Sashe 70
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 5 min read
*“Sleep??"* nayi gaggawar tura mishi da, *“about to.... How was your day?"* ya turo *“dama nasan ba zaki iya barci ba baby na, tun yau fa baki ji murya ta ba balle kiga text dina, nima ina kewar ki baby na nasan da kyar barci ya dauke ni yau, amma kar ki damu, na yau ne kawai..., daga gobe babu wanda zai sake shiga tsakaninmu da yardar Allah"* lokacin dana karanta sai da er dariya ta kufce min, kai Abbu is full of self confidence. Na tura mishi *“says wanda yake da mata., plus ni fa barcin ne kawai bai zo ba amma babu wanda nake kewa sai Mommy da Daddy na!"* na tura ina dariyar tsokana, nasan kila har gari ya waye yau muna musayar sakonni ne, sai kuma har barci ya dauke ni bai dawo da reply ba.
Sai da muka tashi sallar Asabar naga amsar daya maido mintuna kadan da fara barci na, *“zaki ce haka ai tunda har yanzu baki zo hannu ba, gobe war haka ki maimaita abinda kika fada yanzu please...." nayi murmushi kawai na maida wayar kasan filo na fada toilet. Muna gama Sallah muka koma wani barcin, sai karfe tara na safe muka tashi. Muka yi wanka muka kimtsa, an kawo mana abinci daga gidan su Abbu muka fita parlour muka karya. Falon madaidaici ne wanda ya dauki wasu rantsattsun beige couches guda biyu an jera su daya ta kalli gabas daya kuma ta kalli arewa, sai wasu Everette chairs navy blue guda biyu suna fuskantar couch daya, a tsakiya kuma an saka babban teburin gilashi kasan shi wasu woods ne suka tokare shi, a sama kuma an dora flower base mai kyau, sai lamp mai kama da bishiya, kasan parlor hardwood flooring aka yi, kai komi dai na falon ya fita very unique, muka hau kan dinning mai cin kujeru takwas muka karya.
Dakina muka koma Anty Shafa sai cafta take sauke min tana karawa duk da wasu abubuwan duk tuni ne take yi mun. Karfe daya munyi sallar Azzuhur sai ga Abbu shi da abokan shi biyu, nayi sauri na dauko hijabi na dora akan kayana, falo muka fita muka gaisa dasu, ban yi gigin daga ido na kalli kowa ba. Ramlah ce tayi jigilar entertaining dinsu, ni kam suna fara cin abubuwan data kai musu nayi wuf na fada daki. Gefen gado na samu na zauna, ban jima ba sai ga Abbu shima ya shigo. Kai tsaye inda nake zaune shima yazo ya zauna a gefena, hannuwana duka biyun ya kamo da daya hannunshi, dayan kuma yayi amfani dashi wajen dago kafadata, ya wani rausayar da kai, “me nayi ne yau kuma Babyn? Babu gaisuwa, babu murmushi, babu kallo?" na sadda idanuna kasa tunda ya rike fuskar, duk yadda naso in daga baki in gaida shi kasawa nayi, wani irin nauyi da kunyar shi da ban taba ji ba naji sun dabaibaye ni, ya nisa, “bari in maida su AbdulHameed gida in kuma dauko direban da zai maida Anty gida sai in dawo gare ki gabadaya koh?" ya kai hannuna bakin shi yayi kissing as usual kafin ya fita.
Yana fita su Anty suka fara shirye-shiryen tafiya, nayi rau-rau da idanuna nan Anty ta samu abin fada, abin mamaki kuma bayan kamar awa daya da taji direba yazo sai kuma ta hau sharar kwallah, nan na rungumeta ina kuka, Ramlah ma tana gefe tana matsar kwallah, Abbu da kanshi ya leko ya sanar da ita zuwan direban. Ta mike tana share hawayenta tare da rataya jakarta, ta kamo hannuna ta rike cikin nata, “to Nafeesah, sai watarana, Allah ya baku zaman lafiya da maigidanki da abokiyar zaman ki, hakurin nan dai da kowa yake gaya miki kiyi da biyayya shi zan kara jaddada miki, sai kinyi exercising hakuri sannan ne zaki ci ribar rayuwar aure duk da nasan ki da hakuri amma dole sai kin kara kinji? Allah ya miki Albarka" na gyada mata kai ina hawaye.
Ta sa kafa ta fara tafiya Ramlatu ta bita a baya nima na bisu, a bakin falo Abbu ya dora min hijabin dana saka lokacin da abokan shi suka zo, muka karasa fita har shi. Ina tsaye har Anty Shafa ta shige mota Ramlah ma ta shiga different mota tunda ita gidan Anty Haleemah ta nufa. Direba ya tashi motar suka tafi muna daga musu hannu har maigadi ya maida gate ya rufe, wasu hawaye suka kara gangaro min a kumatu, shikenan an tafi an barni ni kadai. Abbu daya tsaya a bayana ya sakalo da kanshi ta wuyana tare da zagaye ruwan cikina da hannuwanshi, duk da halin da nake ciki sai da naji wasu abubuwa na min yawo a jikina, a hankali yake magana, “m sorry Baby, In Shaa Allah ni zan maye miki gurbin su Daddy dinki kinji? Stop crying kinji? Yau ce rana ta farko fa da zamu rayu karkashin rufi daya a matsayin ma'aurata, rana ce mai matukar muhimmanci don haka babu kuka ok?" na gyada kaina a sanyaye, ya sake ni ya juyo dani ina fuskantar shi, hannu yasa ya goge hawayen fuska ta, ya kama hannu na yana min murmushin nan nasa mai kwantar min da hankali muka koma cikin falo. Muna shiga aka kira sallah, ya shiga dakina yayi alwala ya tafi masallaci ni kuma na tada kabbarar tawa a daki abina.
Sai da muka tashi sallar Asabar naga amsar daya maido mintuna kadan da fara barci na, *“zaki ce haka ai tunda har yanzu baki zo hannu ba, gobe war haka ki maimaita abinda kika fada yanzu please...." nayi murmushi kawai na maida wayar kasan filo na fada toilet. Muna gama Sallah muka koma wani barcin, sai karfe tara na safe muka tashi. Muka yi wanka muka kimtsa, an kawo mana abinci daga gidan su Abbu muka fita parlour muka karya. Falon madaidaici ne wanda ya dauki wasu rantsattsun beige couches guda biyu an jera su daya ta kalli gabas daya kuma ta kalli arewa, sai wasu Everette chairs navy blue guda biyu suna fuskantar couch daya, a tsakiya kuma an saka babban teburin gilashi kasan shi wasu woods ne suka tokare shi, a sama kuma an dora flower base mai kyau, sai lamp mai kama da bishiya, kasan parlor hardwood flooring aka yi, kai komi dai na falon ya fita very unique, muka hau kan dinning mai cin kujeru takwas muka karya.
Dakina muka koma Anty Shafa sai cafta take sauke min tana karawa duk da wasu abubuwan duk tuni ne take yi mun. Karfe daya munyi sallar Azzuhur sai ga Abbu shi da abokan shi biyu, nayi sauri na dauko hijabi na dora akan kayana, falo muka fita muka gaisa dasu, ban yi gigin daga ido na kalli kowa ba. Ramlah ce tayi jigilar entertaining dinsu, ni kam suna fara cin abubuwan data kai musu nayi wuf na fada daki. Gefen gado na samu na zauna, ban jima ba sai ga Abbu shima ya shigo. Kai tsaye inda nake zaune shima yazo ya zauna a gefena, hannuwana duka biyun ya kamo da daya hannunshi, dayan kuma yayi amfani dashi wajen dago kafadata, ya wani rausayar da kai, “me nayi ne yau kuma Babyn? Babu gaisuwa, babu murmushi, babu kallo?" na sadda idanuna kasa tunda ya rike fuskar, duk yadda naso in daga baki in gaida shi kasawa nayi, wani irin nauyi da kunyar shi da ban taba ji ba naji sun dabaibaye ni, ya nisa, “bari in maida su AbdulHameed gida in kuma dauko direban da zai maida Anty gida sai in dawo gare ki gabadaya koh?" ya kai hannuna bakin shi yayi kissing as usual kafin ya fita.
Yana fita su Anty suka fara shirye-shiryen tafiya, nayi rau-rau da idanuna nan Anty ta samu abin fada, abin mamaki kuma bayan kamar awa daya da taji direba yazo sai kuma ta hau sharar kwallah, nan na rungumeta ina kuka, Ramlah ma tana gefe tana matsar kwallah, Abbu da kanshi ya leko ya sanar da ita zuwan direban. Ta mike tana share hawayenta tare da rataya jakarta, ta kamo hannuna ta rike cikin nata, “to Nafeesah, sai watarana, Allah ya baku zaman lafiya da maigidanki da abokiyar zaman ki, hakurin nan dai da kowa yake gaya miki kiyi da biyayya shi zan kara jaddada miki, sai kinyi exercising hakuri sannan ne zaki ci ribar rayuwar aure duk da nasan ki da hakuri amma dole sai kin kara kinji? Allah ya miki Albarka" na gyada mata kai ina hawaye.
Ta sa kafa ta fara tafiya Ramlatu ta bita a baya nima na bisu, a bakin falo Abbu ya dora min hijabin dana saka lokacin da abokan shi suka zo, muka karasa fita har shi. Ina tsaye har Anty Shafa ta shige mota Ramlah ma ta shiga different mota tunda ita gidan Anty Haleemah ta nufa. Direba ya tashi motar suka tafi muna daga musu hannu har maigadi ya maida gate ya rufe, wasu hawaye suka kara gangaro min a kumatu, shikenan an tafi an barni ni kadai. Abbu daya tsaya a bayana ya sakalo da kanshi ta wuyana tare da zagaye ruwan cikina da hannuwanshi, duk da halin da nake ciki sai da naji wasu abubuwa na min yawo a jikina, a hankali yake magana, “m sorry Baby, In Shaa Allah ni zan maye miki gurbin su Daddy dinki kinji? Stop crying kinji? Yau ce rana ta farko fa da zamu rayu karkashin rufi daya a matsayin ma'aurata, rana ce mai matukar muhimmanci don haka babu kuka ok?" na gyada kaina a sanyaye, ya sake ni ya juyo dani ina fuskantar shi, hannu yasa ya goge hawayen fuska ta, ya kama hannu na yana min murmushin nan nasa mai kwantar min da hankali muka koma cikin falo. Muna shiga aka kira sallah, ya shiga dakina yayi alwala ya tafi masallaci ni kuma na tada kabbarar tawa a daki abina.