Sashe 11
Ni Da Abokin Baba Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wannan weekend din ziyara nayi, naje gidan Anti Uwani na musu yini a can, daga nan ni da AbdulJalal muka shiga gari sai bayan isha'i ya sauke ni a gida bayan mun tsaya a Mcbae mun sayi tarkacen chocolates da ice cream. Washegari lahdi sai wajen karfe biyar na bar gida cike da kewar Mom da Dad, amma fa can kasan zuciyana wani farin ciki da doki ne dankare a cikinta, dokin in koma inci gaba da yiwa Abbu dadadan girki na yana ci yana yaba min har da santi. Sai dai koda na isa sai na tarar Hareera ta dawo daga biki, Abbu kuma baya gari, gwiwa na yayi sanyi sosai, jiki a sanyaye na shige daki na.
Washegari a tsaitsaye muka ci abinci muka wuce makaranta, ranar mun sha ayyuka a lab kamar me! A matukar gajiye muka zauna akan dakalin da muka saba zama ni da Ramlah cikin dan garden din da muke hutawa, na kalle ta ina dan murmushi, "ke jiya fa muka hadu da Muneer" bata nuna alamun abun ya dadata da kasa ba kamar yadda nayi zato, tayi fuskar shanu tace a ina? Nace "McBae, mun shiga siyayya ni da AbdulJalal. God! Baki ga yanda gayen nan ya kara kyau ba, yayi fari yayi kiba sosai, I think he misses me so much, kin kuwa ga irin fara'ar daya dinga min? Rabona da in....." tayi saurin katse ni, "ai fa kin kika fara bada labarin Muneer kamar wata radio mai jini ba kya ko son kiyi shiru, to sai ki tashi an zo daukar ki" na kalli inda suka saba tsayawa idan suka zo, gabana ya fadi sosai, Abbu ne yazo daukar mu! Ganin Qaseem ya fito yana tunkarar wajen da nake yasa na mike ina lalubar jakata nawa Ramlah sallama. A hankali kuma a sanyaye na bude bayan motar na shiga, "Abbu ina yini?" na furta cikin siririyar murya ta, ya amsa "lafiya qalau Nafeesah, ya kika baro Kaduna?" na amsa da lafiya lau. Yaja motar muka tafi babu mai furta uffan. Hafsat ce ta ciro drawing book dinta daga cikin school bag dinta tana nuna min Assignment din dana taya ta jiya akan zanen gidaje da motoci, tace "Kuma Uncle Jamilu yace ni na cinye 20 over 20 duk cikin class din" na shafa kanta ina murmushi, "Ohh that's very good princess, am proud of you" tayi dariya tana kwantowa a jikina na rungume ta. Muna isa gida sallah muka yi, na bude fridge na ciro fura da nono dana kawo daga gida, musamman Mommy ta bada aka yi, na zauna na dama ta da dan kaurinta na saka kankara da dan sugar, cups na dauko na zuzzubawa su Abdullahi. Muna zaune a falo muna sha kafin lokacin zuwa Islamiyar su yayi. Abbu ya fito daga daki hannunshi dauke da jakar laptop dinshi, dan karamin coffee table din dake gefen mu ya janyo ya dora laptop din nashi akai, kasa kasa yake kallon mu har ya zauna. Ya kalli kofin dake hannuna yace meye wannan kuke sha haka babu tayi? A kunyace nace fura ce! Idanunshi suka dan ware cikin mamaki, "wow, daga ina muka samu fura?" Hafsat tayi caraf tace "daga gidansu tazo da ita jiya!" ya jima sosai idanunshi suna kaina ban san ko tunanin me yake yi ba, ya kauda kanshi ya maida shi ga laptop dinshi, "tunda ba a mana tayi ba ni zan yiwa kaina, a bani idan da akwai" da sauri na tashi naje na dama mishi na kawo na ajiye mai a gefenshi. Su Hafsy suna wucewa makaranta na koma dakina na zauna ina kallo.
Tara da rabi ta nuna lokacin dana kalli agogo, nayi mika ina hamma ina jin kasusuwan jikina na amsawa saboda gajiya, ban kai ga kwanciyar da nayi niyar yi ba na jiyo kamar muryar Abbu a falo yana kwala min kira. Na saurara sosai har zuwa lokacin dana sake jin wani kiran kafin na warci hijabi na zura na fita, yana kan dinning a zaune yana kokarin rufe daya daga cikin food flasks din da aka ajiye akai, ya kalleni fuskar shi dauke da wani irin expression dana rasa ko wani iri ne; na jin haushi ne, embarrassment ne ko fusata? Shi dai ya bar wa kanshi sani. Na dan duka a gefenshi nace Abbu gani a sanyaye. Sai da yayi gyaran murya sannan yace "Please samo min noodles ko simple abu da zan ci, am quite hungry" na danyi jim kamar ba zan tashi ba suna da er aiki, yana da matar shi, ba za a ga laifi na ba idan na tashi na fada kicin na dafa mishi abinci? Koda yake ban ga laifin shi ba, abincin da Hareera tayi yau yadda kasan faten shinkafa saboda yadda shinkafar ta cafke, ita kanta Anty Mubeenah sai data mata fada yau dai har da ce mata idan ba zata gyara ba to lallai tana gab da barin gidan don ita ta gaji haka nan.... Abbu ya dan sake gyara murya ya kalle ni, "well??" nayi saurin dawowa cikin hankali na, "umh.... Dama zan ce ne noodles din kadai ta isa?" ya gyada kai, da sauri na tashi na wuce kicin cikin hardewar kafafu, zuciyana na gaya min cewa idanunshi shi a kaina suke. Tukunya na dora akan gas na hada duk abubuwan da nake bukata, ruwan yana tafasa na zuba indomie a ciki na kara da sardines, na dora ruwa a cikin kettle na zuba danyar citta da kanumfari er garlic don naga alamun kamar mura tana dan damun shi. Ina sauke indomie din na soya kwai na dora a sama, na juye shayin a cikin flask na dora duka kayan akan tray mai fadi na fita. Yanzu ya dawo tsakiyar falon ya zauna hannunshi rike da waya yana karatun labarai, na ajiye su a gefenshi na tura indomie din gaban shi da fork a ciki, na dauki kofi na tsiyaya shayin na mika mishi, shayin ya fara kaiwa bakin shi, ya dan yamutse fuska yana kallon shayin jin kamshin tafarnuwa na tashi, da sauri nace "umh... Naga kamar kana mura ne shine....." na kasa karasawa saboda kalmomin sun kare min kuma sai ya girgiza kai kawai ya fara kurbar shayin a hankali. Naje na dauko mishi ruwa da lemu irin wanda naga yana sha masu rangwamen sanyi a cikin fridge na kai na ajiye a gefenshi, "Abbu kana bukatar wani abu kuma?" ya girgiza kanshi, "babu Nafeesah, nagode. Sai da safe koh?" na tashi da sauri na bace a wajen. Duk zaman da nayi jina na dinga yi kamar akan kaya, zuciyana wani irin duka take kamar zata tsaga kirjina ta fito, ban san me yasa Abbu yake da wani irin effect a kaina na saka ni cikin rashin natsuwa ba.
Washegari ba laifi anyi abinci mai sense don mun zauna mun ci sosai, Abbu ya kalle ni yana ajiye spoon din hannunshi, "Nafeesah ko zaki iya dora min shayi irin na jiya?" a hankali na saci kallon Inda Anty take zaune, abincin ta take ci Hankalinta kwance kamar bata san Allah yayi ruwan tsirar mu a wajen ba. Na dan jijjiga kai na tashi, cikin mintunan da basu gaza bakwai ba na gama na juye a cikin flask, na hada da cup na fito falon. A gaban shi na ajiye su, ya kalle ni yana furta thanks! Kafin ya kalli su Hafsy, "oya a tashi a tafi koh? Malam Bala yazo" duk suka mike kowa yana daukar school bag din shi, muka musu sallama muka tafi.
Muna zaune da Ramlah a lab muna hira na kalleta, "babe ya za ayi ne? Ina bukatar wankin kai da kitso fa kaina yayi datti wallahi" tace ba damuwa, idan mun tashi sai mu biya ta saloon din Anty Haleemah, nima ranar Saturday naje aka wanke min" nace "to shikenan". Muna tashi kuwa Allah yasa su Malam Bala sun zo kenan, nace su wuce gida kawai ni Akwai inda zani. Muka je saloon aka wanke min kaina aka min kitso, da yake ba laifi Masha Allah ina da gashi sosai, Mommy irin bakaken fulanin nan ne, na gado zubi da kira irin tasu da kuma yalwar gashi, kalar fatar jikina kuma ta daddy ce, haka dangin shi suke wankan tarwada duk da cewa Akwai farare, kyawawan dara-daran idanu farare tas da bakaken eyelids, dogon dan siririn hanci kamar an zana da biro, dan karamin zagayayyen baki da jerarrun hakora kanana kuma farare tas da er siririyar wushirya a tsakiyar su. Muna gamawa da saloon gidan Anty Haleemah muka wuce, gidan flat ne dan madaidaici mai kyau dakalin ganshi kaga gidan mutum daya. Mijinta navy ne don haka bai cika zama a gidan ba, tare suke zaune da kanwar mijinta Khaleesat, mun dan saba da ita saboda a cikin BUK take karatu, tana yawan zuwa wajen Anti Haleemah din. Danta daya Mahmoud, nan muka wuni a gidan sai bayan Magriba ta hada ni da direba ya maida ni gida, kafin mu isa tuni an kira sallar isha'i. A bakin gate ya ajiye ni, na gaida maigadin gidan na wuce ciki. A hankali na tura kofar falon na shiga baki na dauke sallama, babu kowa a cikin falon. Na maida kofar na rufe na fara tafiya zuwa dakina, kamar daga sama naji maganar, "Where the heck have you been???". A gigice na juya, Abbu ne zaune akan kujera yana kallona kamar a fusace? Cikina ya bada sautin kululu.... It seems like m in trouble.
*♡Jeedderh♡*
[11/16, 01:44] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*12*
Washegari a tsaitsaye muka ci abinci muka wuce makaranta, ranar mun sha ayyuka a lab kamar me! A matukar gajiye muka zauna akan dakalin da muka saba zama ni da Ramlah cikin dan garden din da muke hutawa, na kalle ta ina dan murmushi, "ke jiya fa muka hadu da Muneer" bata nuna alamun abun ya dadata da kasa ba kamar yadda nayi zato, tayi fuskar shanu tace a ina? Nace "McBae, mun shiga siyayya ni da AbdulJalal. God! Baki ga yanda gayen nan ya kara kyau ba, yayi fari yayi kiba sosai, I think he misses me so much, kin kuwa ga irin fara'ar daya dinga min? Rabona da in....." tayi saurin katse ni, "ai fa kin kika fara bada labarin Muneer kamar wata radio mai jini ba kya ko son kiyi shiru, to sai ki tashi an zo daukar ki" na kalli inda suka saba tsayawa idan suka zo, gabana ya fadi sosai, Abbu ne yazo daukar mu! Ganin Qaseem ya fito yana tunkarar wajen da nake yasa na mike ina lalubar jakata nawa Ramlah sallama. A hankali kuma a sanyaye na bude bayan motar na shiga, "Abbu ina yini?" na furta cikin siririyar murya ta, ya amsa "lafiya qalau Nafeesah, ya kika baro Kaduna?" na amsa da lafiya lau. Yaja motar muka tafi babu mai furta uffan. Hafsat ce ta ciro drawing book dinta daga cikin school bag dinta tana nuna min Assignment din dana taya ta jiya akan zanen gidaje da motoci, tace "Kuma Uncle Jamilu yace ni na cinye 20 over 20 duk cikin class din" na shafa kanta ina murmushi, "Ohh that's very good princess, am proud of you" tayi dariya tana kwantowa a jikina na rungume ta. Muna isa gida sallah muka yi, na bude fridge na ciro fura da nono dana kawo daga gida, musamman Mommy ta bada aka yi, na zauna na dama ta da dan kaurinta na saka kankara da dan sugar, cups na dauko na zuzzubawa su Abdullahi. Muna zaune a falo muna sha kafin lokacin zuwa Islamiyar su yayi. Abbu ya fito daga daki hannunshi dauke da jakar laptop dinshi, dan karamin coffee table din dake gefen mu ya janyo ya dora laptop din nashi akai, kasa kasa yake kallon mu har ya zauna. Ya kalli kofin dake hannuna yace meye wannan kuke sha haka babu tayi? A kunyace nace fura ce! Idanunshi suka dan ware cikin mamaki, "wow, daga ina muka samu fura?" Hafsat tayi caraf tace "daga gidansu tazo da ita jiya!" ya jima sosai idanunshi suna kaina ban san ko tunanin me yake yi ba, ya kauda kanshi ya maida shi ga laptop dinshi, "tunda ba a mana tayi ba ni zan yiwa kaina, a bani idan da akwai" da sauri na tashi naje na dama mishi na kawo na ajiye mai a gefenshi. Su Hafsy suna wucewa makaranta na koma dakina na zauna ina kallo.
Tara da rabi ta nuna lokacin dana kalli agogo, nayi mika ina hamma ina jin kasusuwan jikina na amsawa saboda gajiya, ban kai ga kwanciyar da nayi niyar yi ba na jiyo kamar muryar Abbu a falo yana kwala min kira. Na saurara sosai har zuwa lokacin dana sake jin wani kiran kafin na warci hijabi na zura na fita, yana kan dinning a zaune yana kokarin rufe daya daga cikin food flasks din da aka ajiye akai, ya kalleni fuskar shi dauke da wani irin expression dana rasa ko wani iri ne; na jin haushi ne, embarrassment ne ko fusata? Shi dai ya bar wa kanshi sani. Na dan duka a gefenshi nace Abbu gani a sanyaye. Sai da yayi gyaran murya sannan yace "Please samo min noodles ko simple abu da zan ci, am quite hungry" na danyi jim kamar ba zan tashi ba suna da er aiki, yana da matar shi, ba za a ga laifi na ba idan na tashi na fada kicin na dafa mishi abinci? Koda yake ban ga laifin shi ba, abincin da Hareera tayi yau yadda kasan faten shinkafa saboda yadda shinkafar ta cafke, ita kanta Anty Mubeenah sai data mata fada yau dai har da ce mata idan ba zata gyara ba to lallai tana gab da barin gidan don ita ta gaji haka nan.... Abbu ya dan sake gyara murya ya kalle ni, "well??" nayi saurin dawowa cikin hankali na, "umh.... Dama zan ce ne noodles din kadai ta isa?" ya gyada kai, da sauri na tashi na wuce kicin cikin hardewar kafafu, zuciyana na gaya min cewa idanunshi shi a kaina suke. Tukunya na dora akan gas na hada duk abubuwan da nake bukata, ruwan yana tafasa na zuba indomie a ciki na kara da sardines, na dora ruwa a cikin kettle na zuba danyar citta da kanumfari er garlic don naga alamun kamar mura tana dan damun shi. Ina sauke indomie din na soya kwai na dora a sama, na juye shayin a cikin flask na dora duka kayan akan tray mai fadi na fita. Yanzu ya dawo tsakiyar falon ya zauna hannunshi rike da waya yana karatun labarai, na ajiye su a gefenshi na tura indomie din gaban shi da fork a ciki, na dauki kofi na tsiyaya shayin na mika mishi, shayin ya fara kaiwa bakin shi, ya dan yamutse fuska yana kallon shayin jin kamshin tafarnuwa na tashi, da sauri nace "umh... Naga kamar kana mura ne shine....." na kasa karasawa saboda kalmomin sun kare min kuma sai ya girgiza kai kawai ya fara kurbar shayin a hankali. Naje na dauko mishi ruwa da lemu irin wanda naga yana sha masu rangwamen sanyi a cikin fridge na kai na ajiye a gefenshi, "Abbu kana bukatar wani abu kuma?" ya girgiza kanshi, "babu Nafeesah, nagode. Sai da safe koh?" na tashi da sauri na bace a wajen. Duk zaman da nayi jina na dinga yi kamar akan kaya, zuciyana wani irin duka take kamar zata tsaga kirjina ta fito, ban san me yasa Abbu yake da wani irin effect a kaina na saka ni cikin rashin natsuwa ba.
Washegari ba laifi anyi abinci mai sense don mun zauna mun ci sosai, Abbu ya kalle ni yana ajiye spoon din hannunshi, "Nafeesah ko zaki iya dora min shayi irin na jiya?" a hankali na saci kallon Inda Anty take zaune, abincin ta take ci Hankalinta kwance kamar bata san Allah yayi ruwan tsirar mu a wajen ba. Na dan jijjiga kai na tashi, cikin mintunan da basu gaza bakwai ba na gama na juye a cikin flask, na hada da cup na fito falon. A gaban shi na ajiye su, ya kalle ni yana furta thanks! Kafin ya kalli su Hafsy, "oya a tashi a tafi koh? Malam Bala yazo" duk suka mike kowa yana daukar school bag din shi, muka musu sallama muka tafi.
Muna zaune da Ramlah a lab muna hira na kalleta, "babe ya za ayi ne? Ina bukatar wankin kai da kitso fa kaina yayi datti wallahi" tace ba damuwa, idan mun tashi sai mu biya ta saloon din Anty Haleemah, nima ranar Saturday naje aka wanke min" nace "to shikenan". Muna tashi kuwa Allah yasa su Malam Bala sun zo kenan, nace su wuce gida kawai ni Akwai inda zani. Muka je saloon aka wanke min kaina aka min kitso, da yake ba laifi Masha Allah ina da gashi sosai, Mommy irin bakaken fulanin nan ne, na gado zubi da kira irin tasu da kuma yalwar gashi, kalar fatar jikina kuma ta daddy ce, haka dangin shi suke wankan tarwada duk da cewa Akwai farare, kyawawan dara-daran idanu farare tas da bakaken eyelids, dogon dan siririn hanci kamar an zana da biro, dan karamin zagayayyen baki da jerarrun hakora kanana kuma farare tas da er siririyar wushirya a tsakiyar su. Muna gamawa da saloon gidan Anty Haleemah muka wuce, gidan flat ne dan madaidaici mai kyau dakalin ganshi kaga gidan mutum daya. Mijinta navy ne don haka bai cika zama a gidan ba, tare suke zaune da kanwar mijinta Khaleesat, mun dan saba da ita saboda a cikin BUK take karatu, tana yawan zuwa wajen Anti Haleemah din. Danta daya Mahmoud, nan muka wuni a gidan sai bayan Magriba ta hada ni da direba ya maida ni gida, kafin mu isa tuni an kira sallar isha'i. A bakin gate ya ajiye ni, na gaida maigadin gidan na wuce ciki. A hankali na tura kofar falon na shiga baki na dauke sallama, babu kowa a cikin falon. Na maida kofar na rufe na fara tafiya zuwa dakina, kamar daga sama naji maganar, "Where the heck have you been???". A gigice na juya, Abbu ne zaune akan kujera yana kallona kamar a fusace? Cikina ya bada sautin kululu.... It seems like m in trouble.
*♡Jeedderh♡*
[11/16, 01:44] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*12*