Sashe 82
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read
Abbu ya shigo kicin din, ina tsaye ina wanke hanta a jikin sink, ya tsaya a daidai gefena na dama. Kwana daya kacal daga ni har shi mun yi wani zuru-zuru damu, hannu yasa ya kamo habata a kokarin shi nason mu hada ido, sai nayi kasa da nawa idanun na hana shi ganin kwayar idanu na. Muryar shi tayi kasa sosai cike da damuwa yace “hey, me ke faruwa da ke ne Nafeesah?" na kara yin kasa da kaina na kasa magana, ya kara matsowa kusa dani sosai har ina jin saukar numfashin shi a kaina, fuskana ya sake dagawa sama, “talk to me Nafeesah please..... Look at me" yadda yayi maganar kamar wanda yake rokona yasa na daga idanuna na kalli nashi idanun, tsananin damuwa da kulawa dana hanga a cikin idanunshi suka sa ban san lokacin da hawaye suka zubo min ba, sai dana ji dumin su akan kumatuna sannan na ankara...
Abbu ya ida hade er tazarar dake tsakaninmu tare da rungume ni kam a jikinsa, a hamkali ya kai hannu bayana yana shafawa a hankali alamun rarrashi, hakan ya kara karya min xuciya sosai... Na zagaye hannuwana a bayan shi tare da fashewa da kuka ba tare dana shiryawa hakan ba.....
#TeamAbnaf
#OneLove
*♡Jeeedderh♡*
NI DA ABOKIN BABA NA....!!!
©•°jeedderh Lawals°•
®°•Fikrah Writers Association•°🖊🖊
*57*
Bayana yake tapping a hankali ba tare da yayi magana ba, ina jin yadda zuciyar shi take bugawa da sauri ban sani ba bacin rai ne ko tausayi na? Shi dai ya bar wa kan shi sani. Hannu yasa ya kashe gas din dana kunna, yaja hannuna ba musu na bi bayan shi muka fita daga cikin kicin din. Daki ya kaini ya zaunar dani a gefen gado yayin da shi kuma ya zauna a kasa a gabana ina fuskantar shi.
Sai dana gama shesshekar kukan da nake yi da komi, ya tashi yaje kan mirror ya dauko tissue ya miko min, hannu nasa na amsa na goge fuskata dashi. Wajen daya tashi ya koma ya zauna ya kalleni..., “ok, ina sauraronki. Fada min, me ya faru??".
Idanu na kura mishi cikin tunani, shin in gaya mishi ko kuwa in yi shiru? Shin in nuna mishi hotunan ko kuwa zan ci gaba da boyewa ne ina kwarar mu?? Ganin nayi shiru ba tare da nayi magana ba yasa ya kara matsowa gab dani, ya kamo hannuwana ya damke cikin nashi tare da dora su akan cinyata, murya can kasa wadda ta dakushe cike da damuwa yace “Kalle ni Nafeesah!" na dan yi hesitating na en dakikai kafin na daga kai a hankali na kalli kwayar idanun shi, take jikina yayi sanyi sosai, na kasa daurewa kallon tsananin kulawa, so da kauna da suke cikin idanun shi sai na kara yin kasa da kaina.
Yace “Nafeesah, idan ban manta ba na fada miki cewa babu boye sirri a tsakaninmu, ba zamu boyewa junan mu Abu ba komi tsananin munin shi kuwa, amma meye yanzu kike yi? You are hiding something from me Nafeesah, kin saka ni cikin damuwa gashi na rasa gane matsalar balle in magance miki ita, please tell me Nafeesah, tell me me ke damun ki??" rikon da yayi min a hannuna ya kara karfi, ajiyar zuciya na sauke a hankali. That's it! I couldn't do this anymore, kawai bari inji ta bakin shi in yaso komi ta fanjama shi kenan.
Naja numfashi a hankali tare da tashi cikin sanyin jiki bayan na zare hannuna daga cikin nashi, ya juya ya bini da kallo. Drawer din na bude na ciro hotunan cikin faduwar gaba na koma inda yake, sai dana lalubi gefen gado na zauna kafin na mika mishi hotunan, ya kalleni sosai kafin yasa hannu ya karba, na kura mishi idanu sosai ina so in ga yadda zai karbi ganin hotunan..
Idanun shi suka fito waje sosai kamar wadanda zasu fado kasa, nuna su yake yi da hannunshi kamar wani tababbe, da kyar ya iya kakaro sautin “Naffee..sah.... Daga ina??..." cikin rawar murya yana nuna min hotunan, na kura mishi ido ina kokarin karanta kalar tsoro dana gani a cikin idanuwan shi, na tsoron asirin shi ya tonu ne ko kuma na wani abu daban?? Nace “ba kai bane ba koh Abbu??" na kura mishi idanu cikin tsananin tsoron jin amsar da zata fito daga cikin bakin shi. Kai ya girgiza min da sauri, “bani bane ba Nafeesah., I promise you bani bane ba!".
Wani irin sanyi ya xiyarci zuciyana da gangan jikina gabadaya, na silale daga kan gadon na fada cikin jikin shi na rungume shi kankam kamar zan tsaga shi, nadama ta shige ni sosai. Da ace tun a jiyar na mishi magana da hakika bamu yi kwanan rashin sukuni da bacin rai ba, da ace tun a jiya din na mishi magana da ban ji bugun zuciya da ya dinga yin kamar zai kashe ni ba, da ban kwana cikin dacin rai da fargaba ba..... Nasa kaina a cikin wuyan shi ina kuka a hankali wanda sautin shi baya fita sai jikina da yake rawa saboda danne kukan da nake yi.
Abbu ya zaunar dani a kasan carpet din yasa hannu yana share min hawayen, sai da kukan yayi kasa kafin naji ya fara magana a nutse. “waye ya baki hotunan nan? Yaushe kuma?" naja shessheka kafin nace “ban san ko wanene ba, kawai dai wani yayi mun sallama sai ya bani yace wai sako ne tun shekaranjiya, sai jiya ne na bude" ya kura min idanu kamar wanda yake mamakin abinda nace mishi.. Can yayi magana a hankali, “kuma shine kika boye min, why??"
Na girgiza kaina kawai, yace “look Nafeesah!” na daga kai na kalleshi, yace “na fahimci tsoron abinda zai biyo baya ne ya hana ki fada min. Naji dadin hakan kamar yadda naji haushin boye min din da kika yi. Daga yanzu kada ki sake yi mun irin haka don Allah kinji? Kome ya faru kada kiji tsoron fada min, ta haka ne kadai zamu gina rayuwar aure mai inganci irin wadda nake so kin gane??” na gyada mishi kaina a nutse.
Hotunan ya sake dagawa yana kara kallonsu daya bayan daya yana girgiza kai idanunshi jawur, “Wallahil-Azeem bani bane Nafeesah. Ban taba bin mata ba, ban taba kusanta kaina da zina ba, bane bani!” hannunshi na rike cikin nawa ina gyada kai, “wallahi na yarda da kai Abbu. Ban san me yasa na kasa fada maka ba tun farko, amma ba zan sake maimaita hakan ba” hancina ya dan ja a hankali yana dan murmushi, nima nayi. Hoto daya ya dago yana nuna min, “kalli nan ki gani” na kurawa hoton ido ina kallo, hoton Abbun ne a tsaye babu riga a jikin shi yayin da macen da aka nuno su tare har lokacin ba a ganin fuskarta a kwance akan gado, nace “me zan gani?” kirjin mutumin jikin hoton ya nuna min, “nan, kin ga babu alamun tabo dina” na kama baki cike da tsananin mamaki, ya aka yi ban kula da haka ba? Ba mamaki saboda idanuna sun rufe ne shi yasa. Wani tabo ne a kirjin Abbu kusa da kafadar shi, tabo ne babba wanda yace lokacin da yaji ciwon it took him almost 3 months kafin ciwon ya warke amma tabon yana nan, yanzu dana kalli mutumin jikin hoton sai naga babu alamun tabon, kai karewa ma dana kare mishi kallo sam sai naga Abbuna yafi na jikin hoton kiba, to idan ba Abbu bane waye?.
Abbu ya kuta, “da alama wani ne yake so ya shiga tsakanin rayuwar auren mu Nafeesah, shine yasa aka yi photo editing din wani da fuskana aka kawo miki don ki tada balli, koma waye yayi haka ya gina ramin kuskure mai zurfi wallahi, I wouldn't spare him!”.
Wani tunani ya darsu a cikin raina, da sauri na kauda tunanin. Abbu ya kalleni “menene?” na girgiza kai, “m not sure don zargi bashi da dadi. Amma ranar da saurayin ya bani envelope din lokacin ina kokarin karya kwana, naga the same saurayin a tsaye shi da Dr Lubah... Ganin su kawai nayi, ban sani ba ko tana da hannu akan hakan?” Abbu ya dunkuke hoton hannunshi, “Dr Lubah!!! Zata aika, ta sha fada min zata yi duk abinda zata yi duk abinda zata yi wajen ganin cewa ta raba ni da farin cikina. Ban yi zaton da gaske take ba, I thought kawai tana fada ne don cika baki ashe da gaske take? So she can stoop this low kawai don ta raba ni dake?” nace “ni fa kawai ganin su nayi tare, bani da tabbacin ko ita ce” yace “ki ma daina wani tantama, she's the one” nace “zato dai bashi da kyawu, kamata yayi ka bincika kafin ka yanke hukunci” yayi shiru kafin ya gyada kai, “haka ne kuma, zan bincika in shaa Allah.... Now.., food!” dan murmushi nayi tare da mikewa na nufi kicin shima ya biyo bayana.
Ranar tare dashi muka yi girkin, muka koma falo muka karya muna hirarrakin mu cike da nishadi, ranar ko nan da can Abbu bai fita ba, yana manne dani kamar chewing gum. Da haka rayuwar auren mu ta koma normal kamar, ko ma in ce fiye da da.
Abbu ya ida hade er tazarar dake tsakaninmu tare da rungume ni kam a jikinsa, a hamkali ya kai hannu bayana yana shafawa a hankali alamun rarrashi, hakan ya kara karya min xuciya sosai... Na zagaye hannuwana a bayan shi tare da fashewa da kuka ba tare dana shiryawa hakan ba.....
#TeamAbnaf
#OneLove
*♡Jeeedderh♡*
NI DA ABOKIN BABA NA....!!!
©•°jeedderh Lawals°•
®°•Fikrah Writers Association•°🖊🖊
*57*
Bayana yake tapping a hankali ba tare da yayi magana ba, ina jin yadda zuciyar shi take bugawa da sauri ban sani ba bacin rai ne ko tausayi na? Shi dai ya bar wa kan shi sani. Hannu yasa ya kashe gas din dana kunna, yaja hannuna ba musu na bi bayan shi muka fita daga cikin kicin din. Daki ya kaini ya zaunar dani a gefen gado yayin da shi kuma ya zauna a kasa a gabana ina fuskantar shi.
Sai dana gama shesshekar kukan da nake yi da komi, ya tashi yaje kan mirror ya dauko tissue ya miko min, hannu nasa na amsa na goge fuskata dashi. Wajen daya tashi ya koma ya zauna ya kalleni..., “ok, ina sauraronki. Fada min, me ya faru??".
Idanu na kura mishi cikin tunani, shin in gaya mishi ko kuwa in yi shiru? Shin in nuna mishi hotunan ko kuwa zan ci gaba da boyewa ne ina kwarar mu?? Ganin nayi shiru ba tare da nayi magana ba yasa ya kara matsowa gab dani, ya kamo hannuwana ya damke cikin nashi tare da dora su akan cinyata, murya can kasa wadda ta dakushe cike da damuwa yace “Kalle ni Nafeesah!" na dan yi hesitating na en dakikai kafin na daga kai a hankali na kalli kwayar idanun shi, take jikina yayi sanyi sosai, na kasa daurewa kallon tsananin kulawa, so da kauna da suke cikin idanun shi sai na kara yin kasa da kaina.
Yace “Nafeesah, idan ban manta ba na fada miki cewa babu boye sirri a tsakaninmu, ba zamu boyewa junan mu Abu ba komi tsananin munin shi kuwa, amma meye yanzu kike yi? You are hiding something from me Nafeesah, kin saka ni cikin damuwa gashi na rasa gane matsalar balle in magance miki ita, please tell me Nafeesah, tell me me ke damun ki??" rikon da yayi min a hannuna ya kara karfi, ajiyar zuciya na sauke a hankali. That's it! I couldn't do this anymore, kawai bari inji ta bakin shi in yaso komi ta fanjama shi kenan.
Naja numfashi a hankali tare da tashi cikin sanyin jiki bayan na zare hannuna daga cikin nashi, ya juya ya bini da kallo. Drawer din na bude na ciro hotunan cikin faduwar gaba na koma inda yake, sai dana lalubi gefen gado na zauna kafin na mika mishi hotunan, ya kalleni sosai kafin yasa hannu ya karba, na kura mishi idanu sosai ina so in ga yadda zai karbi ganin hotunan..
Idanun shi suka fito waje sosai kamar wadanda zasu fado kasa, nuna su yake yi da hannunshi kamar wani tababbe, da kyar ya iya kakaro sautin “Naffee..sah.... Daga ina??..." cikin rawar murya yana nuna min hotunan, na kura mishi ido ina kokarin karanta kalar tsoro dana gani a cikin idanuwan shi, na tsoron asirin shi ya tonu ne ko kuma na wani abu daban?? Nace “ba kai bane ba koh Abbu??" na kura mishi idanu cikin tsananin tsoron jin amsar da zata fito daga cikin bakin shi. Kai ya girgiza min da sauri, “bani bane ba Nafeesah., I promise you bani bane ba!".
Wani irin sanyi ya xiyarci zuciyana da gangan jikina gabadaya, na silale daga kan gadon na fada cikin jikin shi na rungume shi kankam kamar zan tsaga shi, nadama ta shige ni sosai. Da ace tun a jiyar na mishi magana da hakika bamu yi kwanan rashin sukuni da bacin rai ba, da ace tun a jiya din na mishi magana da ban ji bugun zuciya da ya dinga yin kamar zai kashe ni ba, da ban kwana cikin dacin rai da fargaba ba..... Nasa kaina a cikin wuyan shi ina kuka a hankali wanda sautin shi baya fita sai jikina da yake rawa saboda danne kukan da nake yi.
Abbu ya zaunar dani a kasan carpet din yasa hannu yana share min hawayen, sai da kukan yayi kasa kafin naji ya fara magana a nutse. “waye ya baki hotunan nan? Yaushe kuma?" naja shessheka kafin nace “ban san ko wanene ba, kawai dai wani yayi mun sallama sai ya bani yace wai sako ne tun shekaranjiya, sai jiya ne na bude" ya kura min idanu kamar wanda yake mamakin abinda nace mishi.. Can yayi magana a hankali, “kuma shine kika boye min, why??"
Na girgiza kaina kawai, yace “look Nafeesah!” na daga kai na kalleshi, yace “na fahimci tsoron abinda zai biyo baya ne ya hana ki fada min. Naji dadin hakan kamar yadda naji haushin boye min din da kika yi. Daga yanzu kada ki sake yi mun irin haka don Allah kinji? Kome ya faru kada kiji tsoron fada min, ta haka ne kadai zamu gina rayuwar aure mai inganci irin wadda nake so kin gane??” na gyada mishi kaina a nutse.
Hotunan ya sake dagawa yana kara kallonsu daya bayan daya yana girgiza kai idanunshi jawur, “Wallahil-Azeem bani bane Nafeesah. Ban taba bin mata ba, ban taba kusanta kaina da zina ba, bane bani!” hannunshi na rike cikin nawa ina gyada kai, “wallahi na yarda da kai Abbu. Ban san me yasa na kasa fada maka ba tun farko, amma ba zan sake maimaita hakan ba” hancina ya dan ja a hankali yana dan murmushi, nima nayi. Hoto daya ya dago yana nuna min, “kalli nan ki gani” na kurawa hoton ido ina kallo, hoton Abbun ne a tsaye babu riga a jikin shi yayin da macen da aka nuno su tare har lokacin ba a ganin fuskarta a kwance akan gado, nace “me zan gani?” kirjin mutumin jikin hoton ya nuna min, “nan, kin ga babu alamun tabo dina” na kama baki cike da tsananin mamaki, ya aka yi ban kula da haka ba? Ba mamaki saboda idanuna sun rufe ne shi yasa. Wani tabo ne a kirjin Abbu kusa da kafadar shi, tabo ne babba wanda yace lokacin da yaji ciwon it took him almost 3 months kafin ciwon ya warke amma tabon yana nan, yanzu dana kalli mutumin jikin hoton sai naga babu alamun tabon, kai karewa ma dana kare mishi kallo sam sai naga Abbuna yafi na jikin hoton kiba, to idan ba Abbu bane waye?.
Abbu ya kuta, “da alama wani ne yake so ya shiga tsakanin rayuwar auren mu Nafeesah, shine yasa aka yi photo editing din wani da fuskana aka kawo miki don ki tada balli, koma waye yayi haka ya gina ramin kuskure mai zurfi wallahi, I wouldn't spare him!”.
Wani tunani ya darsu a cikin raina, da sauri na kauda tunanin. Abbu ya kalleni “menene?” na girgiza kai, “m not sure don zargi bashi da dadi. Amma ranar da saurayin ya bani envelope din lokacin ina kokarin karya kwana, naga the same saurayin a tsaye shi da Dr Lubah... Ganin su kawai nayi, ban sani ba ko tana da hannu akan hakan?” Abbu ya dunkuke hoton hannunshi, “Dr Lubah!!! Zata aika, ta sha fada min zata yi duk abinda zata yi duk abinda zata yi wajen ganin cewa ta raba ni da farin cikina. Ban yi zaton da gaske take ba, I thought kawai tana fada ne don cika baki ashe da gaske take? So she can stoop this low kawai don ta raba ni dake?” nace “ni fa kawai ganin su nayi tare, bani da tabbacin ko ita ce” yace “ki ma daina wani tantama, she's the one” nace “zato dai bashi da kyawu, kamata yayi ka bincika kafin ka yanke hukunci” yayi shiru kafin ya gyada kai, “haka ne kuma, zan bincika in shaa Allah.... Now.., food!” dan murmushi nayi tare da mikewa na nufi kicin shima ya biyo bayana.
Ranar tare dashi muka yi girkin, muka koma falo muka karya muna hirarrakin mu cike da nishadi, ranar ko nan da can Abbu bai fita ba, yana manne dani kamar chewing gum. Da haka rayuwar auren mu ta koma normal kamar, ko ma in ce fiye da da.