Sashe 43
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kamar yadda yake Al'adar gidan mu, bayan an gama muna haduwa a dakin Daddy a yawancin darare, wani lokaci muyi kallo wani lokacin hira, sometimes ma musamman idan daddy yana ayyuka zaku ga kowa abinda ke gaban shi kawai yake yi. Ina zaune a kasan kujera ina browsing Mummy kuma tana kan kujera a xaune, Daddy ya fito daga bedroom din shi ya zauna a kusa da Mommy. Daddy ya kira sunana in a serious tone, "Uwata" na amsa a nutse tare da kallon shi, yace "last two weeks da suka wuce Ibrahim ya same ni da wata magana mai Muhimmanci" yayi shiru yana kallona yayin da zuciyata ta hau duka kamar zata fado kasa, ya cigaba da magana "Yace wai Yana So Ya Aure Ki! Ni kuma nace mishi sai naji daga bakin ki don bana son tursasa ki akan abinda baki da niyar yi, me kika ce? Zaki Auri Ibrahim?" Na sadda kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna, ban san abinda yakamata in ce ba, ina son Abbu kuma Ina son Auren shi? Ina son Abbu amma ina tunanin auren shi is not a good idea? Ko kuwa me zan ce?? Mommy tayi saurin riga ni magana, "Haba Abban Ummiey, kaima kasan cewa wannan ba abu bane mai yiwuwa. Shi bai yi tunanin abinda zai zo ya dawo bane ya kirkiro wannan magana? Wannan abu ba zai yiwu ba sam!" duka ni da Daddy muka kalleta, fuska a hade sosai take yin maganar, daga ganin yanayin idanunta nasan cewa she is strongly against it, sai jikina ya kara yin sanyi akan na da. Daddy yace "me kike cewa ne haka Habibty?" tace "Abinda ya kamata mana, Idan shi idanun shi sun makance da cin Amana bai kamata naka su rufe ba Abban Ummiey. Haba! Ace daga tura yarinya yin IT na wata shida kawai sai aji wai ta buge da aure mai gida? Kaima kasan cewa wannan ba abu bane da zai yiwu ba, sai dai idan so kake ka saka mu a bakin duniya kuma" Daddy ya danyi murmushi, "sai dai idan basa son junan su Habibty, amma idan suna so then who cares about what people will say? Su mutane ai aikin su kenan ina tabbatar miki idan kika ce zaki biye ta mutane to numfashi ma sai sun miki izinin kiyi kenan?" Mommy ta hade fuska "na kula ga gaskiya nan kana gani kuru-kuru amma kana takewa, son Kai ne ko me? Aure dai Nafeesah da Ibrahim babu shi!! Ba zan taba bada hadin kaina ga cin amanar wannan da kuke shirin yi ba" Daddy yace "ke kuma kin ki fahimtar abinda soyayya zata yi da wannan ba zata iya ba, baki tsaya kinji ta bakin yarinya ba kin zauna kina ta tada jijiyoyin wuya, be it zaman aure ko cin amana kamar yadda kika ce don ni dai ban ga komi ba a ciki, ina ga ai ya rage ga yarinyar koh?" Mommy tace "ni nasan Ummiey ba zata taba aminta da hakan ba, ga samari nan bila adadin suna karakaina a kanta sai ta buge da wani can, ga mata ga 'ya'ya, abokinka kuma for that matter, anya Abban Ummiey ka duba maganar nan sosai?" Daddy ya kalleni yace "Uwata!" na daga kai na kalleshi, yace "kada ki damu da abinda take fada kin ji? Just tell me idan kina son Ibrahim kuma zaki iya auren shi" na kalli Daddy na kalli Mommy, toh fa! Ga sanyin Idaniyata guda biyu a gabana, ko wanne ya zuba min ido yana jiran amsa ta wanda nasan cewa amsar da zan ba daya daidai take da bacin ran daya, abinda na tsani gani da ji kenan a duniyata ace daya daga cikin Iyayena yana cikin bacin rai sabida ni. Abinda Mommy take fada gaskiya ne, shima Daddy akan gaskiyar shi yake, to me zan yi kenan? M I going to disappoint one of them? Ya Allah!! M extremely confused! Na samu kaina da girgiza kai wanda ni a karan kaina ban san dalilin yin hakan ba, Daddy yace "me kike nufi da girgiza kai, eh ko aah??" na sake girgiza kaina, "ban sani ba Daddy!" Daddy ya kura min ido na tsawon lokaci, yace "tashi ki tafi kawai Uwata, Allah ya zaba mana mafi alkhairi" ba musu kuma ba tare dana kara uffan ba na musu sai da safe na wuce dakina. Hannu dafe da kai na fada kan gadona na kwanta, na gaji! Na gaji haka nan. Haba! Kwana biyun nan kaina har ciwo yake yi tsabar tunanika da suka hana ni sukuni, abin ya ishe ni haka nan. Tashi nayi na fada toilet na dauro alwala na fito na haye kan Abin sallah, sallah na fara jerowa, dana gama na roki Allah akan yayi mun zabin abu da yafi alkhairi a cikin rayuwata, na gama nayi shirin kwanciya barci na kwanta zuciyata cike da sake-sake.
*****
Tsawon sati guda Daddy bai sake min zancen Abbu ba Mommy ma haka, haka a tsayin lokacin nan ban sake ji daga Abbu ba. Mun koma makaranta don dama ba wani hutu aka bamu mai tsayi ba. Ranar Asabar ina kwance a dakina da hantsi, mun gama waya da Harith kenan yana gaya min yadda suke shan fada shi da Ikram akan wai ni budurwar shi ce ni kuma ina ta shan dariya, na ajiye wayar tare da kurawa ceiling ido ina kallo. Wani kiran wayar ne ya dawo dani cikin hankalina, na mika hannu a sanyaye na dauki wayar. Ban san lokacin dana zabura na tashi zaune dangargar ba, Abbu. Kallon wayar kawai na dinga yi har kiran ya kusa karewa, in daga in ce mishi me? Koda yake na riga na gama yanke shawarar abinda nake ganin daidai ne a rayuwata so let's just finish this once and for all kawai, na karfafawa kaina gwiwa. Nayi gyaran murya tare da daga kiran na kara wayar a kunnena......
(Sorry for the short Chapter, m kinda busy this days wallah..)
So Kafin in tafi let me ask you this:
~Me kuke tunani game da Littafin Ni Da Abokin Baba Na so far?
~Me kuke gani ya kamata Nafeesah tayi a wannan lokacin, Accept or Reject?
~Who's siding with Mom, Dad? Raise your 👐 so I can count you guys lol
~Stay blessed and cool, see yah
Lots of Hearts and Flowers #teamAbbu 💞💞💐💐
*♡Jeedderh♡*
[12/16, 12:04] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*35*
*****
Tsawon sati guda Daddy bai sake min zancen Abbu ba Mommy ma haka, haka a tsayin lokacin nan ban sake ji daga Abbu ba. Mun koma makaranta don dama ba wani hutu aka bamu mai tsayi ba. Ranar Asabar ina kwance a dakina da hantsi, mun gama waya da Harith kenan yana gaya min yadda suke shan fada shi da Ikram akan wai ni budurwar shi ce ni kuma ina ta shan dariya, na ajiye wayar tare da kurawa ceiling ido ina kallo. Wani kiran wayar ne ya dawo dani cikin hankalina, na mika hannu a sanyaye na dauki wayar. Ban san lokacin dana zabura na tashi zaune dangargar ba, Abbu. Kallon wayar kawai na dinga yi har kiran ya kusa karewa, in daga in ce mishi me? Koda yake na riga na gama yanke shawarar abinda nake ganin daidai ne a rayuwata so let's just finish this once and for all kawai, na karfafawa kaina gwiwa. Nayi gyaran murya tare da daga kiran na kara wayar a kunnena......
(Sorry for the short Chapter, m kinda busy this days wallah..)
So Kafin in tafi let me ask you this:
~Me kuke tunani game da Littafin Ni Da Abokin Baba Na so far?
~Me kuke gani ya kamata Nafeesah tayi a wannan lokacin, Accept or Reject?
~Who's siding with Mom, Dad? Raise your 👐 so I can count you guys lol
~Stay blessed and cool, see yah
Lots of Hearts and Flowers #teamAbbu 💞💞💐💐
*♡Jeedderh♡*
[12/16, 12:04] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*35*