← Book details Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 88

Sashe 30

Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 5 min read

Yana ajiye wayar ya lumshe idanunshi tare da maida bayan shi ya jinginar da study table din da yake kai a zaune. Nafeesah! Nafeesah!! Sunan dake ta shawagi kenan a tsakiyar kanshi a lokacin, Allah kadai yasan iyaka adadin kewar ta da yayi. Shi kan shi yau sai da yayi Kokari ya iya sauka daga kan gadon shi, gidan da Babu Nafeesah! Teburin cin abincin da babu Nafeesah!! Rayuwar da babu Nafeesah!!! Abinda yayi ta jinjinawa a cikin ranshi kenan yana tunanin ko zai iya surviving a haka?! A hankali ya bude idanunshi tare da gyara zaman shi, hannunshi ya dora akan system din dake gabanshi ya cigaba da typing din da yake yi kafin Nafeesah ta kira shi ya fada cikin shaukin ta.
Kofar dakin shi yaji an turo, an shigo, tare da maida kofar aka rufe. Da mamaki ya daga idanunshi da suka gama rinewa da shaukin Nafeesah ya kalli Mubeenah dake tunkaro shi. Shi a karan kanshi ba zai iya tuna Lokaci na karshe daya ganta a tsakiyar dakin shi ba, ya jijjiga cikin wani irin takaici na babu gaira babu dalili daya ziyarce shi she has ruined it! She just ruined dan guntun farincikin daya mamaye zuciyar shi for a while. Kallo ya bita dashi har ta zauna a gefen gadon shi, sanye take da doguwar rigar barci har kasa, jelar kitson kanta da aka mata fiye da watanni biyu da suka wuce (lol) ya fito ta cikin hular data saka a kanta ya zubo har kan kafadunta. Kan shi ya dauke ya maida ga rubutun da yake yi, ya kwashe kyawawan mintuna arba'in kafin ya gama. Ya kashe system din tare da tashi ya fada bayi, brush yayi tare da dauro alwala kamar yadda yake a Al'adar rayuwar shi. Ya fito ya tsaya a gaban mirror, turare mai sanyin kamshi ya fesa a gabban jikinshi ya koma kan gado daga can daya gefen da Mubeenah take a zaune har lokacin, light off yayi ya kwanta. Mubeenah data gama kuluwa da abinda yayi, tace "haba Ibrahim wannan wane irin rashin mutunci ne kana gani na zaka yi wani banza dani ka maida ni kamar wata invisible human being?" ya kalli sashen da take duk da baya ganinta saboda duhun da dakin yayi, yace "au! Ai ban yi zaton cewa kina da abun cewa bane, na sani ko zuwa kika yi kawai kiga yadda dakina yake duba da yadda kika share watanni ba tare da kin leko ba?" ta dan ja siririn tsaki, " amma dai kasan cewa bana zuwa dakin ka haka nan koh?" ya gyada kanshi a hankali, a zuciyar shi yace 'right! Bana ganin ki a dakina sai idan kina bukatar either kudina ko jikina!' yayin da wani irin bakin ciki da takaici ya mamaye zuciyar shi. Tashi zaune yayi tare da kunna wutar dakin ya juya yana kallonta, "What do you want then?" ta dan yamutsa fuska "ina bukatar kudi ne!" ya kalleta sosai, "kudi kuma? Har nawa?" tace "one hundred and fifty k" ya gyara zaman da yayi sosai "n why would I?" ta wani hade fuska, "it's for you Ibrahim! Material ne zan saya da jewelries na zuwa bikin bude kamfanin ka kaga kuwa it's worth it" shi gabadaya ya ma kasa magana, kallonta kawai yake yi har ta dire maganar ta. Yace "duka duka yaushe kika amshi 50k a wajena Mubeenah? Wai saboda meye na bude miki saloon? Ina ce dama saboda idan bukatu irin haka sun taso kiyi amfani dasu ba tare da kin tambaye ni ba ne?" ta wani lankwashe murya Ita ala dole kissa tace "kasan cinikin saloon din ne kwana biyu sai a hankali babu customers shi yasa, yanzu haka bani da ko sisi a account dina" ya girgiza kai kawai, Mubeenah! Bai san wace irin mata ce Ita ba, Kwatakwata bata da damuwar yanayin da mutum yake ciki ko zai shiga, Ita dai kawai a bata abinda take so sai a samu zaman lafiya. Yace "Mubeenah! Baki ganin halin da ake ciki ne yanzu? Dinkin dubu dari a wannan zamanin Mubeenah ki duba mana, ina laifin hamsin?" hararar shi tayi a kaikaice tana mai turo baki, "kaga ni fa ba cewa nayi ka zauna kana bani labarai ba. Kudi, zaka bani ko A'ah?!" Murmushi yayi a sanyaye yace "zan baki mana uwargida sarautar mata..... Amma zo kiji kafin nan..." ya janyo ta zuwa jikinshi, cikin sauri ta zame, ya bita da kallo mai dauke da alamun tambaya. Fir taki amincewa dashi sai da tayi tsayin daka taga a take ya tura mata kudin cikin account dinta sannan ta amince. Shima haka nan ta tsaya abinta shi kadai yake kidan shi da rawar shi tana kwance male-male kamar ruwa. Ba a jima ba ya mirgina daya gefen gadon yayi ruf da ciki idanunshi a lumshe, duk dokin da yake yi sai yaji ya kau daga ranshi saboda yadda tayi kamar bata jindadin kasancewa dashi, he means ta ya za ayi ace mace ana having s*x da Ita amma Ita ko a jikinta, karewa ma Allah-Allah take yi ya sauka daga kanta, does it make sense? (Qalubale a gare ku mata, akwai ire-iren ku kuna nan libge cikin lungu da sako na wannan duniyar, a gyara dan Allah!). Bayan nan Kwatakwata baya jin dadin kasancewa da Ita shima, koda yake abu ne daya riga ya saba dashi. Yana tunanin tun wajen haihuwar Hafsat Mubeenah ta karu kuma bata maida hankali wajen ganin cewa an dinke ta ba, ko don bata damu dashi bane? To shi dai tun daga nan ya daina fahimtar Mubeenah, haka nan yake maleji dai ko don raya Sunnah da kuma kare kai daga dattin Zinah to yanzu abun dai ya fara wuce misali. Yana jin lokacin data tashi ta zura kayan jikinta ta fita daga dakin, bata damu da yadda miji ya juya mata baya suna tsakiyar auratayya ba, bata damu taji dalilin daya saka shi aikata haka ba balle tayi tunanin gyara, Ita dai kawai tunda ta samu abinda take muradi to an wuce wajen. Da kyar ya tashi ya fada toilet yayi wanka da ruwa mai sanyi, babu abinda ta6a Mubeenah ya jayo mishi sai kara hargitsa mishi tunani da kwalwa da yayi. Ya fito ya canza kayan barcin shi kafin ya kwanta, zuciyar shi cike da tunanika barkatai, mafi yawa daga cikin su shine 'He had to make Nafeesah his ASAP, kafin wani ya riga shi ya shiga uku'.
Chapter 30 · 0% Book details