Sashe 85
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Kamar yadda nasan cewa kin kula da yanayin zamana da Ibrahim Zama ne kawai muke yi wanda babu armashi ko na kankani. Auran hadi aka mana da Ibrahim ba tare da son mu ba, lokacin ina da wanda nake so. Haka aka kaini gidan Ibrahim ba don naso ba tunda duk yadda naso inyi akan kada ayi auren abin ya faskara. Ibrahim yana kyautata min a matsayin shi na wanda baya so na ma, amma ni na kasa yakar zuciyata akan ta so shi. Ina can ina karewa Mahmud wanda nake so mutuncina wanda kullum sai mun yi waya dashi ya jaddada min in rike mishi amana dai. Duk batanci na duniya babu kalar da ban yiwa Ibrahim akan ya sake ni ba amma yayi biris dani hakan shi yake kara min jin kin shi a raina. It took us almost a year kafin mu kusanci juna, shima ni da kaina naji ina son yin hakan na kai kaina gare shi. Daga nan muka ci gaba da rayuwar ma'aurata amma fa idan naga dama don wani lokacin ko ya neme ni ma sai inyi refusing dinsa, idan kuma ya matsa to sai dai ya biya ni kudin sannan..." tayi shiru hawaye ya zubo mata, yayin da nake jijjiga kai cikin mamaki. Ban taba zaton cewa alakar Abbu da Anty Mubeenah tayi muni irin haka ba, Anty taci gaba...
“Cikin haka na samu cikin Abdullahi, yeah naji dadin samun cikin saboda a lokacin zugar en uwana tayi tasiri akaina da suka ce idan na fara haihuwa a gidan Ibrahim yayana zasu zama magada saboda duk da cewa a lokacin yana karatun masters, amma yana da kudi don bai dogara da kudin mahaifin shi ba, ya dogara da kanshi. Sai dai bayan haihuwar Abdullahi da wata takwas dana kara samun wani cikin mai dan banzan wahala sai naji ina dana sani akan amincewata akan haihuwa. Mun sha danbarwa da Ibrahim akan cikin nan, nayi yunkurin zubar dashi sau ba adadi Allah ya nufa sai da yazo duniya. Wallahi Nafeesah sai da muka tsadance da Ibrahim ya biyani sannan na shayar da jaririn. Watan shi bakwai na yaye shi, babu ruwana da harkar yaran su duka shi yasa zaki ga shakuwar mu dasu bata yi zurfi sosai ba kamar yadda suka shaku da Ibrahim.
Bayan shekaru biyu na sake haihuwar Hafsy, daga nan ne naje asibiti aka saka min loop a mahaifa ta saboda bana son haihuwa da Ibrahim...."
Na zaro idanu waje sosai cikin tsananin mamaki, “loop Anty?" ta gyada kai, “abin ya ba Ibrahim haushi sosai, ya jima yana fushi dani kafin ya sauko ya hau lallashina akan in je a cire min ni kuma nayi biris dani har ya gaji ya daina yace zai karo aure, at first na firgita da jin haka daga karshe da naji shiru sai nayi zaton cewa tsakuwa ce yake taunawa don aya taji tsoro sai kwatsam naji zancen auren shi da ke. In fada miki na firgita ma bata baki ne, na shiga shock bana kadan ba sai dai na cije saboda a gani na bana son Ibrahim meye nawa na jin haushi don zai kara aure? Sai daga baya na fahimci I was wrong! Ina son Ibrahim rashin kulawa irin nawa ne ya hana ni gane hakan, sai daga baya ne bayan ya daga min murya a karo na farko a tarihin rayuwar auren mu, sannan na fahimci halin da zuciyata take ciki game dashi amma ban san ko ta wace hanya zan sanar dashi ba Don haka naja bakina nayi shiru. Amma a en kwanakin nan gabadaya na rasa abinda yake min dadi, shi kuma kamar ya sani, yanzu ko kiran shi nayi a waya baya dauka ma. Zuciyata tana azabtuwa da hakan ba zan iya cigaba da jurewa ba, amma da wani ido zan kalli Ubangijina bayan abubuwan dana aikatawa mijina? Tell me, bayan duk my man and abubuwan nan dana aikata, da wani ido kike so in kalli Ibrahim??".
Na kalleta tun daga sama har kasa, tabbas ta banbanta da Mubeenar dana sani a da. Wannan Mubeenar ba wadda take cike da self esteem bace, sai wata Mubeenah wadda nadama take nukurkusarta. Tausayinta ya mamaye ni matuka.
Nace “kada ki ce haka Anty, shi Allah Gafurur-Raheem ne, yana yafe kuskuran damu muka aikata a gare shi matukar tuban muke nema da gaske. Abbu ma haka ne, ina tabbatar miki da cewa shi zai fi ma kowa jin dadin canzawar ki Anty" ta kalleni da sauri, “da gaske?" na gyada mata kai ina murmushi. Tace “to yanzu me kike so inyi?" nace “abu na farko daya kamata kiyi shine kije ki cire loop din jikinki, bayan hana haihuwa yana da side effects a jikinmu ba kadan ba, bana tantama kibar jikinki loop ne ya assasa miki ita" ta gyada kai cikin nuna yarda da abinda nace, “nima nayi tunanin haka. In Allah ya yarda gobe zan koma asibitin a cire min" nayi murmushin jin dadi, “we will do the other things later then... Bari inje in kwanta haka nan" na mata sai da safe na wuce.
Har na kusa kofata naji ta kira sunana, “Nafeesah!" na juya a hankali, “it was not bad opening up to you.." nayi murmushi sosai, “Anytime Anty" na shige dakin tare da rufo kofata na koma kan gado na kwanta. Tunanin yadda muka kare da Anty na dinga yi, na tsinci kaina da addu'ar Allah yasa ta dore a haka, Allah kuma ya bamu zaman lafiyar da a kullum nake mana addu'ah. Da haka barci ya dauke ni cike da mafarkai iri-iri, mafi yawa daga cikin su shine na wani kyakkyawan yaro da yake bina da tuffa a hannu, na tashi da dan murmushi a fuskata. Addu'a nayi na shafa a fuskata na tashi na fada toilet na dauro alwala nazo nayi sallah.
Da yake ranar Anty ta karbi girki, ban fita falo ba sai da karfe tara tayi. Yara sun tafi makaranta, dana tambayi Harira Anty Mubeenah tace tace a fada min ta tafi asibiti, nayi murmushi kawai. Abinci na zauna naci, nayi gefe da plates din a zuciyata ina raya lokacin barin Harira gidan yayi.
Lokacin da Anty ta dawo har dakina ta leko ta same ni, tace “sun rubuta min magunguna in sha na sati daya sai in koma a cire min" nace “to Allah yasa mu dace" tace “ameen."
Daga ranar alakar mu da Anty Mubeenah ta canza, su kansu yaran sun yi mamaki kuma sun ji dadin hakan kada ma dai Abbu yaji labari wanda nake updating din shi da duk abinda ke faruwa. Ni'imah ta sake haihuwar diya Mace, a ranar muka je muka yi barka ni da Anty Mubeenah. A cikin mota muna dawowa nayi shiru ina tunanin anya a duniya zan ma haihu kuwa? Na tuna ina cikin shekarar aure ta uku kenan zuwa hudu amma har yau shiru babu bayani ko batan wata ban taba yi ba. Mommy tace wai itama hakan ce ta faru da ita, sai a cikin shekararta ta biyar ne sannan ta samu cikina, nayi ajiyar numfashi a hankali ina addu'ar idan da rabona Allah ya kawo masu albarka.
Anty Mubeenah taje an cire mata loop din, sai dai ance sabida jimawar abin a jikinta babu wata kulawa irin yadda ya kamata, ya taba mata mahaifa saboda haka da kyar mahaifar ta iya daukar ciki nan gaba. Hankalinta ya tashi kwarai da jin haka ni na dinga kwantar mata da hankali har ta nutsu. Ni na bata shawarar shiga From My Kitchen Institute da yake Allah ya budawa mai makarantar Hadiza Dogon Daji ta bude reshe anan Kano bayan na Abuja, inda ta fara koyon salon girke girke ina kuma taimaka mata da wasu abubuwa. A gefe guda kuma na dora ta akan weight loss da slimming. Kullum muna gym muna aikin motsa jiki. Abbu ya dawo yayi sati daya ya tafi wata seminar inda daya dawo za a bashi VC.
Cikin wata daya kacal idan ba mugun sanin Anty Mubeenah kayi ba idan ka ganta a hanya ba zaka gane ta ba. Wannan kibar marar fasali da rashin gyara duk ya tafi babu shi, ta dawo tayi wani fresh da ita Masha Allah! Duk da dai har yanzu da sauran kibar amma ta ragu sosai. Musamman ta siya form din wata islamiyah anan bayan gidanmu inda take zuwa daukar karatu kowace rana da yamma, karfe hudu zuwa shida. Ko a yanzu kam Alhamdulillah! Zama na da kishiyata ya canza, idan ka ganmu zaka yi zaton cewa wasu shakikai ne ba kishiyoyi ba.
Result dinmu ya fita, sakamako yayi kyau sosai. Nayi clearance da komi, Abbu kadai nake jira ya dawo in nemi izinin shi in fara aiki da Lab din Aminu Kano Teaching Hospital.
“Cikin haka na samu cikin Abdullahi, yeah naji dadin samun cikin saboda a lokacin zugar en uwana tayi tasiri akaina da suka ce idan na fara haihuwa a gidan Ibrahim yayana zasu zama magada saboda duk da cewa a lokacin yana karatun masters, amma yana da kudi don bai dogara da kudin mahaifin shi ba, ya dogara da kanshi. Sai dai bayan haihuwar Abdullahi da wata takwas dana kara samun wani cikin mai dan banzan wahala sai naji ina dana sani akan amincewata akan haihuwa. Mun sha danbarwa da Ibrahim akan cikin nan, nayi yunkurin zubar dashi sau ba adadi Allah ya nufa sai da yazo duniya. Wallahi Nafeesah sai da muka tsadance da Ibrahim ya biyani sannan na shayar da jaririn. Watan shi bakwai na yaye shi, babu ruwana da harkar yaran su duka shi yasa zaki ga shakuwar mu dasu bata yi zurfi sosai ba kamar yadda suka shaku da Ibrahim.
Bayan shekaru biyu na sake haihuwar Hafsy, daga nan ne naje asibiti aka saka min loop a mahaifa ta saboda bana son haihuwa da Ibrahim...."
Na zaro idanu waje sosai cikin tsananin mamaki, “loop Anty?" ta gyada kai, “abin ya ba Ibrahim haushi sosai, ya jima yana fushi dani kafin ya sauko ya hau lallashina akan in je a cire min ni kuma nayi biris dani har ya gaji ya daina yace zai karo aure, at first na firgita da jin haka daga karshe da naji shiru sai nayi zaton cewa tsakuwa ce yake taunawa don aya taji tsoro sai kwatsam naji zancen auren shi da ke. In fada miki na firgita ma bata baki ne, na shiga shock bana kadan ba sai dai na cije saboda a gani na bana son Ibrahim meye nawa na jin haushi don zai kara aure? Sai daga baya na fahimci I was wrong! Ina son Ibrahim rashin kulawa irin nawa ne ya hana ni gane hakan, sai daga baya ne bayan ya daga min murya a karo na farko a tarihin rayuwar auren mu, sannan na fahimci halin da zuciyata take ciki game dashi amma ban san ko ta wace hanya zan sanar dashi ba Don haka naja bakina nayi shiru. Amma a en kwanakin nan gabadaya na rasa abinda yake min dadi, shi kuma kamar ya sani, yanzu ko kiran shi nayi a waya baya dauka ma. Zuciyata tana azabtuwa da hakan ba zan iya cigaba da jurewa ba, amma da wani ido zan kalli Ubangijina bayan abubuwan dana aikatawa mijina? Tell me, bayan duk my man and abubuwan nan dana aikata, da wani ido kike so in kalli Ibrahim??".
Na kalleta tun daga sama har kasa, tabbas ta banbanta da Mubeenar dana sani a da. Wannan Mubeenar ba wadda take cike da self esteem bace, sai wata Mubeenah wadda nadama take nukurkusarta. Tausayinta ya mamaye ni matuka.
Nace “kada ki ce haka Anty, shi Allah Gafurur-Raheem ne, yana yafe kuskuran damu muka aikata a gare shi matukar tuban muke nema da gaske. Abbu ma haka ne, ina tabbatar miki da cewa shi zai fi ma kowa jin dadin canzawar ki Anty" ta kalleni da sauri, “da gaske?" na gyada mata kai ina murmushi. Tace “to yanzu me kike so inyi?" nace “abu na farko daya kamata kiyi shine kije ki cire loop din jikinki, bayan hana haihuwa yana da side effects a jikinmu ba kadan ba, bana tantama kibar jikinki loop ne ya assasa miki ita" ta gyada kai cikin nuna yarda da abinda nace, “nima nayi tunanin haka. In Allah ya yarda gobe zan koma asibitin a cire min" nayi murmushin jin dadi, “we will do the other things later then... Bari inje in kwanta haka nan" na mata sai da safe na wuce.
Har na kusa kofata naji ta kira sunana, “Nafeesah!" na juya a hankali, “it was not bad opening up to you.." nayi murmushi sosai, “Anytime Anty" na shige dakin tare da rufo kofata na koma kan gado na kwanta. Tunanin yadda muka kare da Anty na dinga yi, na tsinci kaina da addu'ar Allah yasa ta dore a haka, Allah kuma ya bamu zaman lafiyar da a kullum nake mana addu'ah. Da haka barci ya dauke ni cike da mafarkai iri-iri, mafi yawa daga cikin su shine na wani kyakkyawan yaro da yake bina da tuffa a hannu, na tashi da dan murmushi a fuskata. Addu'a nayi na shafa a fuskata na tashi na fada toilet na dauro alwala nazo nayi sallah.
Da yake ranar Anty ta karbi girki, ban fita falo ba sai da karfe tara tayi. Yara sun tafi makaranta, dana tambayi Harira Anty Mubeenah tace tace a fada min ta tafi asibiti, nayi murmushi kawai. Abinci na zauna naci, nayi gefe da plates din a zuciyata ina raya lokacin barin Harira gidan yayi.
Lokacin da Anty ta dawo har dakina ta leko ta same ni, tace “sun rubuta min magunguna in sha na sati daya sai in koma a cire min" nace “to Allah yasa mu dace" tace “ameen."
Daga ranar alakar mu da Anty Mubeenah ta canza, su kansu yaran sun yi mamaki kuma sun ji dadin hakan kada ma dai Abbu yaji labari wanda nake updating din shi da duk abinda ke faruwa. Ni'imah ta sake haihuwar diya Mace, a ranar muka je muka yi barka ni da Anty Mubeenah. A cikin mota muna dawowa nayi shiru ina tunanin anya a duniya zan ma haihu kuwa? Na tuna ina cikin shekarar aure ta uku kenan zuwa hudu amma har yau shiru babu bayani ko batan wata ban taba yi ba. Mommy tace wai itama hakan ce ta faru da ita, sai a cikin shekararta ta biyar ne sannan ta samu cikina, nayi ajiyar numfashi a hankali ina addu'ar idan da rabona Allah ya kawo masu albarka.
Anty Mubeenah taje an cire mata loop din, sai dai ance sabida jimawar abin a jikinta babu wata kulawa irin yadda ya kamata, ya taba mata mahaifa saboda haka da kyar mahaifar ta iya daukar ciki nan gaba. Hankalinta ya tashi kwarai da jin haka ni na dinga kwantar mata da hankali har ta nutsu. Ni na bata shawarar shiga From My Kitchen Institute da yake Allah ya budawa mai makarantar Hadiza Dogon Daji ta bude reshe anan Kano bayan na Abuja, inda ta fara koyon salon girke girke ina kuma taimaka mata da wasu abubuwa. A gefe guda kuma na dora ta akan weight loss da slimming. Kullum muna gym muna aikin motsa jiki. Abbu ya dawo yayi sati daya ya tafi wata seminar inda daya dawo za a bashi VC.
Cikin wata daya kacal idan ba mugun sanin Anty Mubeenah kayi ba idan ka ganta a hanya ba zaka gane ta ba. Wannan kibar marar fasali da rashin gyara duk ya tafi babu shi, ta dawo tayi wani fresh da ita Masha Allah! Duk da dai har yanzu da sauran kibar amma ta ragu sosai. Musamman ta siya form din wata islamiyah anan bayan gidanmu inda take zuwa daukar karatu kowace rana da yamma, karfe hudu zuwa shida. Ko a yanzu kam Alhamdulillah! Zama na da kishiyata ya canza, idan ka ganmu zaka yi zaton cewa wasu shakikai ne ba kishiyoyi ba.
Result dinmu ya fita, sakamako yayi kyau sosai. Nayi clearance da komi, Abbu kadai nake jira ya dawo in nemi izinin shi in fara aiki da Lab din Aminu Kano Teaching Hospital.