← Book details Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 88

Sashe 46

Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 5 min read

Ban maidawa Abbu reply dinshi ba, amma tun kafin karfe tara ta cika na samu waje na zauna ina jiran shigowar kiran Abbu. Kamar yadda yace, karfe tara tana cika kiran shi ya shigo wayata. Na daga wayar tare da mishi sallama ya amsa, a nutse na gaida shi nan ma ya amsa tare da tambayar karatuna, ya dan ja ni da hira kadan kafin ya dulmiya cikin maganar data saka shi kira na. "Nafeesah ranar nan muna waya na katse sai kuma ban sake kira ba, na kara miki lokaci ne wanda zaki yi tunani a nutse don a tunani na a wancan lokacin baki zauna kinyi tunani bane shi yasa. Ina fata in ji different amsa daga gare ki wannan karon". Nayi shiru ina tunani, wata marubuciyata tace wai 'Opportunity comes once (Dama tana zuwa ne sau daya -Takori)' ni kam yau dai ina so inyi wasa da tawa damar. Masu karatu kar kuga laifina. I am a girl in her twenties, a irin wannan age din babban abinda 'ya Mace take bukata daga kowane namiji shine kalmar so, sai dai ni yana proposing din aurena ne kawai ba tare da nasan ainihin abinda yake cikin ran shi ba. In amince da auren shi ince nayi auren me? I can't risk my happiness akan son zuciya irin nawa. Nayi gyaran murya a nutse nace "kayi hakuri Abbu, ina kan bakana har yanzu" ina dire aya ya tare ni, "why?" nayi shiru, yace "me yasa baki son Aurena ne?" nace "it's obvious, saboda kai baban Hafsy dasu Abdullahi ne, kai Mijin Aunty Mubeenah ne, you are Niimah's brother, Abby you Are My Father's Friend.... How are you expecting me to accept your offer?" yace "just because of that?" na gyada kai kamar yana gani na, "yace but is it a sin? Abubuwan nan da kika lissafo dukan su ba wasu obstacles bane da zasu hana ni auren ki Nafeesah! Just tell me ba kya so na shi yasa ba zaki iya aure na ba" nayi shiru zuciyana tana bugawa, ina zan Iya furta wadannan maganganu? Yace "tell me Nafeesah!" cikin husky voice nashi wanda ya fara gauraya da bacin rai, nan ma shiru kawai nayi, zan iya karya akan komi amma banda karyar kin Abbu, ba zan iya ba. "Goddammit Nafeesah! Me kike son nayi for goodness sake?!" wannan Karon bacin ranshi ya fito baro-baro, ya cigaba "kina bukatar ki ganni akan gwiwa na ina rokon ki akan ki aure ni? Ko kuma so kike yi in dinga binki sahu-sahu kamar yaro ina shelantawa duniya ina son in aure ki sannan zaki yarda?" na danyi chuckling a hankali, that is so childish. Yayi shiru kafin inji ya fara magana wannan karon a hankali kuma very calm, "ok, ok. Maganar su Hafsy da kike yi Nafeesah ina tabbatar miki they will be more than happy idan suka ji cewa zaki auri baban su saboda suna Son ki Nafeesah, sun dauke ki da muhimmanci sosai fiye da tunaninki, haka ma su Ni'imah, Dad dinki kuwa has already given us his Blessings. M just trying to be a nice guy anan kin gane? Bana so ne a miki abinda ba kya so ne kawai shi yasa, Mubeenah kuma wannan ba damuwar ki bace, ba lallai sai da blessings dinta ne zamu yi aure ba, Are we good now?" nace "still Abbu....." ya katse ni, "kina da wanda kike so ne?" nayi shiru ban amsa ba, jin shirun da nayi yasa ya sha jinin jikin shi, "akwai kenan koh?" nan ma nayi shiru, yayi kwafa "just wait till I come back. I will not let you go that easily Nafeesah, Aure a tsakanin mu kamar an daura ne Nafeesah coz you are mine! Saboda ni aka halicce ki ba dan wani ba. Zan baki sauran watanni biyu da suka rage min anan don ki tsara yadda Rayuwar ki a gidana zata kasance. Ina dawowa daurin auren mu ba xai dauki lokaci ba Nafeesah in shaa Allah.... Bari in barki haka, sai da safe" da kyar na iya daga baki nace "A tashi lafiya" kusan a lokaci daya muka katse wayar dashi. Na kai hannuwana duka biyun na tallabo kumatuna dasu, Abbu da gaske yake. Wani bangare na zuciyata yana murna da hakan yayin da wani sashen yake jimami da tantama, tantama akan in amince ko inyi akasin haka? Jimami kuma na ya makomar rayuwata zata kasance idan na amince din???

Daga wannan ranar kusan kullum sai mun yi waya da Abbu, yawancin lokuta zai kira ya tambaye ni karatuna da sauran su, bai sake tada min zancen auren ba, hakan shi yake kara jefa zuciyata cikin wasi-wasi. I mean yadda nake ji ana fada ko kuwa dai mostly yadda ake yi a cikin film, a situation irin haka zaku ga Namiji ya shiririce a gefen mace going to the moon and black, proposing ta hanyoyi daban-daban, amma shi Abbu babu alamun haka a tattare dashi. Idan text ya turo min babu kalmar so ko daya da nake tsinta a ciki haka ma idan muka yi waya dashi, amma kulawa kam ina shan ta, kullum cikin tambayar lafiyata da Al'amuran rayuwata yake. Hakan shi yake kara jefa ni cikin tunani., Abbu Wane irin mutum ne shi kam??
#TeamAbbu

*♡Jeedderh♡*
[12/23/2017, 13:52] Beluvd Zee: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*

*©°•Jeedderh Lawals•°*

*37*
Chapter 46 · 0% Book details