Sashe 84
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nace “haba wata biyar ne fa kawai ba wasu watanni ba, Allah na tuba ni ko da ‘yayan ki ma amarya zan dinga ce miki" taja tsaki, “to Allah ya kyauta miki, ya zancen turarukan da na turo miki? Kin amso su kuwa?" nace “ai da kanta ma ta kawo min har gida, Masha Allah sun yi kamshi sosai, kuma suna da kyau wallahi" tace “ai sai dana fada miki, yanzu ya za ayi wajen sauran abubuwan nan da nace a kawo min?" nace “idan na hada komi zan kira ita Nadiya din, sai ta taho miki dasu koh?" tace “to shikenan... Ina Abbu?" nayi murmushi, “Abbu yaje Beijing, suna da wani meeting ne a kamfani shine ya tafi" tace “ranar nan ai na kalli show din da aka bashi award din best prof na Universities din fadin Nigeria, naji ana maganar bashi VC a BUK koh?" na gyada kai, “yeah, he deserve it ai" tace “indeed, ana fadar ayyukan shi da sadaukarwar shi indai ta fannin karatu ne ai, Allah ya kara taimako" na amsa da “ameen" daga haka muka yi sallama da ita.
Toilet na fada na dauro alwala na fito nayi sallar La'asar, bayan na gama na hau en gyare-gyare a dakin babu kakkautawa da yake ba wani aikin yi ne dani ba duk da cewa ranar girki na ce dai. Wajen karfe biyar na tashi na shiga kicin din, Anty Mubeenah tana tsaye a gaban gas cooker da frying pan akai da alamu tana frying abu, na kalleta cike da mamaki ita kuma ta kalleni da blank expression, tunda muke da matar nan sai ranar na taba ganinta a kicin wai da sunan girki, sai na dake kawai na shiga cikin store na fito da duk abubuwan da zan bukata. Da yake babban kicin ne, kuma yawanci komi na amfani a kicin din guda biyu ne sai na kunna wani gas din na fara girkina. Cikin kankanin lokaci kamshi ya bade ko'ina na gidan, ta gefen ido nake kallon Anty Mubeenah ina wasi-wasin dalilinta na yin girki yanzu. Har ta gama soya dankalin ta juye a cikin plate ta kashe gas din ta fita, na tabe baki naci gaba da aiki na. Ba a jima sai gata ta fado kicin din, ta tangwarar da plate din a cikin sink ta juya kamar cikin fushi.
Sai dana gama girkina idanu na ya sauka akan dankalin, na dauki kwara daya na kai bakina, frowning nayi. Dankalin tauri kamar danye ga dan banzan gishiri da yaci. Na gyada kai a hankali tare da zubar da dankalin na wanke kayan dana bata naje na jera girkin na shige daki. Wanka na fara yi kafin nayi sallah na jira aka kira Isha'i nayi kafin na fita falo muka fara dinner. Tun a wajen jikina ya fara rawa, sanyi yake shigar ko wace kofa ta jikina sosai.
Hafsy ta kalleni tace “Anty Nafee, jikinki rawa yake yi baki da lafiya ne?" nace “zazzabi ne, yanzu zan shiga in sha magani ai" tayi shiru tana kallona, can tace “ko dai in kira Anty Raliya?" nayi saurin cewa “a'ah da wannan daren? Mura ce take shirin kama ni zan sha magani" tace “to Allah ya sauwake" bayan mun gama cin abincin muka dan yi kallo kowa ya wuce dakin shi. Shirin kwanciya barci nayi naja bargo na rufe jikina, rawar sanyi nake yi ina jin kamar an watsa ni cikin ruwan kankara hakorana har haduwa suke yi waje guda. Ina cikin wannan halin Hafsy tazo ta same ni, da sauri ta hayo kan gadon tana jijjiga ni amma na kasa daga kai in kalleta, fita tayi da sauri sai gata ta dawo ita da Anty Mubeenah. Da sauri ta dago ni tana tamvayar lafiya?? Ganin na kasa yin magana yasa ta hau daga drawers har ta lalubo paracetamol, Hafsy ta miko ruwa Anty ta bani maganin nasha na koma na kwanta. Ba a jima ba barci ya dauke ni, ban san sanda suka bar dakin ba.
Da asubahi koda na tashi babu zazzabin sai mura data min mugun kamu, nayi sallah ina ta atishawa da tari ba kakkautawa. Na shirya break fast na kai kan dinning na ajiye, ina cikin shiryawa din Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, nan ta min ya jiki na amsa da sauki tare da mata godiyar dawainiyar ta a gare ni a daren jiya, ta wuce dakinta. Nima dakina na koma na kira Abbuna muka sha hirar mu har sai da Hafsy ta leko ta kirani sannan muka yi sallama na fita muka karya. Yaran makaranta suka wuce ni kuma na zauna anan falo ina kallo Anty Mubeenah kuma ta shige dakinta, na kula kwana biyun nan bata cika fita ba.
Wajen karfe goma na safe sai ga su Anty Ameenah da Anty Rahila sun zo wai ashe Hafsy ce ta kira su a waya tace musu bani da lafiya, na kama baki ina dariya nace “Lallai ma Hafsy! Zazzabi ne nayi jiya da dare fa, mura nake yi sai kuma nayi wankan yamma ina jin shine ya saukar mun da zazzabin, amma shine har da shela??" Anty Raliya tace “ai ba shela bace ba Nafeesah, gaskiya ce. Idan wani abu fa ya faru??" nace “babu abinda zai faru ma in shaa Allah. Ai Hafsy din da Anty Mubeenah suka kula dani" na lura da kallon mamakin da suka jefe ni dashi kafin suka basar, Anty Ameenah tace “To Allah ya kara lafiya" nace “Ameen" sai ga Anty Mubeenah ta fito, nan ta samu waje ta zauna suka gaisa, basu jima ba suka mana sallama suka tafi suna jaddada min idan dai naji ciwon ya dawo in kira su fa, nace toh.
*****
Mun fito daga cikin jifatu ni da Hafsy mun je shopping, ina kokarin bude mota mu shiga naji an kira sunana daga bayanmu cikin wata irin murya da naji kamar na san ta, “Nafeesah??" ga namaki na koda na juya Muneer na gani a tsaye, dauke a kafadar shi wata dan yaro ne zai kai kimanin shekaru hudu kila. Ya matso yace “Allahu Akbar! Ashe dai ke din ce, ya kike?" nayi murmushi, shekaru masu yawa sosai rabon da mun hadu kenan tun ma kafin in bar Kadpoly. Nace “lafiya na qalau Muneer, kai fa?" ya kalli Hafsy dake tsaye a gefena tana kallon shi cikin alamun rashin sanayya, yace “diyar ki ce?" ni abin sai ma ya bani dariya, ya kalli zankadediyar budurwa kamar Hafsy yace wai diya ta?? Nace “ehh, baka ga muna kama ba?" sai yayi er dariya, ya nuna min yaron hannunshi yace “dana kenan, Suleiman... Ke fa?" na daga kafada, “Allah bai kawo ba har yanxu" yace “to Allah ya kawo masu Albarka" nace “Ameen" daga haka muka yi sallama kowa ya shiga motar shi yaja. A cikin mota nayi murmushi tare da gyada kai cikin kara sakankancewa da Girma na Subhanah! Lallai Hausawa sun yi gaskiya da suka ce wani baya auren matar wani kamar yadda wani baya haihuwar dan wani...
A daren ranar misalin karfe sha daya na dare na fito daga dakina da niyar zuwa kicin dauko ruwa, naci karo da Anty Mubeenah Zaune akan kujera cikin duhun falon wanda hasken dake waje ne daya dan shigo ta labulaye yasa na ganta, da farko tsoro ta bani kafin na dan matsa zuwa gabanta nace “Anty Mubeenah baki da lafiya ne?" ta dan dago a firgice ta kalleni kafin ta kauda kai, kai ta girgiza tace “lafiya ta qalau... Babu komi" kamar zan yi magana sai na fasa, na tunkari kicin kafin in dakata dalilin kiran sunana da tayi “Nafeesah...!" na juya a hankali na kalleta “ma'am?" ta dan daburce, “umh... Koda yake ma ba komi, je ki kawai" na juya naje na bude fridge na dauko ruwa mara sanyi na sha anan cikin kicin din na maida goran ciki na fita.
Har lokacin Anty tana a yanayin tagumi kamar yadda na fara samunta daga farko, har zan wuce sai kuma na fasa. Na koma kusa da ita na zauna sosai ina fuskantar ta, hannunta na kamo cikin nawa na rike, a hankali nace “Anty Mubeenah..."...
*Gaisuwar ban gajiya zuwa ga en matan Amarya Anty Zee da sister Husnah.... Allah ya huta gajiya ya kuma kawo mana naku bikin mu sha shagali, lol.
~Ni Da Abokin Baba na fans, ya kuke? Sannan me kuke tunani game da canjin halin Mubeenah???
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA...!*
*©Jeedderh Lawals*
*®Fikrah Writers Association* 🖊🖊
*59*
Nace “Anty Mubeenah.... Ni ba karamar yarinya bace ba, kina cikin damuwa naga hakan rubuce akan fuskar ki. Kai ko makaho ya shafa ki yasan cewa kina cikin damuwa.. Nasan cewa ban kai matsayi ko girman da zan zama abokiyar shawarar ki ba, amma idan kina ganin babu damuwa kuma zaki iya, y can't u just tell me?? I'll be a good listener and a judger" tayi shiru tana kallona cikin nuna can I trust you? Na kai daya hannuna na shafa bayan hannunta ina mata murmushi reassuringly, nace “trust me, wallahi u r safe with me... Ki yarda dani".
Numfashi ta ajiye a hankali, “na yarda dake Nafeesah, ke mutum ce ta gari mai hankali da natsuwa. Ina tunanin kila ki tsane ni akan abubuwan da na aikata...!!" tayi shiru tana kallona nima na kalleta ban yi magana ba sai data yi radin kanta kafin taci gaba da magana.
Toilet na fada na dauro alwala na fito nayi sallar La'asar, bayan na gama na hau en gyare-gyare a dakin babu kakkautawa da yake ba wani aikin yi ne dani ba duk da cewa ranar girki na ce dai. Wajen karfe biyar na tashi na shiga kicin din, Anty Mubeenah tana tsaye a gaban gas cooker da frying pan akai da alamu tana frying abu, na kalleta cike da mamaki ita kuma ta kalleni da blank expression, tunda muke da matar nan sai ranar na taba ganinta a kicin wai da sunan girki, sai na dake kawai na shiga cikin store na fito da duk abubuwan da zan bukata. Da yake babban kicin ne, kuma yawanci komi na amfani a kicin din guda biyu ne sai na kunna wani gas din na fara girkina. Cikin kankanin lokaci kamshi ya bade ko'ina na gidan, ta gefen ido nake kallon Anty Mubeenah ina wasi-wasin dalilinta na yin girki yanzu. Har ta gama soya dankalin ta juye a cikin plate ta kashe gas din ta fita, na tabe baki naci gaba da aiki na. Ba a jima sai gata ta fado kicin din, ta tangwarar da plate din a cikin sink ta juya kamar cikin fushi.
Sai dana gama girkina idanu na ya sauka akan dankalin, na dauki kwara daya na kai bakina, frowning nayi. Dankalin tauri kamar danye ga dan banzan gishiri da yaci. Na gyada kai a hankali tare da zubar da dankalin na wanke kayan dana bata naje na jera girkin na shige daki. Wanka na fara yi kafin nayi sallah na jira aka kira Isha'i nayi kafin na fita falo muka fara dinner. Tun a wajen jikina ya fara rawa, sanyi yake shigar ko wace kofa ta jikina sosai.
Hafsy ta kalleni tace “Anty Nafee, jikinki rawa yake yi baki da lafiya ne?" nace “zazzabi ne, yanzu zan shiga in sha magani ai" tayi shiru tana kallona, can tace “ko dai in kira Anty Raliya?" nayi saurin cewa “a'ah da wannan daren? Mura ce take shirin kama ni zan sha magani" tace “to Allah ya sauwake" bayan mun gama cin abincin muka dan yi kallo kowa ya wuce dakin shi. Shirin kwanciya barci nayi naja bargo na rufe jikina, rawar sanyi nake yi ina jin kamar an watsa ni cikin ruwan kankara hakorana har haduwa suke yi waje guda. Ina cikin wannan halin Hafsy tazo ta same ni, da sauri ta hayo kan gadon tana jijjiga ni amma na kasa daga kai in kalleta, fita tayi da sauri sai gata ta dawo ita da Anty Mubeenah. Da sauri ta dago ni tana tamvayar lafiya?? Ganin na kasa yin magana yasa ta hau daga drawers har ta lalubo paracetamol, Hafsy ta miko ruwa Anty ta bani maganin nasha na koma na kwanta. Ba a jima ba barci ya dauke ni, ban san sanda suka bar dakin ba.
Da asubahi koda na tashi babu zazzabin sai mura data min mugun kamu, nayi sallah ina ta atishawa da tari ba kakkautawa. Na shirya break fast na kai kan dinning na ajiye, ina cikin shiryawa din Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, nan ta min ya jiki na amsa da sauki tare da mata godiyar dawainiyar ta a gare ni a daren jiya, ta wuce dakinta. Nima dakina na koma na kira Abbuna muka sha hirar mu har sai da Hafsy ta leko ta kirani sannan muka yi sallama na fita muka karya. Yaran makaranta suka wuce ni kuma na zauna anan falo ina kallo Anty Mubeenah kuma ta shige dakinta, na kula kwana biyun nan bata cika fita ba.
Wajen karfe goma na safe sai ga su Anty Ameenah da Anty Rahila sun zo wai ashe Hafsy ce ta kira su a waya tace musu bani da lafiya, na kama baki ina dariya nace “Lallai ma Hafsy! Zazzabi ne nayi jiya da dare fa, mura nake yi sai kuma nayi wankan yamma ina jin shine ya saukar mun da zazzabin, amma shine har da shela??" Anty Raliya tace “ai ba shela bace ba Nafeesah, gaskiya ce. Idan wani abu fa ya faru??" nace “babu abinda zai faru ma in shaa Allah. Ai Hafsy din da Anty Mubeenah suka kula dani" na lura da kallon mamakin da suka jefe ni dashi kafin suka basar, Anty Ameenah tace “To Allah ya kara lafiya" nace “Ameen" sai ga Anty Mubeenah ta fito, nan ta samu waje ta zauna suka gaisa, basu jima ba suka mana sallama suka tafi suna jaddada min idan dai naji ciwon ya dawo in kira su fa, nace toh.
*****
Mun fito daga cikin jifatu ni da Hafsy mun je shopping, ina kokarin bude mota mu shiga naji an kira sunana daga bayanmu cikin wata irin murya da naji kamar na san ta, “Nafeesah??" ga namaki na koda na juya Muneer na gani a tsaye, dauke a kafadar shi wata dan yaro ne zai kai kimanin shekaru hudu kila. Ya matso yace “Allahu Akbar! Ashe dai ke din ce, ya kike?" nayi murmushi, shekaru masu yawa sosai rabon da mun hadu kenan tun ma kafin in bar Kadpoly. Nace “lafiya na qalau Muneer, kai fa?" ya kalli Hafsy dake tsaye a gefena tana kallon shi cikin alamun rashin sanayya, yace “diyar ki ce?" ni abin sai ma ya bani dariya, ya kalli zankadediyar budurwa kamar Hafsy yace wai diya ta?? Nace “ehh, baka ga muna kama ba?" sai yayi er dariya, ya nuna min yaron hannunshi yace “dana kenan, Suleiman... Ke fa?" na daga kafada, “Allah bai kawo ba har yanxu" yace “to Allah ya kawo masu Albarka" nace “Ameen" daga haka muka yi sallama kowa ya shiga motar shi yaja. A cikin mota nayi murmushi tare da gyada kai cikin kara sakankancewa da Girma na Subhanah! Lallai Hausawa sun yi gaskiya da suka ce wani baya auren matar wani kamar yadda wani baya haihuwar dan wani...
A daren ranar misalin karfe sha daya na dare na fito daga dakina da niyar zuwa kicin dauko ruwa, naci karo da Anty Mubeenah Zaune akan kujera cikin duhun falon wanda hasken dake waje ne daya dan shigo ta labulaye yasa na ganta, da farko tsoro ta bani kafin na dan matsa zuwa gabanta nace “Anty Mubeenah baki da lafiya ne?" ta dan dago a firgice ta kalleni kafin ta kauda kai, kai ta girgiza tace “lafiya ta qalau... Babu komi" kamar zan yi magana sai na fasa, na tunkari kicin kafin in dakata dalilin kiran sunana da tayi “Nafeesah...!" na juya a hankali na kalleta “ma'am?" ta dan daburce, “umh... Koda yake ma ba komi, je ki kawai" na juya naje na bude fridge na dauko ruwa mara sanyi na sha anan cikin kicin din na maida goran ciki na fita.
Har lokacin Anty tana a yanayin tagumi kamar yadda na fara samunta daga farko, har zan wuce sai kuma na fasa. Na koma kusa da ita na zauna sosai ina fuskantar ta, hannunta na kamo cikin nawa na rike, a hankali nace “Anty Mubeenah..."...
*Gaisuwar ban gajiya zuwa ga en matan Amarya Anty Zee da sister Husnah.... Allah ya huta gajiya ya kuma kawo mana naku bikin mu sha shagali, lol.
~Ni Da Abokin Baba na fans, ya kuke? Sannan me kuke tunani game da canjin halin Mubeenah???
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA...!*
*©Jeedderh Lawals*
*®Fikrah Writers Association* 🖊🖊
*59*
Nace “Anty Mubeenah.... Ni ba karamar yarinya bace ba, kina cikin damuwa naga hakan rubuce akan fuskar ki. Kai ko makaho ya shafa ki yasan cewa kina cikin damuwa.. Nasan cewa ban kai matsayi ko girman da zan zama abokiyar shawarar ki ba, amma idan kina ganin babu damuwa kuma zaki iya, y can't u just tell me?? I'll be a good listener and a judger" tayi shiru tana kallona cikin nuna can I trust you? Na kai daya hannuna na shafa bayan hannunta ina mata murmushi reassuringly, nace “trust me, wallahi u r safe with me... Ki yarda dani".
Numfashi ta ajiye a hankali, “na yarda dake Nafeesah, ke mutum ce ta gari mai hankali da natsuwa. Ina tunanin kila ki tsane ni akan abubuwan da na aikata...!!" tayi shiru tana kallona nima na kalleta ban yi magana ba sai data yi radin kanta kafin taci gaba da magana.