Sashe 37
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 5 min read
"Hafsy!!" na furta a hankali, surprisingly, shockingly. Yarinyar ta taso da gudunta ta nufo ni, da sauri na kai gwiwoyina kasa na tare ta muka rungume juna cikin farinciki muna dariya. Sai da muka nutsa na dago fuskarta daga jikina na kalleta da mamaki, "ya aka yi haka Hafsy? Waya kawo ki?" tace "Abbu ne!!" na zaro ido sosai, falon na karade da kallo babu kowa sai Mommy dake kallon TV abinta, a hankali kamar mai rada nace "Abbun yana ina?" tace "ya tafi wajen meeting, dama meeting zai zo anan shine nace sai ya kawo ni wajen ki" na gyada kai a hankali ina kokarin boye embarrassment din daya lullube ni, I am still a stupid again to think that musamman Abbu ya kawo Hafsy wajena ko shima yazo gani na ne, ko ni a su wa?? Na tashi na kama hannunta nace "taho muje dakina koh?" ta daga min Kai tana watso min jerarrun fararen hakoranta, na wa Mommy sannu da gida ta amsa tana jefo min wani kallo, ban kula da ita ba dai naja hannun Hafsy sai dakina. A can fa hirar yaushe gamo ta barke, naga ta kara girma Masha Allah kamar ba Ita ba.... Tace hutun makaranta suka samu jiya, su Qaseem suna gidan Anty Amernah ita kuma da Abbu yace zai zo Kaduna ta saka rigima sai daya taho da ita. Naja kumatun ta ina dariya nace Kin kyauta. Sai dana canza kayan jikina, muka fita muka ci abinci muka dawo daki na kunna mana cartoon muna kallo ni da ita, ga popcorn a gefenmu da lemu muna sha abinmu. Da yamma na dauke ta muka fita cikin gari, mun sha yawace yawacen mu har muka gaji, sai da aka kira sallar Magrib sannan muka dawo gida. Bayan mun gama dinner muka koma dakinmu, na bude jakar kayanta na fitar mata da kayan barci tasa muka kwanta.
Washegari har cikin makarantar mu na shiga da ita, bani da lectures kawai yawo muka shiga. Daga karshe dai muka dire a gidan Anty Uwani. Bayan La'asar muna zaune a falo ni da su AbdulMaleek, The Space Between Us muke kallo a tashar MBC, Sultan Babban dan Anty Uwani ya kalleni cikin tsokana, "wai don Allah meye matsalar ki da wannan film din? Last time da kika zo gidan nan ma fa sai da kika kalleshi" nace "kawai film din ya burge ni ne" ya tabe baki, "a haka kuma idan aka cewa mutum yana acting like a child sai yace ba haka ba, Kun zauna nasara suna raina muku hankali Kun hau kai Kun zauna" filon kujera na dauka na jefa mishi ya cafe yana dariya. Daidai lokacin wayata tayi ringing, da sauri na daga ganin sunan Mom, "Ke kiyi sauri ku dawo Baban Hafsat yazo daukar ta!" wani irin faduwar gaba ta ziyarce ni kafin inji wani irin sanyi ya dabaibaye min jiki, jikina har rawa yake yi lokacin dana tashi ina lalubar gyalena da jakata, duk suka bini da kallo mai dauke da alamun tambaya. Na cewa Hafsy ta tashi mu tafi Abbu ne yazo, yarinyar ta tashi tana gunaguni da turo baki, ban ko bi ta kanta ba. Abinda na damu dashi a lokacin kawai shine in ganni a gaban Abbu, in dora idanuna akan fuskar Abbu. Anty Uwani ta fito daga kitchen, cikin mamaki take kallonmu, "ku kuma sai ina haka? Ba dai tafiya ba koh?" nace "Mommy ce ta kira ni yanzu tace muje Abbun Hafsat yazo tafiya da ita" ta kuma kicin ta dawo dauke da Leda wadda aka saka plastic roba a ciki wadda nasan dambun nama ne a ciki sana'ar ta kenan, bakery gareta wanda ake sarrafa fulawa ta hanyoyi daban-daban, suna kuma yin dambun nama a can. Ta mikawa Hafsy ledar tace "ga wannan sai kici a hanya koh?" Hafsy ta amsa tare da mata godiya, su Sultan suka raka mu har waje. Mun bata mintuna goma kyawawa bamu samu abun hawa ba gashi an aiki direban gidansu, Sultan yace "Kema ku jira direba ya dawo mana, sai ya kaiku. Nasan ba zai jima ba yanzu zai dawo" na girgiza kaina, a yadda nake jina dinnan a kagare, gani nake idan da halin inyi fuffuke da wallahi sai nayi, jiran Direban nan daidai yake da buguwar zuciyata ta tsage, nasan tsakanin doki da kaguwa ma ba zasu bar ni. Naja hannun Hafsy muka fara tattaki, Allah ya taimake mu kafin muyi nisa muka samu mai Adaidaita Sahu muka shiga. Bamu muka isa gida ba kuwa sai karfe Shida saura, a farfajiyar gidan Motar Abbu ce a fake a cikin gareji inda ake ajiye Motocin gidanmu. Zuciyata ta fara wani irin tsallen murna, duk yadda naso in boye farin cikina abun yaci tura. Sai dai muna shiga falo murnata ta koma ciki ganin falon wayam babu kowa, na dan hade fuska. Kamshin abinci na jiyo yana tashi nasan Mommy ce take girki, na shiga kicin din na sameta tana zuba abinci a cikin kuloli tana gani na tace "yauwa, zo ki dauki wannan ki kai sitting room daddynki yana can shi da Baban Hafsat" ban san lokacin dana saki ajiyar zuciya ba a sace, ashe yana sitting room ni ai nayi zaton ya gaji da jiranmu ne ya tafi. Kafin in shiga kicin din babu irin tunanin da ban yi ba a raina, kila ya gaji ya tafi, kila ma bai zo ba gabadaya, kila motar shi ce ta lalace ya ajiye tashi a gidanmu ya dauki ta Daddy ya tafi, tunanika dai barkatai. Mommy ta kalleni ganin yadda nake grinning ear to ear, tace "lafiya?" da sauri na gyara fuskata nace "babu komi" ta min nuni da Tray din data shirya flasks da jugs na ruwa da lemu akai, na cicciba na fita. Sitting room din yana can a karshen falon, kofar shi ta waje ake shiga ta bayan gidan inda ake hango dan karamin garden din gidanmu, amma akwai karamar kofa a falon gidan wadda muke shiga ta ciki.
Washegari har cikin makarantar mu na shiga da ita, bani da lectures kawai yawo muka shiga. Daga karshe dai muka dire a gidan Anty Uwani. Bayan La'asar muna zaune a falo ni da su AbdulMaleek, The Space Between Us muke kallo a tashar MBC, Sultan Babban dan Anty Uwani ya kalleni cikin tsokana, "wai don Allah meye matsalar ki da wannan film din? Last time da kika zo gidan nan ma fa sai da kika kalleshi" nace "kawai film din ya burge ni ne" ya tabe baki, "a haka kuma idan aka cewa mutum yana acting like a child sai yace ba haka ba, Kun zauna nasara suna raina muku hankali Kun hau kai Kun zauna" filon kujera na dauka na jefa mishi ya cafe yana dariya. Daidai lokacin wayata tayi ringing, da sauri na daga ganin sunan Mom, "Ke kiyi sauri ku dawo Baban Hafsat yazo daukar ta!" wani irin faduwar gaba ta ziyarce ni kafin inji wani irin sanyi ya dabaibaye min jiki, jikina har rawa yake yi lokacin dana tashi ina lalubar gyalena da jakata, duk suka bini da kallo mai dauke da alamun tambaya. Na cewa Hafsy ta tashi mu tafi Abbu ne yazo, yarinyar ta tashi tana gunaguni da turo baki, ban ko bi ta kanta ba. Abinda na damu dashi a lokacin kawai shine in ganni a gaban Abbu, in dora idanuna akan fuskar Abbu. Anty Uwani ta fito daga kitchen, cikin mamaki take kallonmu, "ku kuma sai ina haka? Ba dai tafiya ba koh?" nace "Mommy ce ta kira ni yanzu tace muje Abbun Hafsat yazo tafiya da ita" ta kuma kicin ta dawo dauke da Leda wadda aka saka plastic roba a ciki wadda nasan dambun nama ne a ciki sana'ar ta kenan, bakery gareta wanda ake sarrafa fulawa ta hanyoyi daban-daban, suna kuma yin dambun nama a can. Ta mikawa Hafsy ledar tace "ga wannan sai kici a hanya koh?" Hafsy ta amsa tare da mata godiya, su Sultan suka raka mu har waje. Mun bata mintuna goma kyawawa bamu samu abun hawa ba gashi an aiki direban gidansu, Sultan yace "Kema ku jira direba ya dawo mana, sai ya kaiku. Nasan ba zai jima ba yanzu zai dawo" na girgiza kaina, a yadda nake jina dinnan a kagare, gani nake idan da halin inyi fuffuke da wallahi sai nayi, jiran Direban nan daidai yake da buguwar zuciyata ta tsage, nasan tsakanin doki da kaguwa ma ba zasu bar ni. Naja hannun Hafsy muka fara tattaki, Allah ya taimake mu kafin muyi nisa muka samu mai Adaidaita Sahu muka shiga. Bamu muka isa gida ba kuwa sai karfe Shida saura, a farfajiyar gidan Motar Abbu ce a fake a cikin gareji inda ake ajiye Motocin gidanmu. Zuciyata ta fara wani irin tsallen murna, duk yadda naso in boye farin cikina abun yaci tura. Sai dai muna shiga falo murnata ta koma ciki ganin falon wayam babu kowa, na dan hade fuska. Kamshin abinci na jiyo yana tashi nasan Mommy ce take girki, na shiga kicin din na sameta tana zuba abinci a cikin kuloli tana gani na tace "yauwa, zo ki dauki wannan ki kai sitting room daddynki yana can shi da Baban Hafsat" ban san lokacin dana saki ajiyar zuciya ba a sace, ashe yana sitting room ni ai nayi zaton ya gaji da jiranmu ne ya tafi. Kafin in shiga kicin din babu irin tunanin da ban yi ba a raina, kila ya gaji ya tafi, kila ma bai zo ba gabadaya, kila motar shi ce ta lalace ya ajiye tashi a gidanmu ya dauki ta Daddy ya tafi, tunanika dai barkatai. Mommy ta kalleni ganin yadda nake grinning ear to ear, tace "lafiya?" da sauri na gyara fuskata nace "babu komi" ta min nuni da Tray din data shirya flasks da jugs na ruwa da lemu akai, na cicciba na fita. Sitting room din yana can a karshen falon, kofar shi ta waje ake shiga ta bayan gidan inda ake hango dan karamin garden din gidanmu, amma akwai karamar kofa a falon gidan wadda muke shiga ta ciki.