Sashe 40
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 7 min read
Harith yayi parking motar shi a kofar gidanmu, da yake ya dawo tun last week. Yau tsokana muka fita, gidan su Ikram budurwar shi muka je da yake itama tazo hutu. Har kofar gidansu muka je aka mata sallama ta fito da saurinta ita ala dole masoyinta yazo, yadda tayi turus ganina akan motar shi ina wasa da keys din motar shi sai daya kusa bata mana budget, kaina na kawar gefe ina boye dariyar data kama ni. Haka ta daure ta karaso wajenmu muka gaisa Harith ya gabatar dani a matsayin sister dinshi, suka dan fara hira da ita, mintuna biyar basu cika ba na kalli Harith ina hamma nace "Hari, mu tafi gida!" da sauri ya mata sallama muka shige mota muka tafi, tana tsaye a inda take har muka bar layin. Dariyar abun muke yi har muka shiga gida kamar wasu sabbin mahaukata. Idanuna suka tsaya cak akan Abbu dake zaune akan fararen kujeru inda Daddy ya saba zama yana shan iska ko karatun jarida mostly on weekends. Kamar koda yaushe, babu abinda ya canza daga bugun da zuciyata take a duk lokacin dana ganshi, rawar da kafafuna suke da wani irin doki daya mamaye ni, makaman yakin dana tanada domin yakar zuciyar dake kayata min Abbu naji sun min nauyin dauka. Idanunshi fes akan mu suke, na kalli Harith a nutse nace "ina xuwa" ya gyada min kai. A hankali na fara tafiya zuwa inda yake zaune, kafafuna rawa suke yi saboda yadda nake jin idanun shi masu kaifi a kaina, da taimakon Allah dai na karasa inda yake. Na dan duka a hankali nace "Abbu barka da yamma" ya gyada kai, "barka dai Nafeesah. Daga ina haka?" na rasa abinda zan ce mishi saboda ba makaranta naje ba saboda ranar bamu yi exams ba, nace "mun dan fita ne" ya kalli kofar da Harith ya bi ya shiga falo ya kara kallona fuskar shi dauke da wani irin kallo daya kada min sassan jiki, "and who is he??" nima na kalli kofar, nasan da Harith yake, nace "Harith...." na rasa abin cewa saboda yadda idanunshi suke zagaye fuskata gabadaya sun dauke min kuzari, ganin nayi shiru babu amsa ya gyada kai, "well dama naso ganin Daddyn ki ne shi yasa na zauna jiran shi nayi zaton zai dawo da wuri don na biya ta ofishin shi baya nan, but bana tunanin zan cigaba da jira kam. Zan kira shi kawai" ya tashi yana gyara wuyan rigar shaddar daya saka, ya kalleni har zuwa lokacin normal kallonshi bai dawo ba, yace "Kano na nufa yanxu in shaa Allah. Nan da sati daya zaki zo bikin su Ni'imah koh?" na gyada mishi kaina a hankali, yace "good! Sai mun hadu kenan" ya fara tattaki xuwa inda ya ajiye motar shi, na samu kaina da take mishi baya har gaban motar. Ya saka makulli ya bude motar ya shiga ya kunna, sai lokacin ya juyo ya kalleni yana dan murmushi, Ya Allah! Da ba dan motar shi dana rike da hannuna ba da babu abinda zai hana ni faduwa a lokacin, na rasa irin effect din da Abbu yake dashi a tare dani. Yace "so??" nayi saurin kallonshi saboda gabadaya hankalina ya dauke daga gare shi, nayi saurin daidaita natsuwata nace "Allah ya sauke ka lafiya Abbu, a gaida su Anty Mubeenah da Hafsy" yayi murmushi wannan karon genuinely wanda tunda yaxo sai lokacin naga murmushin shi irin haka, yace "Ameen Nafeesah, zasu ji in shaa Allah!" yaja motar shi ya tafi nima na wuce cikin gida, a bakin kofa muka ci karo da Harith zai fito, yana gani na yace "sai anjima koh babe?" na harare shi ya danyi dariya saboda yasan na tsani sunan, ya wuce abinshi ni kuma na shige gida. Sai dana biya ta dakin Mommy na gaya mata na dawo, ta kalleni fuskarta babu yabo babu fallasa, "kin ga Baban Hafsat a waje kuwa?" gabana ya dan fadi, Allah dai yasa ba wani fadan zan sha ba. Nace "ehh, ya ma tafi ai" Mommy ta kalleni cikin tuhuma, na sadda kaina kasa ina wasa da jakar hannuna, tace "na tambaye ki abinda ke tsakaninku kin ce babu komi, yanzu kuma me ya kawo shi wajen ki?" na kalleta da sauri, "ni fa ba wajena yazo ba wajen Daddy yazo, ya gaji da jiran dawowar shi ne shi yasa ya tafi" tace "haka ya gaya miki?" nace "ehhh, ba haka bane?" ta dan harare ni na kauda kaina, tace "shi kenan je ki" kamar jira nake yi dama, da sauri na bar mata dakin na wuce nawa ina ajiye numfashi a hankali. Duk yadda Tunanin Abinda Mommy take nufi da Tunanin makomar rayuwata da Abbu suka so dabaibaye ni haka naki basu dama, na dage da karatun exams sosai. Cikin ikon Allah cikin sati daya muka gama exams dinmu, cikin lokacin mun kara zuwa gidan su Ikram sau biyu. Wato idan na tuno diramar da muka buga a zuwanmu na karshe gidansu dariyar dake kama ni koh??
Sai ana washegari a fara harkokin bikin su Ni'imah sannan na tafi Kano. Gidan Anty Ameenah muka sauka directly saboda a can amaren suke zaman biki, su Hafsy suka fito suka min oyoyo yaran sun wani kara girma, ban taba sanin nayi kewar su sosai ba sai dana dora idanuna a kansu. Qaseem ne ya dauki jakar hannuna na kama hannun Hafsy Abdullahi ya biyo mu a baya muka shiga gidan. Tarbar dana samu daga Anty Ameenah ta bani mamaki, har uwar dakinta ta kaini inda na samu su Anty Raliya da wasu abokan su, na gaida su suka amsa Anty Raliya na min korafin na tafi babu sallama ni dai nawa bada hakuri ne kawai don nasan cewa m at fault. Na shiga bandakin ta na watsa ruwa na fito nayi sallar Laasar, kafin in gama har an shirya min abinci a tsakiyar dakin ina gamawa na zauna na fara ci. Sai dana gama sannan aka kaini inda amaren suke. Dakine guda aka ware musu inda ake musu gyaran jiki, ina shiga hayaniya ta barke kamar me. Sai a lokacin aka min kitso da kunshi Allah ma yasa na je wankin kai a Kaduna.
Washegari aka yi kamu a Triple Crown Reception Masha Allah wajen ya tsaru iya tsaruwa, mata ne zallah a wajen mun yi shiga ta gargajiya haka ma kide-kiden da aka sa na gargajiya ne zallah. A wajen kamun ne muka hadu da Anty Mubeenah, tana nan yadda take babu abinda ya ragu a yanda take. Kibar nan tata marar fasali ta karu, table daya suka ja ita da kanwar ta Anty Shakira, ta hakimce tana ta hure-huren hanci yayin da su Anty Ameenah suke ta kai kawo suna kokarin entertaining din baki. Na ja hannun Ramlah muka nufi teburin da suke zaune, tun kafin mu karasa nake yago hakora ina murmushi har muka gaban su na musu sallama tare da gaida su, I didn't expected her to look at me with a smile on her face, tace "Nafeesah sai a haka ake ganin ku ko?" ko babu komi naji dadin yadda tayi, nayi zaton wulakanci zan sha a wajenta kam. Nayi er dariya kawai na zauna a gefen Anty Shakira ina kara gaishe su, nan muka dan yi hirar yaushe gamo kafin na musu sallama na tashi muka cigaba da gudanar da sha'anin bikin mu. Bayan mun koma gida da dare na shiga dakin Anty Ameenah zan dauko kayan barcina da yake tunda naxo kayana suna dakinta, ina yin sallama muryar Abbu ta amsa min, sai dana yi kamar in koma da baya don dai kawai nasan yaji murya ta ne shi yasa. Na shiga cikin falon a hankali kaina a kasa kamar tsohuwar munafuka, daga can gefen shi na durkusa nace "Abbu sannu da zuwa!" muryar shi tayi kasa sosai akwai alamun gajiya sosai a tattare dashi, yace "yauwa Nafeesah, bani ruwa please!" nace toh. Na fita zuwa kicin naje na dauko mishi ruwa mai dan sanyi, har zan fito na kula da farfesun kayan cikin dake cikin warmer, na koma na dauko plate na zuba a ciki na cicciba. Na dire kayan a gaban shi, ya kalleni ya Kalli abincin, fuskar shi ta nuna alamun relaxing and amusement. Ya kalleni cikin lumsassun idanunshi, "Nafeesah!!" ya kira sunana cikin muryar rada, na kalleshi a hankali ba tare dana amsa ba, it's not that ban amsa ba, nayi niyar amsawa sai dai muryata bata fita ne balle har yaji, yace "Nafeesah!! Zaki iya....." maganar shi ta katse lokacin da Anty Ameenah ta shigo falon, na kalleshi da sauri cikin mamakin dalilin tsayawar maganar shi. Anty Ameenah ta zauna a gefen shi cike da tsokana tace "ya aka yi Ibu??" na sadda kaina kasa ina kokarin boye dariyar data taso min da jin sunan da Anty Ameenah ta kira shi dashi, ya dan ja tsaki kawai ya fara cin abinda na ajiye mishi. Ganin haka na tashi na shiga dakin na dauko kayana na fito na musu sai da safe na fita, idanun su suna kaina har na fita. Na kai gadon bayana akan katifar da aka shimfida mana a tsakiyar dakin na kwanta, tunanina a lokacin me Abbu yaso fada min dazu??
Sai ana washegari a fara harkokin bikin su Ni'imah sannan na tafi Kano. Gidan Anty Ameenah muka sauka directly saboda a can amaren suke zaman biki, su Hafsy suka fito suka min oyoyo yaran sun wani kara girma, ban taba sanin nayi kewar su sosai ba sai dana dora idanuna a kansu. Qaseem ne ya dauki jakar hannuna na kama hannun Hafsy Abdullahi ya biyo mu a baya muka shiga gidan. Tarbar dana samu daga Anty Ameenah ta bani mamaki, har uwar dakinta ta kaini inda na samu su Anty Raliya da wasu abokan su, na gaida su suka amsa Anty Raliya na min korafin na tafi babu sallama ni dai nawa bada hakuri ne kawai don nasan cewa m at fault. Na shiga bandakin ta na watsa ruwa na fito nayi sallar Laasar, kafin in gama har an shirya min abinci a tsakiyar dakin ina gamawa na zauna na fara ci. Sai dana gama sannan aka kaini inda amaren suke. Dakine guda aka ware musu inda ake musu gyaran jiki, ina shiga hayaniya ta barke kamar me. Sai a lokacin aka min kitso da kunshi Allah ma yasa na je wankin kai a Kaduna.
Washegari aka yi kamu a Triple Crown Reception Masha Allah wajen ya tsaru iya tsaruwa, mata ne zallah a wajen mun yi shiga ta gargajiya haka ma kide-kiden da aka sa na gargajiya ne zallah. A wajen kamun ne muka hadu da Anty Mubeenah, tana nan yadda take babu abinda ya ragu a yanda take. Kibar nan tata marar fasali ta karu, table daya suka ja ita da kanwar ta Anty Shakira, ta hakimce tana ta hure-huren hanci yayin da su Anty Ameenah suke ta kai kawo suna kokarin entertaining din baki. Na ja hannun Ramlah muka nufi teburin da suke zaune, tun kafin mu karasa nake yago hakora ina murmushi har muka gaban su na musu sallama tare da gaida su, I didn't expected her to look at me with a smile on her face, tace "Nafeesah sai a haka ake ganin ku ko?" ko babu komi naji dadin yadda tayi, nayi zaton wulakanci zan sha a wajenta kam. Nayi er dariya kawai na zauna a gefen Anty Shakira ina kara gaishe su, nan muka dan yi hirar yaushe gamo kafin na musu sallama na tashi muka cigaba da gudanar da sha'anin bikin mu. Bayan mun koma gida da dare na shiga dakin Anty Ameenah zan dauko kayan barcina da yake tunda naxo kayana suna dakinta, ina yin sallama muryar Abbu ta amsa min, sai dana yi kamar in koma da baya don dai kawai nasan yaji murya ta ne shi yasa. Na shiga cikin falon a hankali kaina a kasa kamar tsohuwar munafuka, daga can gefen shi na durkusa nace "Abbu sannu da zuwa!" muryar shi tayi kasa sosai akwai alamun gajiya sosai a tattare dashi, yace "yauwa Nafeesah, bani ruwa please!" nace toh. Na fita zuwa kicin naje na dauko mishi ruwa mai dan sanyi, har zan fito na kula da farfesun kayan cikin dake cikin warmer, na koma na dauko plate na zuba a ciki na cicciba. Na dire kayan a gaban shi, ya kalleni ya Kalli abincin, fuskar shi ta nuna alamun relaxing and amusement. Ya kalleni cikin lumsassun idanunshi, "Nafeesah!!" ya kira sunana cikin muryar rada, na kalleshi a hankali ba tare dana amsa ba, it's not that ban amsa ba, nayi niyar amsawa sai dai muryata bata fita ne balle har yaji, yace "Nafeesah!! Zaki iya....." maganar shi ta katse lokacin da Anty Ameenah ta shigo falon, na kalleshi da sauri cikin mamakin dalilin tsayawar maganar shi. Anty Ameenah ta zauna a gefen shi cike da tsokana tace "ya aka yi Ibu??" na sadda kaina kasa ina kokarin boye dariyar data taso min da jin sunan da Anty Ameenah ta kira shi dashi, ya dan ja tsaki kawai ya fara cin abinda na ajiye mishi. Ganin haka na tashi na shiga dakin na dauko kayana na fito na musu sai da safe na fita, idanun su suna kaina har na fita. Na kai gadon bayana akan katifar da aka shimfida mana a tsakiyar dakin na kwanta, tunanina a lokacin me Abbu yaso fada min dazu??