← Book details Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 88

Sashe 67

Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read

A haka har muka gama exams dinmu, ina ta kauce-kauce yayin da Abbu bai fasa abin shi ba sai ma abubuwa da suke karuwa kullum. Kwana biyun nan ya dameni akan wai shi fa lallai sai ya kaini naga gidan mu, ni kuwa nasan muddin na taka kafa naje gidan to sunana sorry, kila warning din dasu Ni'imah da Firdausi suke yi mun na in daure kar in tare da ciki ya tabbata. Tun a ranar da nayi exams dina na karshe na fara hada kayana, na kira Daddy a waya yace washegari zai turo a zo a dauke ni saboda ranar sai da yamma muka gama exams din, nace mishi don Allah ya turo direban tun da safe mu tafi, a matukar kagauce nake da in tafi gida, I have to clear my thoughts and brain kuma nasan gidanmu ne kawai zai bani wannan natsuwar, ga kewar su Daddy da nake yi kamar me, hakika nayi kokari, watanni biyar rigis ba tare dana saka su a cikin idanuna ba. Na kira Ramlah da tace tare zamu wuce Kadunar da ita na sanar da ita, tace zata shirya sai mu biya ta gida mu dauketa nace to muka yi sallama.
Karfe tara na safe kayana sun kammala waje daya, nayi wanka na shirya cikin riga da siket na atamfa, hijabin data zame min mayafi na ajiye a gefen gado a linke, na dauki wayata na fara buga game don ya dan kashe min time kafin direba ya zo. Kiran Abbu ya shigo wayata, gabana ya fadi sosai gabadaya na manta bamu yi sallama dashi ba saboda doki, na dauki wayar na kara a kunnena, “meet me at my office" kadai yace ya kashe wayar, na bi wayar da kallo kamar ba zan tashi ba, can kuma na mike na saka hijabina, Firdausi bata dakin taje rubuta jarabawa don haka na rufe dakin na fita. Zaune na same shi akan kujera fara dake a tsakiyar ofishin da alamun jirana yake yi, na maida kofar na rufe na zauna akan kujera dake fuskantar shi na zauna, fuskar shi sam babu yabo babu fallasa hakan yasa naji sanyin jiki ya mamaye ni, Allah dai ya taimakeni muyi rabuwar aminci yau don na kula da cewa rigima yake ji yau. Murmushi nayi a sanyaye nace “Abbu ina kwana? Ka tashi lafiya?" yace “ke zan tambaya ai, amma ni kin tambayeni tashina lafiya bayan kina neman hana min abinda yake nawa ne?" na dan zamo daga kan kujerar da nake zaune nace “don Allah Abbu kayi hakuri, idan kayi hakuri ma duka kwanaki nawa suka rage kafin a kawo maka ni gabadaya kayi yadda kake so dani?" ya lumshe idanun shi tare da maida kanshi ya jinginar da kujerar da yake zaune, “I tried Nafeesah, I really do. But I can't anymore, all I ask for u is just half an hour, please ki zo muje gidana, I so badly want you Nafeesah!!" na kura mishi idanu, idanun shi a lumshe suke har lokacin, Abbuna ne a gabana yake rokona, da ace zan iya da na mishi abinda yake so domin samun farin cikin rayuwar shi, sai dai ba zan iya din bane, I'm still not ready for it. Mikewa tsaye nayi a hankali, hanya mafi sauki in bar mishi ofishin kafin in kara bata mishi rai, nasan ba zai fasa tambayana ba, ni kuma in yaci gaba da tambaya it's either inyi abu daya cikin biyu; ko dai in sallama mishi ko kuma inyi denying wanda duka cikin biyun babu wanda zai mun dadi, nace “Abbu don girman Allah kayi hakuri, kayi hakuri na wata da watanni ma balle na en kwanaki? I am very sorry, zamu wuce Kaduna yanzu don Allah kar kayi fushi dani Abbu..." na juya cike da sassarfa zan fita. Ban ji lokacin daya tashi tsaye ba sai maganar shi dana jiyo daga bayana, “Please Mana Nafeesahh!!" Ya fada cikin wata irin murya wadda ta narke cikin tsantsar qauna da soyayyah. Kaina na fara girgizawa a tsorace, "Bazan iya ba. Kai fa Abokin Babana ne please kayi hakuri, bazan iya ba wallahi!!" idanunshi ya zuba min wadanda suke a lumshe kamar na mashaya, dama a yawancin lokuta a haka suke, sai dai na yau sun banbanta dana sauran lokutan. Na yau cike suke da wata irin soyayyah, zallar qauna, pure lust, I can sense them radiating from his body. Muryarshi ta kara yin kasa sosai “ina tunanin mun riga da mun gama wannan maganar Nafeesah? saboda Allah mutane nawa kika san sun yi aure irin namu kuma suna zaune lafiya har ma da zuria a tsakaninsu, ko a cikin tarihi ki duba fa, Sayyadah Aisha RTA diyar Sayyidina Abubakar ce wanda ya kasance babban Amini makusanci a wajen manxon mu (S. A. W) nasan kin san da haka ba sai na sake gaya miki ba" maganganun shi haka suke sai dai na kasa convincing kaina da zuciyata" nace “yeah, I know.., I just need time please kayi hakuri" ya girgiza kai, “na gaya miki ba zan iya bane Nafeesah, it's not as if wani sabo ne nake shirin aikatawa" Kai na ci gaba da girgizawa hawaye na sauka akan kumatuna, ya zanyi da raina da rayuwa ta ne ni kam? Ban san ya aka yi ba sai ganin shi nayi a gabana, kafin inyi wani yunkuri yayi pinning dina da bangon ofishin, "I love you Nafeesah....I want you n I know you do, u just don't want to admit it!" "no.... No... I... I" na fara fada cikin in'ina kafin inji wasu tausasan lebba sun hana ni karasa maganar. Lebena na kasa ya kamo ya fara tsotsa cikin wani irin passionate kiss, a hankali na lumshe idanuna tare da kamo nashi leben na sama nima na fara tsotsa, ya saka hannu daya ya zagaya dashi ta kuguna ya kara matso dani zuwa gare shi tare da zura harshen shi cikin bakina muka fara hadamammen kiss, ihu ake a cikin kaina da kwalwata, “Ya Allah! What am I doing? He's my father's Friend for Heaven's sake!! Cewar wani sashe na zuciyata, but hell! I couldn't let him go, sai ma kara rike shi da nayi tsam....

Karan da wayata ta dauka baby kakkautawa ne ya dawo da hankulanmu cikin ofishin, a matukar kunyace na janye jikina daga nashi yayi saurin janyo ni ya rungume a cikin kirjinshi, duk yadda naso in kwace abin yaci tura ina ji ina gani haka na Hakura har wayar ta gama burari ta katse, numfashi yake saukewa a hankali har ya dawo cikin natsuwar shi, ya hade goshina da nashi yana kallona ni kuwa naki hada idanu dashi, murmushi ya saki a hankali, “kin gani koh? We need each other Nafeesah, amma kina hana kan ki abinda zuciyar ki da gangar jikinki ke so, why?" a hankali na daga baki nace “kayi hakuri" ga mamakina sai naji yace “na hakura Nafeesah" na daga kai cikin mamaki na kalleshi, ya daga kafada, “to me zan yi idan ba hakurin ba? Kin san cewa ba zan taba tursasa ki ga yin abinda baki so ba, zan jira har a kawo ki din sai dai kada ma ki roke ni wani abu a wannan lokacin don ba zan ji ki ba...., muje in kaiki hostel din" ya zari makullin mota ya fita, na bishi da kallo ina murmushi, saukin kan Abbu yana burge ni sosai da sosai, Allah ya yaye min fargabar nan da wasi-wasi da nake ji ko na samu na faranta mishi rai kamar yadda yake kokarin faranta min. Na bi bayanshi na fita daga ofis din ya rufe muka tafi. Koda na duba miss call din da aka min direban da daddy ya turo min ne, na kira shi ya sanar dani ya iso nace mishi gani nan. Koda muka isa mun dauki lokaci muna hira da Abbu kafin muka yi sallama dashi akan cewa zamu yi waya, ya kama hannuna yayi kissing bayan hannun kamar yadda ya mayar dashi al'adar shi tun ina jin abun banbarakwai har nazo na saba da hakan yace “m gonna miss you baby" nace “me too" a kunyace, yayi murmushi, da haka yaja motar shi ya tafi. Firdausi ta taya ni dauko kayana muka lode su a bayan booth, daga nan muka yi sallama da ita ita sai nan da kwana biyu zata gama nata exams din, na shiga mota direba yaja muka wuce Kaduna bayan mun dauko Ramlah. Karfe biyu a Kaduna ta mana, da gudu na shiga gidan ina ihun kiran Mommy, ta fito daga kicin tana goge hannunta da kicin towel, na tafi da guduna na rungumeta ina murna, ta janye ni daga jikinta tace “ke tafi can ni, wannan yarinya ban san yaushe zaki girma ba ni kam" na kara shigewa jikinta ina tsalle abina, sai da Ramlah ta shigo sannan na sake ta. Suka gaisa da Mommy kafin muka shiga dakina muka yi wanka muka yi sallah, sai a lokacin na kira Abbu na sanar dashi mun sauka, nan muka danyi hira muka yi sallama sannan muka fita falo muka ci abinci. Da yamma Daddy ya dawo muka sha hira da murnar ganin juna, ko da dare ma dai hirar muka yi har sai da dare yayi sannan na musu sallama na wuce dakina. Washegari Anty Uwani tazo ta daukemu ni da Ramlatu muka tafi gidanta bayan ta sa mun dauki kayan sawar mu kala biyar, ban san me zamu yi ba na dai ji suna maganar Gyaran jiki ita da Mommy ni kam ban maida hankali wajen sanin lallai sai na san me zamu yi ba.
#TeamAbnaf
#OneLove

*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA....!*

*©°•Jeedderh Lawals•°*

*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋

*GARGADI!!: Wannan littafi ko ince labari Mallaki na ne wanda ni nake cracking din kwalwata in turo muku shi, lokacin da zan fara babu wanda ya bani izini game da yin haka saboda haka ni nake da right din rubuta shi. On that note nake rokon duk wadda/wanda take/yake re-editing number din pages din littafina ya/ta daina. DON ALLAH a daina! Ana causing confusion a tsakanin makaranta. Thanks and Stay Blessed!!*
Chapter 67 · 0% Book details