Sashe 53
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kwana biyu kuwa ban yarda na latsa sunan Mom a wayana da sunan kira ba sanin halinta na sauka daga fushi da kanta idan ta hau don sau tari idan tana fushi bata cika son ana bin kanta ana bata hakuri ba ma, she prefers a kyaleta har sai ta sauka don kanta, don haka ban tarki kiranta ba sai dai na tura mata text message which of course bata yi replying ba.
Ina fitowa daga class na koma daki, su Ni'ima suka kira ni suka ce suna dakina. Ina shiga suka tare ni da shewa ni har suka sa gabana ya fadi ina tunanin ko zancen mu da Abbu ya kai kunnensu ne, sai da muka gaisa har muka fara hira naga basu yi maganar ba sannan na dan saki jikina. Na kunna stove ina kallonsu, "me zan dora muku?" Ni'ima tace Indomie noodles, Sadiya kuma tace Spaghetti, na kallesu "guys, idan zaku daidaita akan abu daya ku daidaita don kun san bani da lokacin yin girki biyu" suka kwashe da dariya, Sadiya tace "dora mana noodles, wannan maman Babyn ba zata barmu mu shaki iska mai dadi ba idan ba a dafa noodles dinnan ba" nace "kema ai Maman Babyn ce" ta wani zare ido, wa?? Muka kwashe mata da dariya ni da Ni'ima. Nan da nan na dora Indomie na ta dahu na juye mana a tray muka fara ci. Muna cikin ci kiran Abbu ya shigo wayata, na kalli wayar tare da kallon su Ni'ima dake kallona suma, na ci mur tare da janye wayar na kife ta akan gado, suka yi sharing glancing a tsakaninsu. Sadiya ce tace "wai ni me ke tsakanin mutanen nan biyu ne? I've started putting a big question mark a tsakanin su" Ni'imah tace "kamar kin shiga zuciyata wallahi... Ni kaina na kasa fahimta" na kara hade fuska ina cusa indomie bakina ba tare da nayi magana ba, sam bana so maganar mu da Abbu ta fita ta shiga cikin dangin sa don tsakanina da Allah ban san da wani ido zan kallesu ba, ban shirya ba. Ni'imah tace "idan tayi wari dai mun ji" ni dai na kyale su ban tankasu ba. Muka gama na wanke kwanuka na kai mana soft drinks muka sha, daga nan na koma class bayan nayi sallah na bar su a dakin, dana dawo ban same su ba sun bar mun sako dai kan cewa sun tafi. Da dare Abbu ya sake kirana, na daga wayar da sallamata ya amsa ya dora da cewa "me bawan Allah yayi aka ki daga kiran shi dazu" nace "bana kusa da wayar ne Abbu.... Ina yini?" ya amsa, anan yake fada min wae washegari zai tafi Ilorin zai yi sati daya a can. Yace "me zai hana idan na dawo kawai a daura mana aure Nafeesah?" nace "Abbu baka tunanin it's too sudden?" yayi sighing, "Nafeesah, y do u always keep saying yayi sudden? Kina tunanin haka zan ci gaba da kallonki Ina kauda kai har zuwa yaushe? Har ki gama makaranta ko me?" nayi kasa da murya nace "at least in dan yi nisa a karatu na mana!" yace "really? Kin san? Ko session dinnan ba zan bari ya kare ba ba tare dana aure ki ba Nafeesah, idan kuma ba so kike yi in..... God! Nafeesah wae me kike nufi da rayuwata ne??" muryar shi ta dan fara yin sama alamun ranshi ya fara baci, nayi shiru ban bashi amsa ba. Lokacin dana gama yanke shawarar yarda da Abba, kamuwa da son shi da amincewa akan cewa zan aure shi, ban yi tunanin zancen aure ba, ban yi tunanin cewa zai taso zancen aure nan kusa ba, ban yi tunanin zai so ya aure ni ina cikin karatu na ba, nayi tunanin zai bar ni in karasa karatuna ko kuma at the very least ya bari sai na kusa kammala karatuna sai kuma gashi yana zancen aure in the next two weeks when I'm not even ready for it, hell ban ma san meye ma'anar auren ba, me zan yi kenan?? Ga zancen mu da Mommy ga.... Ya katse ni ta hanyar cewa "just forget about it Nafeesah, bana son tursasaki yin abinda baki yi niyar yi ba. Na hakura da zancen auren, idan muka ci gaba da zama a haka ma ya ishe ni, I want your happiness" naji kwallah ta tsattsafo min a idanu, nace "Abbu kayi hakuri" yace "don't mind Amour, na fahimce ki" nayi murmushi mai sauti wanda na tabbata ya jiyo sautin shi, ya maido min da martanin wani wanda yasa naji gwiwoyin kafana sun yi wani sanyi, yace "Pretty na tana ta cigiyar ki, yaushe zaki zo ki ganta?" na zaro ido kamar yana gabana, har sai da naji gabana ya fadi nace "ni?? A'ah gaskiya" ya danyi er dariya, "tsoron me kike ji ne? Na manta ma dazu in fada musu you are now my wife to be" nayi saurin cewa "pls Abbu no! Don Allah ba yanzu ba!" yace y? Na dan turo baki, "ni dai don Allah a'ah" yace "naki, sai na fada musu" na kula tsokana ta kawai yake yi don haka na kyale shi yayi ya gaji sannan muka danyi hira kafin muka yi sallama na mishi Allah ya kiyaye hanya muka ajiye wayar. Abin mamaki sai ga kiran Mommy ya shigo wayana, nayi tsuru Ina kallon wayar kamar ba zan daga ba, Ina tsoron abinda zai faru idan na daga kiran. Sai daya kusa tsinkewa sannan na daga, a hankali kamar mai tsoronta nayi sallama tare da gaida ta, cikin usual tone dinta ta amsa yadda take min, ta tambayeni karatu da sauran abubuwa duk na amsa mata da lafiya lau, tace "naji abinda kika yi Nafeesah, kina ganin daidai ne hakan?" nace "Mommy kiyi hakuri don Allah" tayi shiru kafin tayi ajiyar numfashi, "to tell you the truth naji haushin Abin daga farko, daga baya sai naga cewa abinda kike so kenan and I don't have the right da zan hana ki yin auren da kike so ba Ummiey. I really hope decision din da kika yanke shine daidai kuma zai kawo miki farinciki mai dorewa a cikin rayuwar auren ki" naji zuciyata tayi wani irin sanyi, na saki sansanyar ajiyar zuciya Ina jan hamdala a cikin raina, nace "Mommy nagode sosai" tace "Ni me ma zaki ce mun ne? Kwana biyu baki kira ni ba saboda kina gudun kar in hana ki yin soyayya ko?" nace "mommy ba haka bane" tace "idan haka ne ma ya zanyi? Tunda daddyn ki ya kitsa miki kin hau kai kin zauna, ina jinshi ai yana baki shawarar kar ki kira ni shine ke kuma kika ki kirana" na sake cewa "kiyi hakuri" ina danne dariyar data taso min, ta kuta, "he was even threatening me wai zai iya karo aure, bai san cewa abinda matar shi Ibrahim din zata yi da halin da zata shiga idan taji zancen auren bane nake gujewa ba, yayi zaton son raina ne nake shirin shiga tsakaninki da abinda kike so ba. Ummiey mata da kike gani baki san irin tashin hankali da fargaba da suke shiga idan suka ji zancen kishiya ba balle ita data zauna dake a gida daya ta rike ki cikin amana, dare daya ace zaki aure mata miji kin san ba zata ji dadi ba dai koh?" jikina yayi sanyi na sadda kaina kasa, wannan yana daya daga cikin abinda ya saka ni hesitating at first amma ya zamu yi? Ba zamu danne farinciki cikinmu don faranta ran wadda bata san namu farin cikin ba. Mommy tace "kada ki damu fa, kuma kada ki saka maganar a cikin zuciyar ki babu abinda zai faru da yardar Allah. Amma ya miki zancen aure? Yaushe yace za ayi?" nayi wuri-wuri da ido, tace "baki sani bane? Zan yiwa Daddyn ki magana, ya kamata ace anyi auren nan kawai" nayi saurin cewa, "Mom, ba zaku bari in gama karatu bane?" shiru ya biyo baya kafin tayi magana, "kina da hankali kuwa Ummiey? Shekaru nawa suka rage miki kafin ki gama karatunki, kina tunanin zamu zuba miki ido ko kuma shi Ibrahim din ne yace sai kin gama karatu?" nace A'ah, tace "to ai ko shine Ummiey ba zamu zuba miki ido ba, zan yiwa Daddynki magana a zauna ayi maganar auren ku don gaskiya hankalina ba zai kwanta ba kina karatu a Kano shima wanda ke son naki yana Kano mu muna nan Kaduna bamu san abinda ke faruwa ba a yadda duniyar nan ta baci" nace "Mommy baki yarda dani bane?" tace na yarda dake Ummiey, nasan irin tarbiyar dana baki, but still, hankalina ba zai kwanta ba gaskiya" nayi rolling eyes, "ai shikenan Mom" tace "zan dai tuntubi Daddynki inji, goodnight baby" na mata sai da safe tare da kashe wayar.
Ina fitowa daga class na koma daki, su Ni'ima suka kira ni suka ce suna dakina. Ina shiga suka tare ni da shewa ni har suka sa gabana ya fadi ina tunanin ko zancen mu da Abbu ya kai kunnensu ne, sai da muka gaisa har muka fara hira naga basu yi maganar ba sannan na dan saki jikina. Na kunna stove ina kallonsu, "me zan dora muku?" Ni'ima tace Indomie noodles, Sadiya kuma tace Spaghetti, na kallesu "guys, idan zaku daidaita akan abu daya ku daidaita don kun san bani da lokacin yin girki biyu" suka kwashe da dariya, Sadiya tace "dora mana noodles, wannan maman Babyn ba zata barmu mu shaki iska mai dadi ba idan ba a dafa noodles dinnan ba" nace "kema ai Maman Babyn ce" ta wani zare ido, wa?? Muka kwashe mata da dariya ni da Ni'ima. Nan da nan na dora Indomie na ta dahu na juye mana a tray muka fara ci. Muna cikin ci kiran Abbu ya shigo wayata, na kalli wayar tare da kallon su Ni'ima dake kallona suma, na ci mur tare da janye wayar na kife ta akan gado, suka yi sharing glancing a tsakaninsu. Sadiya ce tace "wai ni me ke tsakanin mutanen nan biyu ne? I've started putting a big question mark a tsakanin su" Ni'imah tace "kamar kin shiga zuciyata wallahi... Ni kaina na kasa fahimta" na kara hade fuska ina cusa indomie bakina ba tare da nayi magana ba, sam bana so maganar mu da Abbu ta fita ta shiga cikin dangin sa don tsakanina da Allah ban san da wani ido zan kallesu ba, ban shirya ba. Ni'imah tace "idan tayi wari dai mun ji" ni dai na kyale su ban tankasu ba. Muka gama na wanke kwanuka na kai mana soft drinks muka sha, daga nan na koma class bayan nayi sallah na bar su a dakin, dana dawo ban same su ba sun bar mun sako dai kan cewa sun tafi. Da dare Abbu ya sake kirana, na daga wayar da sallamata ya amsa ya dora da cewa "me bawan Allah yayi aka ki daga kiran shi dazu" nace "bana kusa da wayar ne Abbu.... Ina yini?" ya amsa, anan yake fada min wae washegari zai tafi Ilorin zai yi sati daya a can. Yace "me zai hana idan na dawo kawai a daura mana aure Nafeesah?" nace "Abbu baka tunanin it's too sudden?" yayi sighing, "Nafeesah, y do u always keep saying yayi sudden? Kina tunanin haka zan ci gaba da kallonki Ina kauda kai har zuwa yaushe? Har ki gama makaranta ko me?" nayi kasa da murya nace "at least in dan yi nisa a karatu na mana!" yace "really? Kin san? Ko session dinnan ba zan bari ya kare ba ba tare dana aure ki ba Nafeesah, idan kuma ba so kike yi in..... God! Nafeesah wae me kike nufi da rayuwata ne??" muryar shi ta dan fara yin sama alamun ranshi ya fara baci, nayi shiru ban bashi amsa ba. Lokacin dana gama yanke shawarar yarda da Abba, kamuwa da son shi da amincewa akan cewa zan aure shi, ban yi tunanin zancen aure ba, ban yi tunanin cewa zai taso zancen aure nan kusa ba, ban yi tunanin zai so ya aure ni ina cikin karatu na ba, nayi tunanin zai bar ni in karasa karatuna ko kuma at the very least ya bari sai na kusa kammala karatuna sai kuma gashi yana zancen aure in the next two weeks when I'm not even ready for it, hell ban ma san meye ma'anar auren ba, me zan yi kenan?? Ga zancen mu da Mommy ga.... Ya katse ni ta hanyar cewa "just forget about it Nafeesah, bana son tursasaki yin abinda baki yi niyar yi ba. Na hakura da zancen auren, idan muka ci gaba da zama a haka ma ya ishe ni, I want your happiness" naji kwallah ta tsattsafo min a idanu, nace "Abbu kayi hakuri" yace "don't mind Amour, na fahimce ki" nayi murmushi mai sauti wanda na tabbata ya jiyo sautin shi, ya maido min da martanin wani wanda yasa naji gwiwoyin kafana sun yi wani sanyi, yace "Pretty na tana ta cigiyar ki, yaushe zaki zo ki ganta?" na zaro ido kamar yana gabana, har sai da naji gabana ya fadi nace "ni?? A'ah gaskiya" ya danyi er dariya, "tsoron me kike ji ne? Na manta ma dazu in fada musu you are now my wife to be" nayi saurin cewa "pls Abbu no! Don Allah ba yanzu ba!" yace y? Na dan turo baki, "ni dai don Allah a'ah" yace "naki, sai na fada musu" na kula tsokana ta kawai yake yi don haka na kyale shi yayi ya gaji sannan muka danyi hira kafin muka yi sallama na mishi Allah ya kiyaye hanya muka ajiye wayar. Abin mamaki sai ga kiran Mommy ya shigo wayana, nayi tsuru Ina kallon wayar kamar ba zan daga ba, Ina tsoron abinda zai faru idan na daga kiran. Sai daya kusa tsinkewa sannan na daga, a hankali kamar mai tsoronta nayi sallama tare da gaida ta, cikin usual tone dinta ta amsa yadda take min, ta tambayeni karatu da sauran abubuwa duk na amsa mata da lafiya lau, tace "naji abinda kika yi Nafeesah, kina ganin daidai ne hakan?" nace "Mommy kiyi hakuri don Allah" tayi shiru kafin tayi ajiyar numfashi, "to tell you the truth naji haushin Abin daga farko, daga baya sai naga cewa abinda kike so kenan and I don't have the right da zan hana ki yin auren da kike so ba Ummiey. I really hope decision din da kika yanke shine daidai kuma zai kawo miki farinciki mai dorewa a cikin rayuwar auren ki" naji zuciyata tayi wani irin sanyi, na saki sansanyar ajiyar zuciya Ina jan hamdala a cikin raina, nace "Mommy nagode sosai" tace "Ni me ma zaki ce mun ne? Kwana biyu baki kira ni ba saboda kina gudun kar in hana ki yin soyayya ko?" nace "mommy ba haka bane" tace "idan haka ne ma ya zanyi? Tunda daddyn ki ya kitsa miki kin hau kai kin zauna, ina jinshi ai yana baki shawarar kar ki kira ni shine ke kuma kika ki kirana" na sake cewa "kiyi hakuri" ina danne dariyar data taso min, ta kuta, "he was even threatening me wai zai iya karo aure, bai san cewa abinda matar shi Ibrahim din zata yi da halin da zata shiga idan taji zancen auren bane nake gujewa ba, yayi zaton son raina ne nake shirin shiga tsakaninki da abinda kike so ba. Ummiey mata da kike gani baki san irin tashin hankali da fargaba da suke shiga idan suka ji zancen kishiya ba balle ita data zauna dake a gida daya ta rike ki cikin amana, dare daya ace zaki aure mata miji kin san ba zata ji dadi ba dai koh?" jikina yayi sanyi na sadda kaina kasa, wannan yana daya daga cikin abinda ya saka ni hesitating at first amma ya zamu yi? Ba zamu danne farinciki cikinmu don faranta ran wadda bata san namu farin cikin ba. Mommy tace "kada ki damu fa, kuma kada ki saka maganar a cikin zuciyar ki babu abinda zai faru da yardar Allah. Amma ya miki zancen aure? Yaushe yace za ayi?" nayi wuri-wuri da ido, tace "baki sani bane? Zan yiwa Daddyn ki magana, ya kamata ace anyi auren nan kawai" nayi saurin cewa, "Mom, ba zaku bari in gama karatu bane?" shiru ya biyo baya kafin tayi magana, "kina da hankali kuwa Ummiey? Shekaru nawa suka rage miki kafin ki gama karatunki, kina tunanin zamu zuba miki ido ko kuma shi Ibrahim din ne yace sai kin gama karatu?" nace A'ah, tace "to ai ko shine Ummiey ba zamu zuba miki ido ba, zan yiwa Daddynki magana a zauna ayi maganar auren ku don gaskiya hankalina ba zai kwanta ba kina karatu a Kano shima wanda ke son naki yana Kano mu muna nan Kaduna bamu san abinda ke faruwa ba a yadda duniyar nan ta baci" nace "Mommy baki yarda dani bane?" tace na yarda dake Ummiey, nasan irin tarbiyar dana baki, but still, hankalina ba zai kwanta ba gaskiya" nayi rolling eyes, "ai shikenan Mom" tace "zan dai tuntubi Daddynki inji, goodnight baby" na mata sai da safe tare da kashe wayar.