Sashe 81
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin da aka kira sallar La'asar lokacin ne hankalina ya dawo cikin jikina, na tashi da kyar da bin bango ina jin jiri na shiga toilet nayi alwala na fito nayi sallah, akan abin sallah naci gaba da zama na kurawa hotunan dake watse a tsakiyar dakin idanu gabadaya kwalwata ta kasa nema min mafita akan abinda ya kamata inyi.
Nayi tunanin in jira Abbun ya dawo in kwashi hotunan in watsa mishi a fuska, wata zuciyar tace shake shi zan yi har sai ya gaya min gaskiyar abinda ya faru, wata tace kawai in tashi in bar mishi gidan shi bai kamata in ci gaba da zama da maha'inci ba, tunanika barkatai har ta kai ga bana fahimtar abinda zuciyoyina suke kullawa da warwarewa. Cikin wannan halin na jiyo karar mota alamun dawowar Abbu daga masallaci, na tashi da kyar naje bakin kofa na tsaya ina hangen shi yana fitowa daga cikin mota hannunshi dauke da leda, agogo na duba. Awowi uku da suka wuce ya kamata ace ya dawo gidan, ina ya tsaya? Na samu zuciyata da saka tunanika marasa dadi, ina kallon shi ya taho da waya makale a kunnenshi, at the last step da zai hada shi da kofar falon, wani tunani ya dar su a cikin raina. Abbu na ne fa? Abbu na dai the gentle and good man dana sani ba wani ba, mutumin dana zauna a gidan shi na tsayin watanni shida ba tare daya taba rike yatsan Hannuna idan ba mistake ba, da ace dan iska ne kamar yadda nayi zato anya zai iya kyale ni kuwa bayan da ace yaso ya lalata ni da tuni yayi hakan? Mutumin da ko bayan aurenmu sai daya jira da ixini na da komi kafin ya kusance ni?? Dana kara tuno wasu abubuwan sai na samu kaina da sake kallon hotunan idanuna na hango katon question akan kowannen su zuciyata na tamvaya na anya kuwa babu lauje a cikin nadi??.
Da sauri na koma na hau tattare hotunan na janyo drawer ta gefen gado na watsa su ciki tare da fadawa toilet da sauri na, dole in zauna in sake tunani kafin in yanke hukuncin abinda ya dace inyi, ina rufe kofar bayin naji shigowar Abbu dakin....
Ganin bana dakin yasa ya fita daga dakin tare da maida min kofar dakin ya rufe. Na kurawa kaina idanu a jikin mirror ina kallon reflection dina, kwalliyar da nayi ta hade da ruwa da hawaye ta maida ni kamar zombie. Ruwa da sabulu nasa na wanke fuskana na kara yin wata kwalliyar kafin na fita, akan kujera na gan shi a zaune. Yana ganina ya saki murmushi mai taushi, yayin da naji gabana ya fadi sosai, anya zan iya daurewa kuwa? Don a daidai lokacin zuciyata tana kitsa min in ci kwalar shi ne kawai. Na daure na kakalo murmushi wanda nasan ko fatar bakina bai gama hadewa bama, a sanyaye na karasa kusa dashi na dan duka tare da cewa “Abbu sannu da zuwa" ya amsa yana murmushi, “kin ga na dade koh?" na gyada mishi kai kawai, yace “wai gidan Rahina na biya, shine ta hado ni da kaya ma tace in kawo miki" ya miko min ledar daya shigo da ita na amsa tare da dubawa, turaren wuta ne sai wani kamar na tsuguno idan ban manta ba naga irin shi cikin kayayyakin da aka hado min daga gida. Na maida ledar na rufe tare da kallon shi nace “abinci?" ya lumshe idanu tare da gyada kai, “please, m hungry... Very" da ace zuciyana cikin kwanciyar hankali take da babu abinda zai hana ni kamo fuskar shi in bashi sumba a baki, a yanzu kam koda tunanin ya fado cikin raina I found it disgusting sosai. Sai kawai nayi wajen dinning table ban ko yi magana ba yayin da naji lokacin daya tashi ya biyo bayana.
Abincin na hau zuba mishi, gabadaya cikina a cushe yake nasan sam babu abinda zai shiga cikina a lokacin don haka na zuba mishi iya wanda zai iya ci kawai, ina gamawa na tura mishi su gaban shi na juya da niyar tafiya yayi saurin sa hannu ya riko hannuna, ji nayi kamar garwashi ya taba ni, kallona yayi sosai, “ina zaki je haka? Ba zaki ci abincin bane?" na girgiza kai tare da kallon shi, “naci tun dazu da naga baka dawo ba" ya kara kallona kamar wanda bai yarda da abinda nace ba kafin naga yayi murmushi tare da jan kujerar gefen shi tayi baya ya zaunar dani, “ok, zauna ki taya ni hira toh, kin san cewa dai bana jin dadin cin abinci idan ba kya gefena koh?".
Haka na zauna tare da kurawa kasan carpet din idanu ina ta saka da warwara, ban san lokacin daya gama cin abincin ba, ya juyo dani na fuskance shi, “baby, me ke damun ki ne?" ya fada cikin nuna damuwa da halin da rashin walwalata a gare shi, nima nasan cewa yaudarar kaina kawai nake yi idan har nace wai zan iya pretending inyi behaving kamar yadda na saba.
Na girgiza kaina kawai, “babu komi Abbu, bana jin dadin jikina ne kawai" da sauri ya dora hannun shi akan goshina yaji babu zafi, ya dawo dashi wuya nan ma komi normal, yace “amma jikin ki lafiya lau... Are you sure ba sai mun je asibiti ba??" nayi saurin gyada kai, “m ok" yace “idan kin ji da wani abu don't hesitate fa, ki sanar dani" na gyada mishi kai, yayi murmushi tare da cewa “good girl" fuskana ya matso daidai tashi tare da kawo bakin shi saitin nawa, ina fahimtar abinda yake shirin yi nayi saurin kauda kaina gefe ta yadda leben shi ya kare da sauka akan kumatuna ba lebe na ba, ya dago ya kalleni cike da alamun tambaya, da sauri na tashi na tattara kayan da yayi amfani dasu na kai kicin. Wanke su nayi tare da dora abincin dare, ya leko kicin din ganin ina girki yazo ya kashe gas din, a hankali na dago na kalleshi amma ban yi magana ba, kafada ya daga cikin alamun tsokana “hey chill! Ba sai kinyi girki ba yau, zan fita in sayo mana abinci" sai kawai na juya na sauke tukunyar dana dora na zubar da ruwan tare da rabawa ta gefen shi na fita.
Ina gaban wardrobe dina ina shirya kayan ciki wadanda na ciro su daga ciki musamman saboda in dauke hankalina daga tunanika, Abbu ya sake shigowa dakin. Gefen gado ya samu ya zauna yayi tagumi tare da zuba min idanu wadanda seriously na dinga jin su a cikin jikina kamar me?? Kokari nake kawai naci gaba da aikina. Can kasan zuciyata ina so in mishi maganar, sai dai ina matukar tsoron abinda xai fito daga bakinshi, ina tsoron ya amsa min da ehh shine don a hakikanin gaskiya ban san ina zan jefa rayuwata idan hakan ta kasance ba.
Haka muka wanzu har aka kira sallar Magrib, Abbu ya tashi ya shiga toilet dina ya fito daure da alwala ya wuce masallaci, sai dana ga fitar shi sannan ne nima na dauro alwalar naxo na tada kabbarar sallah, anan kan sallayar na zauna bayan na gama ina laxumi har aka yi Isha'i nayi sallah. Tashi nayi na nade abin sallar, ina ta en kimtse-kimtse na wanda a zahirin gaskiya basu da amfani ina yi kawai don kada su dauke mun tunani, Abbu ya dawo daga masallaci. Dakin kawai ya leko yace in fita mu ci abinci. Na fita falon na same shi har ya fiddo plates waje, naje gefen shi na zauna kawai.
Gashin nama ya xuba mana cikin plate din da yoghurt a cikin cups, na sa cokali muka fara ci daga cikin kwano daya. Ba wai don wani abu ko yunwa nake cin abincin ba, kawai saboda bana so Abbu ya dame ni da korafi ne don a lokacin ko kadan bana so inyi magana, gabadaya raina a jagule yake. Abu na karshe da nake bukatar yi shine in kadaice a waje guda in nemi mafita a cikin rayuwata data aurena gabadaya.
Duk da halin da nake ciki hakan bai hana ni jin dadin naman ba har ma ban san lokacin dana bude ciki naci naman sosai ba, sai dana ji cikina ya cika kafin na kora da yogurt din, lokacin Abbu ya ture kwanon gefe alamun ya koshi don haka na tattara kayan na kai kicin, sauran kayan duk na saka su a cikin freezer na fita falo. Abbu yana zaune akan kujera yana kallon labaran kasa, na shige shi zuwa dakinshi da yake yanzu yawancin kayana ma suna dakin don ragewa kaina wahalar je ka dawo daga wannan dakin zuwa wancan. Toilet na shiga nayi brush na fito na shirya cikin kayan barci tare da fesa en turaruka na kwanta. Not that barci nake ji ko kuma gajiya, kawai ina gujewa Abbu ne.
Misalin karfe tara Abbu ya shigo dakin, ina jin alamun shigowar shi na kara lafewa akan gado kamar mai barci. Ina ji ya gama duk abubuwan da zai yi kamar su brush, shafa turare, sa kayan barci da sauran su. Ina jin lokacin daya kashe wutar dakin kafin inji alamun hawan shi kan gadon, na kara sakankance jikina sosai. Ina jin lokacin daya janyo ni jikinsa, duk da ihun da naji ana min a kunne akan in kwace jikina sharewa nayi, bana so inyi abinda zai sa Abbu yayi zaton idanu na biyu. Ina jin shi yana lalubata wanda da da ne tashi zanyi koda barcin nake yi in shige cikin kirjin Abbuna mai fadi, yau kam ban yi hakan ba.
Bayan lokaci mai tsayi naji alamun yayi barci, a hankali na zare jikina daga nashi tare da juya mishi baya, wasu siraran hawaye suna gangaro min a kumatu, ban san yaushe barci ya kwashe ni ba. Da asubahi Abbu ya tashe ni daga barci ya wuce masallaci. Ina kan sallaya ina karatu lokacin daya dawo daga masallacin, kan gado ya hau ya kwanta rigingine, ban motsa daga inda nake ba har sai da gari yayi sha, na rufe al-qur'anin na mayar dashi inda ake ajiye shi na fita daga dakin. Kicin na shiga na fara shirya break fast.
Nayi tunanin in jira Abbun ya dawo in kwashi hotunan in watsa mishi a fuska, wata zuciyar tace shake shi zan yi har sai ya gaya min gaskiyar abinda ya faru, wata tace kawai in tashi in bar mishi gidan shi bai kamata in ci gaba da zama da maha'inci ba, tunanika barkatai har ta kai ga bana fahimtar abinda zuciyoyina suke kullawa da warwarewa. Cikin wannan halin na jiyo karar mota alamun dawowar Abbu daga masallaci, na tashi da kyar naje bakin kofa na tsaya ina hangen shi yana fitowa daga cikin mota hannunshi dauke da leda, agogo na duba. Awowi uku da suka wuce ya kamata ace ya dawo gidan, ina ya tsaya? Na samu zuciyata da saka tunanika marasa dadi, ina kallon shi ya taho da waya makale a kunnenshi, at the last step da zai hada shi da kofar falon, wani tunani ya dar su a cikin raina. Abbu na ne fa? Abbu na dai the gentle and good man dana sani ba wani ba, mutumin dana zauna a gidan shi na tsayin watanni shida ba tare daya taba rike yatsan Hannuna idan ba mistake ba, da ace dan iska ne kamar yadda nayi zato anya zai iya kyale ni kuwa bayan da ace yaso ya lalata ni da tuni yayi hakan? Mutumin da ko bayan aurenmu sai daya jira da ixini na da komi kafin ya kusance ni?? Dana kara tuno wasu abubuwan sai na samu kaina da sake kallon hotunan idanuna na hango katon question akan kowannen su zuciyata na tamvaya na anya kuwa babu lauje a cikin nadi??.
Da sauri na koma na hau tattare hotunan na janyo drawer ta gefen gado na watsa su ciki tare da fadawa toilet da sauri na, dole in zauna in sake tunani kafin in yanke hukuncin abinda ya dace inyi, ina rufe kofar bayin naji shigowar Abbu dakin....
Ganin bana dakin yasa ya fita daga dakin tare da maida min kofar dakin ya rufe. Na kurawa kaina idanu a jikin mirror ina kallon reflection dina, kwalliyar da nayi ta hade da ruwa da hawaye ta maida ni kamar zombie. Ruwa da sabulu nasa na wanke fuskana na kara yin wata kwalliyar kafin na fita, akan kujera na gan shi a zaune. Yana ganina ya saki murmushi mai taushi, yayin da naji gabana ya fadi sosai, anya zan iya daurewa kuwa? Don a daidai lokacin zuciyata tana kitsa min in ci kwalar shi ne kawai. Na daure na kakalo murmushi wanda nasan ko fatar bakina bai gama hadewa bama, a sanyaye na karasa kusa dashi na dan duka tare da cewa “Abbu sannu da zuwa" ya amsa yana murmushi, “kin ga na dade koh?" na gyada mishi kai kawai, yace “wai gidan Rahina na biya, shine ta hado ni da kaya ma tace in kawo miki" ya miko min ledar daya shigo da ita na amsa tare da dubawa, turaren wuta ne sai wani kamar na tsuguno idan ban manta ba naga irin shi cikin kayayyakin da aka hado min daga gida. Na maida ledar na rufe tare da kallon shi nace “abinci?" ya lumshe idanu tare da gyada kai, “please, m hungry... Very" da ace zuciyana cikin kwanciyar hankali take da babu abinda zai hana ni kamo fuskar shi in bashi sumba a baki, a yanzu kam koda tunanin ya fado cikin raina I found it disgusting sosai. Sai kawai nayi wajen dinning table ban ko yi magana ba yayin da naji lokacin daya tashi ya biyo bayana.
Abincin na hau zuba mishi, gabadaya cikina a cushe yake nasan sam babu abinda zai shiga cikina a lokacin don haka na zuba mishi iya wanda zai iya ci kawai, ina gamawa na tura mishi su gaban shi na juya da niyar tafiya yayi saurin sa hannu ya riko hannuna, ji nayi kamar garwashi ya taba ni, kallona yayi sosai, “ina zaki je haka? Ba zaki ci abincin bane?" na girgiza kai tare da kallon shi, “naci tun dazu da naga baka dawo ba" ya kara kallona kamar wanda bai yarda da abinda nace ba kafin naga yayi murmushi tare da jan kujerar gefen shi tayi baya ya zaunar dani, “ok, zauna ki taya ni hira toh, kin san cewa dai bana jin dadin cin abinci idan ba kya gefena koh?".
Haka na zauna tare da kurawa kasan carpet din idanu ina ta saka da warwara, ban san lokacin daya gama cin abincin ba, ya juyo dani na fuskance shi, “baby, me ke damun ki ne?" ya fada cikin nuna damuwa da halin da rashin walwalata a gare shi, nima nasan cewa yaudarar kaina kawai nake yi idan har nace wai zan iya pretending inyi behaving kamar yadda na saba.
Na girgiza kaina kawai, “babu komi Abbu, bana jin dadin jikina ne kawai" da sauri ya dora hannun shi akan goshina yaji babu zafi, ya dawo dashi wuya nan ma komi normal, yace “amma jikin ki lafiya lau... Are you sure ba sai mun je asibiti ba??" nayi saurin gyada kai, “m ok" yace “idan kin ji da wani abu don't hesitate fa, ki sanar dani" na gyada mishi kai, yayi murmushi tare da cewa “good girl" fuskana ya matso daidai tashi tare da kawo bakin shi saitin nawa, ina fahimtar abinda yake shirin yi nayi saurin kauda kaina gefe ta yadda leben shi ya kare da sauka akan kumatuna ba lebe na ba, ya dago ya kalleni cike da alamun tambaya, da sauri na tashi na tattara kayan da yayi amfani dasu na kai kicin. Wanke su nayi tare da dora abincin dare, ya leko kicin din ganin ina girki yazo ya kashe gas din, a hankali na dago na kalleshi amma ban yi magana ba, kafada ya daga cikin alamun tsokana “hey chill! Ba sai kinyi girki ba yau, zan fita in sayo mana abinci" sai kawai na juya na sauke tukunyar dana dora na zubar da ruwan tare da rabawa ta gefen shi na fita.
Ina gaban wardrobe dina ina shirya kayan ciki wadanda na ciro su daga ciki musamman saboda in dauke hankalina daga tunanika, Abbu ya sake shigowa dakin. Gefen gado ya samu ya zauna yayi tagumi tare da zuba min idanu wadanda seriously na dinga jin su a cikin jikina kamar me?? Kokari nake kawai naci gaba da aikina. Can kasan zuciyata ina so in mishi maganar, sai dai ina matukar tsoron abinda xai fito daga bakinshi, ina tsoron ya amsa min da ehh shine don a hakikanin gaskiya ban san ina zan jefa rayuwata idan hakan ta kasance ba.
Haka muka wanzu har aka kira sallar Magrib, Abbu ya tashi ya shiga toilet dina ya fito daure da alwala ya wuce masallaci, sai dana ga fitar shi sannan ne nima na dauro alwalar naxo na tada kabbarar sallah, anan kan sallayar na zauna bayan na gama ina laxumi har aka yi Isha'i nayi sallah. Tashi nayi na nade abin sallar, ina ta en kimtse-kimtse na wanda a zahirin gaskiya basu da amfani ina yi kawai don kada su dauke mun tunani, Abbu ya dawo daga masallaci. Dakin kawai ya leko yace in fita mu ci abinci. Na fita falon na same shi har ya fiddo plates waje, naje gefen shi na zauna kawai.
Gashin nama ya xuba mana cikin plate din da yoghurt a cikin cups, na sa cokali muka fara ci daga cikin kwano daya. Ba wai don wani abu ko yunwa nake cin abincin ba, kawai saboda bana so Abbu ya dame ni da korafi ne don a lokacin ko kadan bana so inyi magana, gabadaya raina a jagule yake. Abu na karshe da nake bukatar yi shine in kadaice a waje guda in nemi mafita a cikin rayuwata data aurena gabadaya.
Duk da halin da nake ciki hakan bai hana ni jin dadin naman ba har ma ban san lokacin dana bude ciki naci naman sosai ba, sai dana ji cikina ya cika kafin na kora da yogurt din, lokacin Abbu ya ture kwanon gefe alamun ya koshi don haka na tattara kayan na kai kicin, sauran kayan duk na saka su a cikin freezer na fita falo. Abbu yana zaune akan kujera yana kallon labaran kasa, na shige shi zuwa dakinshi da yake yanzu yawancin kayana ma suna dakin don ragewa kaina wahalar je ka dawo daga wannan dakin zuwa wancan. Toilet na shiga nayi brush na fito na shirya cikin kayan barci tare da fesa en turaruka na kwanta. Not that barci nake ji ko kuma gajiya, kawai ina gujewa Abbu ne.
Misalin karfe tara Abbu ya shigo dakin, ina jin alamun shigowar shi na kara lafewa akan gado kamar mai barci. Ina ji ya gama duk abubuwan da zai yi kamar su brush, shafa turare, sa kayan barci da sauran su. Ina jin lokacin daya kashe wutar dakin kafin inji alamun hawan shi kan gadon, na kara sakankance jikina sosai. Ina jin lokacin daya janyo ni jikinsa, duk da ihun da naji ana min a kunne akan in kwace jikina sharewa nayi, bana so inyi abinda zai sa Abbu yayi zaton idanu na biyu. Ina jin shi yana lalubata wanda da da ne tashi zanyi koda barcin nake yi in shige cikin kirjin Abbuna mai fadi, yau kam ban yi hakan ba.
Bayan lokaci mai tsayi naji alamun yayi barci, a hankali na zare jikina daga nashi tare da juya mishi baya, wasu siraran hawaye suna gangaro min a kumatu, ban san yaushe barci ya kwashe ni ba. Da asubahi Abbu ya tashe ni daga barci ya wuce masallaci. Ina kan sallaya ina karatu lokacin daya dawo daga masallacin, kan gado ya hau ya kwanta rigingine, ban motsa daga inda nake ba har sai da gari yayi sha, na rufe al-qur'anin na mayar dashi inda ake ajiye shi na fita daga dakin. Kicin na shiga na fara shirya break fast.