← Book details Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 79 OF 88

Sashe 79

Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kafin mu karasa sama na jigata kwarai da gaske, hawa steps din bene dari bakwai da hudu ba abu bane mai sauki lol, wai don ma muna dan tsayawa mu huta, ko kuma mu dan yi hotuna a wajajen da suka burge mu. At last! Bayan lokutan da suka fi awa biyu sai gamu on top of Eiffel Tower! Dana leka kasa ko tracing din mutane ba ka gani, sai kayi zaton cewa dots dots ne, but it was amazing really!! Na daga kai na kalli sararin samaniya, yadda ta zama soo close dani kamar in mika hannu in kamo kyakkyawar rana da take shirin faduwa saboda kusancina da ita. Mun jima a gun sosai, sai da muka huce har lokacin Magrib yayi sannan ne muka bi ta elevator muka sauka kasa, sai lokacin na yarda da maganar Vincent, sam banji dadin tafiya ta cikin elevator ba.

Sai data raka mu har hotel kafin ta mana sallama ta tafi, muka tsaya a wata restaurant anan wajen Hotel din, na zauna a lounge wajen da aka tanada don hutu yayin da Abbu ya tafi yayi sallah kasancewar ina fashi, bayan ya dawo muka ci abinci, Bhajia, steak da lemu mai sanyi. Daga nan muka sake komawa kasan Tower din inda bamu fi minti biyar da zuwa ba aka fara Fire Work! Woah, sai lokacin na fahimci dalilin da yasa Abbu yake ce min in jira ashe saboda show din ne. Naji dadin hakan sosai kuwa ba kadan ba, ban taba ganin abinda ya burge ni ba kamar kallon fireworks dinnan, idan ina kallo a cikin film jikina har rawa yake yi don burgewa, yau da aka yi displaying abin a gabana sai naji na rasa bakin magana in fayyace wa Abbu halin da nake ciki, kawai na sarkafo wuyan shi na hade bakina da nashi, ina ji ya fahimci sakon da nake son isar mishi, ya rungume ni sosai yana shafa bayana, a hankali na janye daga jikinshi ina dan murmushi cike da jin kunya, sai lokacin da ihu da iface ifacen mutanen wajen ya shiga kunnena na tuna inda muke, nan na karkata hankalina ga display din.

Bayan mintuna sha biyar aka gama display din muka koma dakinmu, Abbu yana Sallah na kira Daddy na fara bashi labari, ranar kam har sai daya gaji da saurare ya min sai da safe, na turo baki nace “Daddy har ka gaji dani koh?" dariya yayi yace ni na isa in gaji da jin story daga bakin Uwata? Na gaji ne, ga kuma Mommy dinki can tana jirana mu ci abinci" nace “to Daddy sai da safe, a gaida Mommy" muka yi sallama na ajiye wayar. Toilet na shiga na yi wanka na fito na shirya, already Abbu na kan gado don haka na bi bayan shi muka kwanta.

Daga Paris muka wuce Sao Paulo, Brazil. Kwanan mu biyar a can muka wuce Amsterdam, can kuma muka yi kwana hudu muka karasa Beijing. Kwananmu biyu a can bana lekawa ko can da nan saboda tsananin gajiya, sai a kwanaki na uku muka fita muka je kamfanin su Abbu.

Babban Kamfani ne Masha Allah! Shi kanshi ofishin Abbun wani wawakeken ofishi ne daya isa ace an gina wani karamin gida. Muna zuwa suka shiga meeting, ya hada ni da PA dinshi, Chao Shang muka zagaya kamfanin wanda ya dauke mu lokaci mai tsawo sosai kafin muka sake komawa ofis dinshi, har sai da nayi barci akan kujerar hutu kafin ya dawo, nan ya tashe ni muka koma hotel din da muka sauka.

Mun sha yawo a Beijing kamar Hauka, satin mu daya, mun je kananun garuruwa da kauyukan su mun bude idanu, mun shiga kasuwa mun yi siyayyar tarkace iri-iri da kayayyaki, Abbu dai duk inda muka je kayan jarirai ne yake saya unisex har da kayan wasanni inyi ta mishi dariya. Satinmu daya cif muka hada namu-i-namu muka dawo bayan Abbu ya hada mana kayayyakinmu an auna su a container amma fa sai da muka biya ta Bangladesh wajen Aminu kanin su. Kamanninsu da Abbu har ta baci, gashi da fara'ah da dan banzan tsokana, yana karantar Mechanical engineering ne a nan University dinsu. Already ya mana booking daki a hotel, don haka yana dauko mu daga airport can ya wuce damu, muka yi wanka muka yi Sallah muka yi abinci muka kwanta. Ranar duk nacin Abbu sai kyaleni yayi don ina jin kaina akan gado barci yayi awon gaba dani, ina jin yana lalubata amma na ma kasa daga hannu balle in maida mishi Martani, ina ji yayi kuta tare da furta bashi naci kafin ya janyo ni jikinshi. Aikuwa sai daya biya bashin nan da asubahi har sai daya kara min da alakoro.

Kwananmu biyu a can muka harhada namu ya namu muka wuce Najeriya cike da kewar Aminu da muka saba dashi sosai, shi ya zama idanun mu a can duk da cewa ba wasu yawace-yawace ne muka yi a can ba na azo a gani.

Saukar dare muka yi don haka muna yin Sallah sai barci, washegari aka yi ta zuwa sannu da zuwa da ganin gidan Amarya da wasu basu zo sun gani ba. Tsawon kwanaki uku ana ta shiga da fita kafin kafa ta daga, na tunkari Abbu da zancen ina so in je gida in ga su Daddy, idanu ya kura min a nutse lokacin kwanan shi daya a gidana, kamar ba zai yi magana ba can kuma yace “yaushe kike son zuwa?" nace “idan ka tafi gidan Anty Mubeenah gobe sai in tafi in dawo jibi" idanu ya xubo min sosai yana kallona kamar wadda notin kanta ya kunce dinnan, “haba Nafeesah! Kwana kuma? A'ah sam ban yarda ba gaskiya, za dai kije ki yini a can wannan kam na yarda amma ban da kwana" na turo baki gaba, “haba don Allah ka bar ni, yaushe rabon da in gansu har na manta fa, kuma ma sai fa nayi ziyarce-ziyarce idan naje can" yace “gaskiya ba zan iya ba Baby, kawai kije ki yini sai ki dawo" tashi nayi ina dira kafafu ni ban yarda ba nayi fushi na fada daki, ya bini da kallo yana dan murmushi.

Da yake dare ne mun gama cin abinci already, wanka na shiga nayi na shafa lotion mai kamshi sosai na aloe Vera, na shafa wani Arabian perfume mai kamshi sosai na fito dakin daure da towel a kirjina, Abbu yana zaune a gefen gado cikin pyjamas ya rungume hannuwa a kirji yana kallona, dauke kai nayi naje na bude wardrobe na fara binciken kayan barci, ban ji lokacin daya tashi daga kan gadon ba sai ji nayi an daga ni sama cak! Na dan saki kara cikin tsoro tare da kara rukunkume shi, kan gado ya dora ni tare da biyo bayana. Na fara mirginawa zan sauka yayi saurin janyo ni tare da pinning dina akan gadon ta hanyar rike min hannuwa. Kallon juna muka tsaya muna yi, a hankali ya saukar da bakinshi kan nawa ya fara tsotsa a hankali, da fari mutsu-mutsu na fara amma daga baya, wadannan effects da charming na Abbu a duk lokacin da fatar shi ta hadu da tawa suka sa na manta da zancen fushi na biye mishi...

A hankali yace “kiyi hakuri" nace “umh?" cikin daukewar hankali don bansan akan abinda yake ba da hakuri akai ba, yace “maganar xuwan ki gida, please ki daure kije ki musu yini kawai kinji Baby, please?" nayi shiru ina sauraren bugun da zuciyar shi take yi a hankali, numfashi naja nace to shikenan! Ya kara jana cikin jikinshi sosai, “oh Nafeesah! Shi yasa nake kara sonki a cikin raina kullum. Jibi zaki tafi da safe sai ki dawo da yamma ya miki?" na gyada mishi kai tare da kara shigewa cikin jikin shi.

Ranar Assabar muka dauki hanya ni dashi sai Kaduna. Misalin karfe Goma muna cikin gidanmu, kasa bari nayi mu shiga tare, na bazama da gudu nayi cikin gidan ina kwalawa su Daddy kira, a kofar falo muka ci karo dasu, nan na hada su duka su biyun na rungume a jikina, sai lokacin nasan ashe ba karamar kewar su nayi ba, har da yan guntun hawaye na. Sai da muka gama murnar ganin juna sannan muka karasa cikin falo, Daddy ya fita suka gaisa da Abbu wanda yace xai je ya dawo da yamma mu tafi, ya tafi bayan ya sauke tulin tsaraba da nayo musu daga sassa-sassa na garuruwan da muka da muka je.....

~Hii there my Lovie Dovie Fans!! Ya kuke? Miss Me?? Yeah, I can smell that. Kar ku damu, me too I miss you bhohhot kwarai da gaske. So I just steal some time ne haka na dan yi typing not that mun gama exams, har yanzu muna yi addu'o'inku are still needed., ina fata kun ji dadin chapter din ta yau??. And Wattpadians!! Ehh, naga comments da Votes suna kasa ne ya dae?? Yau dai ga chapter nan, I need to see bunches of ur Votes ta haka ne zaku nuna min how happy u guys are. Please comment line by line saboda ta haka ne nake sanin what is in u guys minds, and hu knows? Kila zuwa nan da ranar Talata ku sake ganin wata chapter, deal???

#TeanAbnaf
#AnaTare
#OneLove

*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA....!*

*©°•Jeedderh Lawals•°*

*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋

Shafin yau dungurungum naku ne mutanen Fikrah!!! Kungiya mai ban mamaki da ban Al'ajabi...., Allah ya albarkaci Alkalumanku da sauran marubuta baki daya......

*55*
Chapter 79 · 0% Book details