← Book details Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 88

Sashe 60

Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read

Shiru muna cin abinci a cikin restaurant din da muke zuwa lokaci zuwa lokaci, baka jin karan komi sai karan cokali da plate din dake gaban Abbu yana cin abinci yayin da na kurawa nawa plate din idanu kawai, duk yunwar da nake ji sai naji ta tafi, babu space din komi a cikina a lokacin sai na numfashin da nake shaka. Fushin Abbu ya takura ni, ya tsorata ni, gabadaya na rasa abinda yake min dadi a lokacin. Tunda ya sadda kanshi ga plate din gabanshi bai dago idanunshi ba, na kula yana gudun kallona ne kamar yadda na kula cusa abincin kawai yake yi ba wai don yana jin dadin shi ba. A hankali nace “Abbu!" ya dakata da cin abincin da yake yi kafin ya dago ya kalleni, kyawawan idanuwan shi da a koda yaushe suke farare tas-tas suna sheki suna kallona cike da so da kulawa, sun rine daga ainihin kalar su zuwa ja-brown, gaba na ya fadi sosai ban taba ganin wannan kamar ta Abbu ba, ya maida kanshi kasa ya cigaba da cin abincin. Nace “Abbu don Allah kayi hakuri kar kayi fushi dani, kawai Harith yazo ne mu gaisa ba wani abu ba please" bai yi magana ba kamar yadda bai dakata da abinda yake yi ba, na sake cewa “kaji?? Please Abbu na!!" duk da cewa sau tari ya kan nuna bai son sunan amma na kula jin sunan daga bakina yana dadada mishi rai sai dai da alamun hakan bai yi tasiri ba yau, babu murmushin nan daya saba yi, bai yi scowling dinnan ba yana kallona dangerously kamar zai zuke ni da idanunshi, instead sai kawai ya kalleni yayi wani murmushi da bai ma gama hade fatar bakin shi ba balle fuskarshi, muryar shi tayi can kasa kamar wanda yake suffering daga cutar mura yace, “eat, Nafeesah!" ya cigaba da cin abincin, sai kawai naji gwiwoyina sun sage, me ke damun Abbu ne yau? Gabadaya ya wani rikice min kamar ba Abbun dana sani ba, ban taba ganin wannan Abbun da yake gabana ba don haka ne naji nima na gigice sosai. Na xuba duka tafukan hannuwa na biyu a cikin kumatuna kawai na kura mishi idanu, ban damu da cewa hakan zai takura shi ba ko kuma idon mutane dake cikin restaurant din, ni dai fata na da burina shine in karanto abinda yake damun Abbu inyi gaggawar magance mishi koma meye sai dai ban karanci komi ba, ya gama cin abincin ya dago ya kalli plate dina sai kuma ya tashi, yaje ya biya kudin abincin suka dawo tare da yaron wajen aka maida nawa abincin cikin take away muka fita daga restaurant din. Ko a cikin mota ma haka tafiyar ta kasance, yayi wani kicin-kicin da rai kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa. Har muka je bakin hostel ya samu waje a parking lot yayi parking. Na dan saci kallonshi kafin na yunkura da niyar fita daga cikin motar ya katse ni ta hanyar kiran sunana, “Nafeesah!" na dakata amma ban juya na kalleshi ba, na tsani ganin expression din fuskar shi kamar yadda na tsani mutuwata. Murya a hankali yace “kiyi hakuri don Allah" cike da tsananin mamaki na juya na kalleshi, fuskar shi nuna how apologetic he was, nace “me ya faru?" ya girgiza kanshi, “na saka ki cikin damuwa saboda son rai irin nawa, you didn't do anything wrong amma na saka ki gaba ina hade miki fuska, na..." ya sadda kanshi kasa saboda maganar data kakare mishi ni kuma na kura mishi idanu, he looks soooooo lovely and adorable, Anya soyayyar Abbu zata barni in rayu cikin dadin rai?? Ya sake dago kanshi ya kalleni, wannan karon babu bacin rai dake tattare dashi sai idanuwanshi dake nuna tsananin so, kauna, kulawa da wani abu kamar tsoro? I'm not sure. Yace “I was afraid" cikin mamaki na kalleshi nace “of what?" ya girgiza kanshi, “I don't know. Kawai tunda na ganki da wani a tsaye naji wani tsoro ya dabaibaye ni, I really cherish you alot Nafeesah, I was afraid of you leaving me ko wani ya juye miki tunani daga gareni, idan hakan ya faru ban san ya zan yi ba!" wannan ba Abbu Baban su Hafsat da Abdullahi bane, wannan Ibrahim ne a zamanin da yake kan ganiyar kuruciyar shi, na muskuta ta yadda zan fuskance shi sosai, “ni ko wanene kwanakin baya yake cewa ba zai zauna yana soyayya irin ta yara ba? I wonder ko wace kalar soyayya ce wannan?" ya dan jefe ni da harara, na danyi murmushi kafin nace “nima idan hakan ta faru ban san yadda tawa rayuwar zata kasance ba Abbu, idan hakan ta faru I'll be more shattered than u, gwanda kai kana da mata da ‘ya‘y'a ni kuwa dama daga kai sai Mommy da Daddy nake dasu" ya kura min idanu kaman wanda yake kokonton abinda nace, na saki murmushi reassuringly “kada ka damu Abbu, in shaa Allahu abinda kake tsammani ba zai taba faruwa ba, I am yours, and I'll always be in shaa Allah!" ya lumshe idanunshi for a second, daya bude duk wani duhu da rikicin dake cikin idanunshi sun yaye, damuwar data lullube shi ta tafi, Abbuna ya dawo kamar yadda yake, ya saki kayataccen murmushin nan nashi, “you are almost mine dai but at least am relieved, God! Kin tsorata ni wallahi, amma do you really mean what you said?" wai sai a lokacin naji kunya ta dabaibaye ni, nayi gaggawar Kai hannu na rufe fuskata, ina jin er dariyar da yayi, “ana so ana kaiwa kasuwa.... Zaki yi bayani ne idan aka miki snatching" fuskana na cikin tafukan hannuna nace “ai babu wanda ya isa ya kwace min abinda nake so!" ya rankwafo kanshi kusa dani yana wani smirking, ina kallonshi ta yatsun hannuna, yace “Ashe dai ana so na?" da sauri na bude murfin motar na fita na barshi yana dariya, da alamun abin ba karamin dadi yake mishi ba, haka kawai naji murmushi ya subuce min. Ya fito daga cikin motar shima, “tambayar ki fa nayi baki amsa min ba" inaa, ai nayi gaba abina. Yace “to tsaya ki amshi abincin ki" naja tunga na tsaya, ina ji ya bude motar ya dauko takeaway din ya tako zuwa inda na tsaya ya miko min, nasa hannu na karba ina wani sinke fuska, ya wani kuta kamar gaske “zaki yi bayani ne wallahi, sai ki wani dinga sinke fuska kina cuta na wai ke kunya, Allah ya kaimu ranar da zaki shigo hannuna" na saki murmushi, yace “dariya ma kike yi koh? Allah Nafeesah kina bukatar in gyara miki zama, dazu kin ce wai I was cute, yanzu kince ina soyayyar yara and ina magana kina dariya koh?? Sai na tabbatar dana hukunta bakin nan naki da baya jin magana wata rana" dariya na dan saki kasa-kasa, da alamun yau en rigimar ne akan Abbu. Naci gaba da tafiya abina, ya tsaya a inda yake yana magana cikin korafi, “wato ma tafiya kika yi kika barni koh? Ba komi, sai kinyi sati biyu baki sake ganin mai kama dani ba, kai sai ranar auren mu zaki sake ganina ma" na juyo ina kallonshi nace “to ka gaida gida dasu Hafsy" yayi wani irin chuckling daya sa ni bude baki ina kallonshi, ji nayi kamar in ruga da gudu in fada cikin faffadan kirjin shi, sai nayi murmushi kawai tare da girgiza kaina na wuce cikin hostel. Kafin in karasa daki kiran Anty Raheena ya shigo wayata, na daga muka gaisa da ita. Tace wai kira tayi in fada mata size dina zasu siyo under wears da za a saka a cikin kayan lefena, ni wallahi kunya ma ta bani. Da kyar na iya bude baki na fada mata, ko sallama bamu yi ba na kashe wayar.
Bayan kwana biyu aka kai akwatina gidanmu, guda takwas sai kit, sai ta waya Anty Uwani ta turo min akwatunan na gani, wasu azababbun akwatuna kirar kasar Italy na zallan fata kalar pink ne, kayan dake ciki kuwa kama daga shadda, lace, materials, atamfofi, takalma ma kadai daga na kamfanin vincci, dg, poshter, ga jakunkuna da jewelries duka babu kanana gaskiya ba karamin kokari Abbu yayi ba wajen hada kayan nan, na dinga gyada kai kawai lokacin dana dinga duba kayan, ‘kaya kam sun yi kyau gabadaya babu na yar wa sai dai fatan in more su a gidan aurena cikin tattali da soyayyar juna ni da mijina'., a cewar Anty Uwani, ni kam na amsa da ameen a cikin raina.

☆☆☆☆☆☆
Chapter 60 · 0% Book details