Sashe 7
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsabar rufewar da idon Safiyya yayi Sam Bata San da shigowar Naseer da jikinsa ya kwashi wani irin rawa ba Hajara kanta sai data tsorata da yanda ya shigo da balain sauri ta mik'e tana k'ok'arin yiwa Safiyya magana Naseer ya isa wajensu ya kaiwa Safiyya wani irin wawura ya hadata da bango ya shaketa Ta fara kakarin mutuwa.
Hajara kuwa ihu ta saka Dan dagaske Naseer so yake ya kashe Safiyya fata kawai yake ta mutu a hannunsa a Kai shi gidan yari ya huta da bakin cikin Safiyya da Mahaifiyarsa.
Duk dukan da Hajara take kaiwa Naseer Sam baiji ba har muciya sai daya karye a jikinsa Bai cikata ba
Safiyya kuwa tuni ta sume a hannunsa.
Hajara sai waje tayi da gudu ta Kira aka zo aka bambara Safiyya daga hannun Naseer.
Hajara tayi Kan Safiyya tana ihun Naseer ya kashe Mata ya.
Naseer kuwa d'akin ha Shiga ya hau watso da kayan Safiyya waje Yana ta bar Masa gidansa bazata Kara kwanar Masa a gida ba.
A ranar ba karamin rikici akayi tsakanin Hajara da Naseer ba
Dan da Safiyya ta farfado sai da Naseer ya fitar da ita waje Akan bazata Kara kwanan Masa a gida ba
Hajara kuwa ta dage akan sai dai ya koresu su biyun K'arfi da Yaji Hajara ta Masa fin karfin ita mahaifiyarsa ce ta kulle Safiyya a daki Akan ba Inda zata je ai ba Haka kawai Safiyya ta daki zahiran ba rashin kunya tayi Mata.
A ranar Naseer kwana yyi Yana kuka daga tafiya Naeema da zaa auna jininsa zaa iya ganin ya mugun Hawa sabida tashin hankali shi kam yasan rayuwar Zahira na cikin hatsari Bai tab'a ganin uwar da Bata San danta bata San jikokinta ba sai Mahaifiyarsa ya yarda uwa na iya tsanar matar danta Bai San uwa na tsanar danta ta tsani zaman lafiyarsa ba.
Ya Zama Dole ya d'auki mataki inama Naeema ta tafi da Zahira da Nadeeya ta bar mishi sauran yaran bazai dauwama Yana zaman gida ba Dole wani uzurin ya taso yyi nesa da gida Amma in ya fita yasan yana ckin fargaba da rashin kwanciyar hankali.
A takaice tundaga ranar Safiyya ta fara balain tsoron Naseer indai Yana Nan ko fitowa Bata iya Yi gashi baya fita sai dai idan Massallaci zaije.
Akan engine markaden ma sai da sukayi rikici da Hajara ta dage sai dai ya bar Mata guda daya ya dau daya idan aka kawo.markade ita ta d'au daya shi ya dau daya sai dai me tunda aka siyo engine sau biyu aka kawo markade baa Kara kawowa ba Sabida masifar Hajara har suna Suka saka Mata a unguwar suna kiranta da masifafiyar tsohuwa.
Naseer yanda ya d'auka zai samu kudi idan ya siyi engine markaden lura da yanda Naeema ke samun kudi Bai samu ba Dan bama zuwa ake ba wani zubin yana ma zaune a k'ofar gida zaa wuce gidansa a Kai wajen bakin titi da dai a Zo gidansa tuni damuwa tayi.masa yawa kasa da wata daya komai na gidan ya Kare Wanda sai da ta Kai shi da siyar da engine guda daya Dan Bai shigo Masa da kudin ba.
A cikin kudin ya biya kudin makarantar su Zahira sauran canjin shima Nan da Nan ya Kare.
Kafin kace me dayan ma sai daya siyar.
Hajara kuwa masifa ta hau yi akan ita tasan Naeema ce tayi asiri aka ki kawo musu markade k'arfi da yaji tana ji tana gani Naseer ya siyar da engine data ci burin samun kudi dashi ta siyi filaye.
Kamar ta fashe dan bakin ciki wata uku da tafiyar Naeema sai gashi abinda zasu saka a cikinsu Yana neman gaggararsu.
Safiyya kuwa data ga bazata iya ba aikatau taje ta nema a wani gidan masu kudi zata ringa zuwa tana dawowa daddare.
Idan taje abincin da ake Bata shi take kawowa gida taci Hajara na kallo idan tayi Magana kuwa Sai tace Mata kowa tasa ta fishe shi
Naseer kuwa Dan abinda ya fita ya Dan samo sabida tuni ya nemi aikin lebura na gini ya farayi Dan kudin daya samu yake siyowa su Zahira abinda zasuci ahaka ma sai dai shi ya hakura Dan bazai iya barin Hajara da yunwa ba.
Ahaka Safiyya tayi albashi Hajara tayi ta rokon ta Allah da annabi kafin ta yarda ta Bata wani Abun.
Tana Bata kuwa ta siyo shinkafa da kayan Miya ta girka ta kakasafta a kwanu.
Zahira na dawowa daga makaranta tasa ta cire uniform ta Dora Mata farantin
Ta bawa Nadeeya Yar robar miyan tace musu su dau hanya su tafi su siyar Mata taja musu kunne akan kar su sake su dawo gida batare da sun siyar Mata ba idan Naseer ya Isa idan ya dawo ya mata magana yaga yanda zata Yi dashi
Suna fita ta dakawa Minal tsawa Akan su saka kayan islamiyya su tafi.
Minal sai data Dan gwada Mata taurin Kai ta dan bubuge ta kafin suka bar gidan.
Naseer dake ta Dora bullo a wani gida da ake ginawa kamar ance ya daga kansa ya hango Zahira da Nadeeya na tafe a Gefen titi suna rarrabewa a gefe ga uban faranti akan Zahira ga Nadeeya itama da nata robar miyar.
Naseer Bai San sanda ya duro Yana mirtsika Ido ba Dan ya tabbata da su Zahira yake gani.
Jiki na rawa ya Isa wajensu.
Ya sauke farantin dayake ganin yayi wa Zahira nauyi yace musu waye ya Dora musu talla.
Ce Masa sukayi Hajara ce.
Yayi shiru Ransa na balain baci.
Dak'yar ya hadiye b'acin Ransa yace su zauna a wani dakali su jira shi Yana zuwa.
Ba a cikin hankalinsa Suka karasa aikin ba Dan har sai da bulo ya Fado Masa a kafa Sabida tunani.
Ana biyansa kudinsa ya wanke jikinsa ya cire kayan aikinsa ya maida Mai kyau jikinsa.
Ya tsallaka wajen su Zahira ya d'auki farantin abincin.
Ya rarrabawa almajirai
Ya Kama hannunsu ya tare musu bus Suka hau suka nufi gwammaja.
Bashida tabbacin Gane gidan Tijjani Amma ahaka yaje sai da kyar ya Gane gidan da kwantance.
Suna zuwa k'ofar Gidan Tijjani na isowa a vespa.
Ko parking baiyi sosai ba ya duro daga vespan Dan murna ya rungume Naseer cikin murna
Naeema
Kwana biyu kawai nayi a garinmu danaje da Ashe sun Dade suna nemana sosai naji mutuwar Mai unguwa da nake Jinsa tamkar mahaifina ashe shekara daya kenan da rasuwarsa
Kafin rasuwarsa ya siyar da gidanmu ya boyemin kudin Dan lokacin sosai ake San siyan gidan hayan daya saka kuwa sai yaga ma.kamar mutanen ciki Bata gidan suke hakane yasa ya siyar da gidan Akan duk lokacin da Nazo zai bani ya kuma San bazanji Haushin siyarmin da gidan mu da yayi ba
Dubu dari uku da sabain ya siyar da gidan namu.
Kafin rasuwarsa Haka yayi ta rokan yayansa da matansa akan Dan Allah Kar su tabamin kudina duk lokacin Dana Zo a damka min kudina.
Sosai naci kuka na Godewa Allah da rashin Mai unguwa a Haka na kwana biyu cikin zuciyata ba dadi uwa uba ga tunanin yarana daya dameni ko baccin kirki bana iya yi sabida Ina tunanin kamar suna can suna Shan duka a wajen Safiyya abinda zai taimakeni kawai shine Kila Naseer bazai yarda a tab'a min su ba da Wanan tunanin hankalina ke Dan kwanciya.
Sosai iyalin Mai unguwa suka nunamin soyaya Dana tashi dawowa Dan Kaya Suka bani sosai na amfani Dan ban Gaya musu abinda ke faruwa Dani ba.
Karfe uku na rana na iso gidan kanwar Aunty Ina zuwa kuwa na tada Aunty a gidan.
Bazan manta Aunty a rayuwata ba tamin abunda har na mutu bazan manta alherinta a gareni ba.
Ina sallahr La'asar muka nufi dorayi da ita.
Ta kaini gidan data kama min ta hau min bayanin da kyar Mai gidan ya yarda ya bada haya Dan yace siyarwa zaiyi Amma ko yanzu ya samu Mai siya zai maidamin kudina ne na siyar.
Gidan Mai kyau ne dakuna biyu da bandaki biyu da Palo sai dan karamin shago a k'ofar gida
Gwada tambayarta nayi nawa ne gidan.
Tacemin Dubu dari uku da ashirin
Take nace Mata Zan siyi gidan Kamar Wasa ta rakani wajen Mai gidan na nemi ya siyarmin Dubu dari biyu da hamsin dak'yar ya siyar min a Dubu dari biyu da casain
Washegari muka Kai Masa kudin gidan ya d'auko takarda gidan ya bani
Aunty sai murna takemin ni kuwa sai tambayarta nake tana ganin yarana cemin tayi tana ganinsu kar na damu Naseer na kula dasu Dan ta saka Ido a kansu
Take naji hankalina ya Dan kwanta.
A. Cikin kwana uku naja wutan.nepa gidan
Aunty ta Nemo min Katifa second hand na biya da Dan ledar tsakar daki da Dan kayan amfanin gida da bazaa rasa ba.
Wata Hassana da take bazawara da ta kasance Yar uwarsu ta kawomin Akan mu ringa kwana tare Dan Ina tsoron kwana Ni kadai.
Hassana kuwa zata iya girme min Amma tana da kirki
Makotana na zaga na Dan duba abinda baa samu unguwar Naga har da dai markaden sai sunyi tafiya Mai nisa suke samu.
Ana Kuma neman ruwan Sanyi kayan provision ma sai sun Yi tafiya Mai nisa.
Take kuwa na nemi engine second hand na siya Dan gaskiya Ina San sanaar markaden dan ya shigomin da kudi
Cikin Ikon Allah kuwa sati daya da siya aka faramin layi.
Dan har Hassana Tayani takeyi idan na gaji.
Kamar Wasa sauran kudin hannuna na Nemo kafinta ya bubbuga min canter na Dan zuba provision din kad'an su Maggi biscuit bredi da alewa da littattafai makaranta Dan Naga Ana yawan nema
Shima sati da fara siyar da provision din Rabbi ya Sanya min albarka a hankali sai gashi shagon k'ofar gida ya cika da kaya.
Sai gashi a cikin wata biyu har freezer na siya shima na saka a shagon Ina siyar da ruwa.
Hajara kuwa ihu ta saka Dan dagaske Naseer so yake ya kashe Safiyya fata kawai yake ta mutu a hannunsa a Kai shi gidan yari ya huta da bakin cikin Safiyya da Mahaifiyarsa.
Duk dukan da Hajara take kaiwa Naseer Sam baiji ba har muciya sai daya karye a jikinsa Bai cikata ba
Safiyya kuwa tuni ta sume a hannunsa.
Hajara sai waje tayi da gudu ta Kira aka zo aka bambara Safiyya daga hannun Naseer.
Hajara tayi Kan Safiyya tana ihun Naseer ya kashe Mata ya.
Naseer kuwa d'akin ha Shiga ya hau watso da kayan Safiyya waje Yana ta bar Masa gidansa bazata Kara kwanar Masa a gida ba.
A ranar ba karamin rikici akayi tsakanin Hajara da Naseer ba
Dan da Safiyya ta farfado sai da Naseer ya fitar da ita waje Akan bazata Kara kwanan Masa a gida ba
Hajara kuwa ta dage akan sai dai ya koresu su biyun K'arfi da Yaji Hajara ta Masa fin karfin ita mahaifiyarsa ce ta kulle Safiyya a daki Akan ba Inda zata je ai ba Haka kawai Safiyya ta daki zahiran ba rashin kunya tayi Mata.
A ranar Naseer kwana yyi Yana kuka daga tafiya Naeema da zaa auna jininsa zaa iya ganin ya mugun Hawa sabida tashin hankali shi kam yasan rayuwar Zahira na cikin hatsari Bai tab'a ganin uwar da Bata San danta bata San jikokinta ba sai Mahaifiyarsa ya yarda uwa na iya tsanar matar danta Bai San uwa na tsanar danta ta tsani zaman lafiyarsa ba.
Ya Zama Dole ya d'auki mataki inama Naeema ta tafi da Zahira da Nadeeya ta bar mishi sauran yaran bazai dauwama Yana zaman gida ba Dole wani uzurin ya taso yyi nesa da gida Amma in ya fita yasan yana ckin fargaba da rashin kwanciyar hankali.
A takaice tundaga ranar Safiyya ta fara balain tsoron Naseer indai Yana Nan ko fitowa Bata iya Yi gashi baya fita sai dai idan Massallaci zaije.
Akan engine markaden ma sai da sukayi rikici da Hajara ta dage sai dai ya bar Mata guda daya ya dau daya idan aka kawo.markade ita ta d'au daya shi ya dau daya sai dai me tunda aka siyo engine sau biyu aka kawo markade baa Kara kawowa ba Sabida masifar Hajara har suna Suka saka Mata a unguwar suna kiranta da masifafiyar tsohuwa.
Naseer yanda ya d'auka zai samu kudi idan ya siyi engine markaden lura da yanda Naeema ke samun kudi Bai samu ba Dan bama zuwa ake ba wani zubin yana ma zaune a k'ofar gida zaa wuce gidansa a Kai wajen bakin titi da dai a Zo gidansa tuni damuwa tayi.masa yawa kasa da wata daya komai na gidan ya Kare Wanda sai da ta Kai shi da siyar da engine guda daya Dan Bai shigo Masa da kudin ba.
A cikin kudin ya biya kudin makarantar su Zahira sauran canjin shima Nan da Nan ya Kare.
Kafin kace me dayan ma sai daya siyar.
Hajara kuwa masifa ta hau yi akan ita tasan Naeema ce tayi asiri aka ki kawo musu markade k'arfi da yaji tana ji tana gani Naseer ya siyar da engine data ci burin samun kudi dashi ta siyi filaye.
Kamar ta fashe dan bakin ciki wata uku da tafiyar Naeema sai gashi abinda zasu saka a cikinsu Yana neman gaggararsu.
Safiyya kuwa data ga bazata iya ba aikatau taje ta nema a wani gidan masu kudi zata ringa zuwa tana dawowa daddare.
Idan taje abincin da ake Bata shi take kawowa gida taci Hajara na kallo idan tayi Magana kuwa Sai tace Mata kowa tasa ta fishe shi
Naseer kuwa Dan abinda ya fita ya Dan samo sabida tuni ya nemi aikin lebura na gini ya farayi Dan kudin daya samu yake siyowa su Zahira abinda zasuci ahaka ma sai dai shi ya hakura Dan bazai iya barin Hajara da yunwa ba.
Ahaka Safiyya tayi albashi Hajara tayi ta rokon ta Allah da annabi kafin ta yarda ta Bata wani Abun.
Tana Bata kuwa ta siyo shinkafa da kayan Miya ta girka ta kakasafta a kwanu.
Zahira na dawowa daga makaranta tasa ta cire uniform ta Dora Mata farantin
Ta bawa Nadeeya Yar robar miyan tace musu su dau hanya su tafi su siyar Mata taja musu kunne akan kar su sake su dawo gida batare da sun siyar Mata ba idan Naseer ya Isa idan ya dawo ya mata magana yaga yanda zata Yi dashi
Suna fita ta dakawa Minal tsawa Akan su saka kayan islamiyya su tafi.
Minal sai data Dan gwada Mata taurin Kai ta dan bubuge ta kafin suka bar gidan.
Naseer dake ta Dora bullo a wani gida da ake ginawa kamar ance ya daga kansa ya hango Zahira da Nadeeya na tafe a Gefen titi suna rarrabewa a gefe ga uban faranti akan Zahira ga Nadeeya itama da nata robar miyar.
Naseer Bai San sanda ya duro Yana mirtsika Ido ba Dan ya tabbata da su Zahira yake gani.
Jiki na rawa ya Isa wajensu.
Ya sauke farantin dayake ganin yayi wa Zahira nauyi yace musu waye ya Dora musu talla.
Ce Masa sukayi Hajara ce.
Yayi shiru Ransa na balain baci.
Dak'yar ya hadiye b'acin Ransa yace su zauna a wani dakali su jira shi Yana zuwa.
Ba a cikin hankalinsa Suka karasa aikin ba Dan har sai da bulo ya Fado Masa a kafa Sabida tunani.
Ana biyansa kudinsa ya wanke jikinsa ya cire kayan aikinsa ya maida Mai kyau jikinsa.
Ya tsallaka wajen su Zahira ya d'auki farantin abincin.
Ya rarrabawa almajirai
Ya Kama hannunsu ya tare musu bus Suka hau suka nufi gwammaja.
Bashida tabbacin Gane gidan Tijjani Amma ahaka yaje sai da kyar ya Gane gidan da kwantance.
Suna zuwa k'ofar Gidan Tijjani na isowa a vespa.
Ko parking baiyi sosai ba ya duro daga vespan Dan murna ya rungume Naseer cikin murna
Naeema
Kwana biyu kawai nayi a garinmu danaje da Ashe sun Dade suna nemana sosai naji mutuwar Mai unguwa da nake Jinsa tamkar mahaifina ashe shekara daya kenan da rasuwarsa
Kafin rasuwarsa ya siyar da gidanmu ya boyemin kudin Dan lokacin sosai ake San siyan gidan hayan daya saka kuwa sai yaga ma.kamar mutanen ciki Bata gidan suke hakane yasa ya siyar da gidan Akan duk lokacin da Nazo zai bani ya kuma San bazanji Haushin siyarmin da gidan mu da yayi ba
Dubu dari uku da sabain ya siyar da gidan namu.
Kafin rasuwarsa Haka yayi ta rokan yayansa da matansa akan Dan Allah Kar su tabamin kudina duk lokacin Dana Zo a damka min kudina.
Sosai naci kuka na Godewa Allah da rashin Mai unguwa a Haka na kwana biyu cikin zuciyata ba dadi uwa uba ga tunanin yarana daya dameni ko baccin kirki bana iya yi sabida Ina tunanin kamar suna can suna Shan duka a wajen Safiyya abinda zai taimakeni kawai shine Kila Naseer bazai yarda a tab'a min su ba da Wanan tunanin hankalina ke Dan kwanciya.
Sosai iyalin Mai unguwa suka nunamin soyaya Dana tashi dawowa Dan Kaya Suka bani sosai na amfani Dan ban Gaya musu abinda ke faruwa Dani ba.
Karfe uku na rana na iso gidan kanwar Aunty Ina zuwa kuwa na tada Aunty a gidan.
Bazan manta Aunty a rayuwata ba tamin abunda har na mutu bazan manta alherinta a gareni ba.
Ina sallahr La'asar muka nufi dorayi da ita.
Ta kaini gidan data kama min ta hau min bayanin da kyar Mai gidan ya yarda ya bada haya Dan yace siyarwa zaiyi Amma ko yanzu ya samu Mai siya zai maidamin kudina ne na siyar.
Gidan Mai kyau ne dakuna biyu da bandaki biyu da Palo sai dan karamin shago a k'ofar gida
Gwada tambayarta nayi nawa ne gidan.
Tacemin Dubu dari uku da ashirin
Take nace Mata Zan siyi gidan Kamar Wasa ta rakani wajen Mai gidan na nemi ya siyarmin Dubu dari biyu da hamsin dak'yar ya siyar min a Dubu dari biyu da casain
Washegari muka Kai Masa kudin gidan ya d'auko takarda gidan ya bani
Aunty sai murna takemin ni kuwa sai tambayarta nake tana ganin yarana cemin tayi tana ganinsu kar na damu Naseer na kula dasu Dan ta saka Ido a kansu
Take naji hankalina ya Dan kwanta.
A. Cikin kwana uku naja wutan.nepa gidan
Aunty ta Nemo min Katifa second hand na biya da Dan ledar tsakar daki da Dan kayan amfanin gida da bazaa rasa ba.
Wata Hassana da take bazawara da ta kasance Yar uwarsu ta kawomin Akan mu ringa kwana tare Dan Ina tsoron kwana Ni kadai.
Hassana kuwa zata iya girme min Amma tana da kirki
Makotana na zaga na Dan duba abinda baa samu unguwar Naga har da dai markaden sai sunyi tafiya Mai nisa suke samu.
Ana Kuma neman ruwan Sanyi kayan provision ma sai sun Yi tafiya Mai nisa.
Take kuwa na nemi engine second hand na siya Dan gaskiya Ina San sanaar markaden dan ya shigomin da kudi
Cikin Ikon Allah kuwa sati daya da siya aka faramin layi.
Dan har Hassana Tayani takeyi idan na gaji.
Kamar Wasa sauran kudin hannuna na Nemo kafinta ya bubbuga min canter na Dan zuba provision din kad'an su Maggi biscuit bredi da alewa da littattafai makaranta Dan Naga Ana yawan nema
Shima sati da fara siyar da provision din Rabbi ya Sanya min albarka a hankali sai gashi shagon k'ofar gida ya cika da kaya.
Sai gashi a cikin wata biyu har freezer na siya shima na saka a shagon Ina siyar da ruwa.