin da naji Abbu yana er dariya, yace "why? Baki son sunan ne ko me?" naki bude fuskata balle in kalleshi, yace "idan baki son sunan it's okay, but bude mun fuskar ki plss" na kara kankame fuskar tawa, ina zan iya fuskanta Abbu a yanzu? Ina jin lokacin daya tashi daga inda yake ya dawo gefena ya zauna kamshin turaren shi ya cika min hanci, yace "zaki bude da kanki ne ko sai na janye da kaina?" a hankali na janye hannuwan nawa sai dai fuskana tana kasa, a yadda nake jina a lokacin nasan ba zan taba iya hada ido dashi ba. Ya rankwafo da kanshi saitin fuskata, da sauri na daga kaina na kalleshi cikin sa'a muka hada idanu dashi, wayyo Allah! Kasa tsaye in shige. Ban taba ganin Kwarjinin da yayi mun a lokacin a tattare dashi ba, wani irin magnet naji ya fara fuzgata yana kokarin hada ni dashi, da sauri na mike tsaye ina lalubar jakata tun kafin in kai ga yin abinda zan zo ina dana sani gwara in bar office din. Abbu ya bini da ido yana frowning, na tsaya a gaban shi ina rataye jakata a kafada kaina a kasa, nace "umh.... Zan tafi... In... na da class anjima" ya kalli agogon hannunshi tare da dan jan siririn tsaki, "so nayi mu tattauna game da yadda zamu tsara rayuwar auren mu dake fa, amma ba komi there's always a second time. Amma zan sanar da Daddynki dai" na kalleshi da sauri ina zaro idanu, "tun yanzu?" yayi scrunching din brows dinshi, "tun yanzu? Me kike nufi?" nayi kasa da kaina "na ga kamar yayi kusa ne" ya girgiza kanshi "bai yi kusa ba Nafeesah, na gaya miki na kagauta ki zama mallakin, ni da so samu ne ma sai ince satin sama a daura mana aure in killace ki a gidana, Ya Allah! Na tabbata burina ya gama cika, I wouldn't ask for anything sai dawwama dake a gidan Aljannar Firdaus" sai kawai na daga kafa na fara tafiya, Anya Abbu ne? Ban san me ya shiga kan shi da kwalwar shi ba a Kwanakin nan sai ya dinga min wasu maganganu da suke saka ni cikin ramin matsananciyar kunyar shi. Ya mike tsaye, "tunda baki son yin hira dani bari in maida ki hostel to" na fita na tsaya a bakin kofar Ofishin ina jiran shi, ya fito daga ciki ya rufe office din yayi gaba na bishi a baya har inda yayi parking din motar shi. Muka shiga yaja motar, a hankali muke tafiya yana ja na da er hira. Duk yadda nake kauce-kauce da kare-karen fuska sai dana dawo ina dariya, kafin mu karasa hostel na sake daga awkwardness din daya dabaibaye ni, a cikin motar ma mun jima muna hira a gaban hostel dinmu har sai da aka fara kiran sallar azuhur sannan muka yi sallama. Na bude murfin motar ina ce mishi ya gaida su Hafsy, yace "me zaki ce musu bayan tunda kika zo baki ziyarce su ba? Fushi ma take yi dake don ki sani... Koda yake ai na kusa ciccibar ki in kai mata ke cikin gidan gabadaya, ki fara haifo mata kanne nasan zata yi farin ciki sosai, zan gaya mata ta daina fushi dake haka nan" ni dai na ida sa kafata waje na fita ina dan murmushi, da gaske Abbu ya canza daga cool and calm Abbun dana sani zuwa Romantic, wanda yake fadar duk maganganun da suka zo bakin shi ba tare da yayi la'akari da cewa sun girmi kunnuwana ba. Ya dan leko da kanshi ta cikin motar, "baki ce komi ba fa" na dan juyo na kalleshi tare da haske shi da murmushi na juya na shige cikin hostel, ina jin hot gaze dinshi a kaina har na yi nisa a cikin hostel din, na tura kofar dakin na shiga. Firdausi na zaune akan kujera da littafi a hannunta tana karatu, ta dago tana min sannu da zuwa na amsa, kallona ta cigaba dayi kamar wadda taga wani bakon abu a jikina, na rataye jakar hannuna a jikin hanga na kalleta, "wannan kallon naki lafiya dai koh?" tayi murmushi tace "you are blushing! Did someone propose to you??" na kalli kaina a cikin madubi, I couldn't help the chuckling daya fito min, na kalleta ina murmushi "Ina ga dan zafi zafin da ake yi ne kawai" ta kalleni tana murmushi tare da gyada kai ta maida Idanunta ga littafin hannunta. Nima nayi murmushin na fita naje nayi alwala na dawo nayi sallah, kafin in gama Firdausi ta dafa mana indomie ina gamawa muka ci na sake fita wajen lecture.
A daren ranar sai ga wayar Daddy ta shigo, na daga wayar cikin sanyin jiki da faduwar gaba. Ina gaida shi ya amsa ya dora da fadin, "Ibrahim ya kira ni yanzu yana fada min wani labari" na sadda kaina kasa kamar ina gaban shi, "kayi hakuri Daddy" ya danyi murmushi, "meye kike bani hakuri dear? I just call to know that you are okay with it. Are you sure zaki iya?" na gyada kaina amma ban yi magana ba, yace "naji dadin zabin da kika yanke sosai Uwata, naji dadin cewa mutumin da kika zaba ya zama abokin rayuwar ki Ibrahim ne, naji dadin cewa zan barki a hannu na gari kuma na kwarai, nasan ba zan taba yin fargaba game da yadda kike ba saboda na yarda da Ibrahim. Allah ya miki albarka Nafeesah" naji hawaye suna kokarin cika min ido, da ace ina kusa dashi da sai na rungume shi, nace "I love you Daddy, nagode" yace "You are all we have Uwata, dole mu so farincikin ki, ina Alfahari dake" nace "nima haka Daddy.... Amma Mommy fa?" yayi kasa da murya nasan sirri yake nufi, "Mommy dinnan taki fa sai a hankali, tun dazu take hawa tana kumbura kamar fulawa daga mata maganar wae ai ita bata yarda ba cin amana zata yi, shine nace mata idan haka ne itama za a turo mata yarinya kamar ki idan tayi watanni sai in aureta, don Allah ba anyi 1-1 ba?? Sai kawai ta hau kumbure-kumbure, yau ko magana bata min ba dana dawo daga aiki" duk da banji dadin abun ba sai dana yi er dariya nace kai Daddy! Yace "it will be better idan baki kira ta ba for two days, zan yi kokari in ga cewa na ganar da ita abinda take fahimta" nace toh Daddy. Yace good girl, kije kiyi alwala ki kwanta, nasan kina da darasi da safe nace "exactly Dad, goodnight" muka yi sallama na ajiye wayata jikina a sanyaye. Na jima a zaune ina tunanin yadda zan yi idan Mommy taki bamu albarkarta game da auren nan, ni dai nasan cewa ba zan iya auren Abbu ba tare da yardar Iyayena ba gaskiya. Na tashi naje na dauro alwala nayi shirin kwanciya barci. Dana daga wayata naga message din da Abbu ya turo min mintuna biyar da suka wuce, cewa yayi; "A lokacin da kowa yake neman makwanci da niyar warware gajiyar data addabe shi, a daidai lokacin bawan Allah Ibrahim yake karawa kan shi wani tarin gajiyar, why? Saboda bashi da makwanci kwanciya balle filon tada kai. Ina fata wadda take karanta sakon nan zata yi gaggawar kasancewa tashi ko zai samu sanyin rai dana zuciya a tare dashi. Sai da safe, lots of love and kisses" n zan iya rantsewa naji saukar lebba a kumatuna, na kai hannu na dafe wajen ina duba gefe na, dariya na saki tare da dan dukan goshi na, silly me! I am even expecting him to kiss me, woah!! 'Goodnight' kawai na tura mishi as a reply na kwanta tare da lumshe idanuna. Barci mai dadi cike da kyawawan mafarkai ya daukeni ni.
~So how are you doing outta there Abbu and Nafee's fan??
#TeamAbbu
#OneLove
*♡Jeedderh♡*
[12/25/2017, 00:47] Hauwa-Jedderh💕: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*♡41♡*
A daren ranar sai ga wayar Daddy ta shigo, na daga wayar cikin sanyin jiki da faduwar gaba. Ina gaida shi ya amsa ya dora da fadin, "Ibrahim ya kira ni yanzu yana fada min wani labari" na sadda kaina kasa kamar ina gaban shi, "kayi hakuri Daddy" ya danyi murmushi, "meye kike bani hakuri dear? I just call to know that you are okay with it. Are you sure zaki iya?" na gyada kaina amma ban yi magana ba, yace "naji dadin zabin da kika yanke sosai Uwata, naji dadin cewa mutumin da kika zaba ya zama abokin rayuwar ki Ibrahim ne, naji dadin cewa zan barki a hannu na gari kuma na kwarai, nasan ba zan taba yin fargaba game da yadda kike ba saboda na yarda da Ibrahim. Allah ya miki albarka Nafeesah" naji hawaye suna kokarin cika min ido, da ace ina kusa dashi da sai na rungume shi, nace "I love you Daddy, nagode" yace "You are all we have Uwata, dole mu so farincikin ki, ina Alfahari dake" nace "nima haka Daddy.... Amma Mommy fa?" yayi kasa da murya nasan sirri yake nufi, "Mommy dinnan taki fa sai a hankali, tun dazu take hawa tana kumbura kamar fulawa daga mata maganar wae ai ita bata yarda ba cin amana zata yi, shine nace mata idan haka ne itama za a turo mata yarinya kamar ki idan tayi watanni sai in aureta, don Allah ba anyi 1-1 ba?? Sai kawai ta hau kumbure-kumbure, yau ko magana bata min ba dana dawo daga aiki" duk da banji dadin abun ba sai dana yi er dariya nace kai Daddy! Yace "it will be better idan baki kira ta ba for two days, zan yi kokari in ga cewa na ganar da ita abinda take fahimta" nace toh Daddy. Yace good girl, kije kiyi alwala ki kwanta, nasan kina da darasi da safe nace "exactly Dad, goodnight" muka yi sallama na ajiye wayata jikina a sanyaye. Na jima a zaune ina tunanin yadda zan yi idan Mommy taki bamu albarkarta game da auren nan, ni dai nasan cewa ba zan iya auren Abbu ba tare da yardar Iyayena ba gaskiya. Na tashi naje na dauro alwala nayi shirin kwanciya barci. Dana daga wayata naga message din da Abbu ya turo min mintuna biyar da suka wuce, cewa yayi; "A lokacin da kowa yake neman makwanci da niyar warware gajiyar data addabe shi, a daidai lokacin bawan Allah Ibrahim yake karawa kan shi wani tarin gajiyar, why? Saboda bashi da makwanci kwanciya balle filon tada kai. Ina fata wadda take karanta sakon nan zata yi gaggawar kasancewa tashi ko zai samu sanyin rai dana zuciya a tare dashi. Sai da safe, lots of love and kisses" n zan iya rantsewa naji saukar lebba a kumatuna, na kai hannu na dafe wajen ina duba gefe na, dariya na saki tare da dan dukan goshi na, silly me! I am even expecting him to kiss me, woah!! 'Goodnight' kawai na tura mishi as a reply na kwanta tare da lumshe idanuna. Barci mai dadi cike da kyawawan mafarkai ya daukeni ni.
~So how are you doing outta there Abbu and Nafee's fan??
#TeamAbbu
#OneLove
*♡Jeedderh♡*
[12/25/2017, 00:47] Hauwa-Jedderh💕: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*♡41♡*