Sashe 11
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nadeeya ma. Yatsun Murja sai daya fito a kumatunta
A Haka suka Shiga palon suna rab'e rab'e sai data Kara daka musu tsawa Suka zub'e a gaban ta jikinsu na rawa.
Wukan data ajiye a gaban ta ta Dago musu tana "Mai wanan"?
Hade jikinsu sukayi waje daya jkinssu na balain rawar tsoro Zahira har wani fitsari ne ya matseta
"Dan ubanku nace me wanan"
"Wukane Aunty Dan Allah kiyi hakuri karki yanka mu"
Zahira tace tana fashewa da kuka.
"Toh wlh idan Tijjani ya dawo kuka ce na muku wani Abu kukace na Hana ku abinci na rantse da Allah sai na cire muku Ido kunji na rantse muku idan ya dawo kuce Masa kunci abinci Kun koshi ke Kuma da ganinki kin iya munafirci Abu kad'an sai ki hau hawaye wlh ya dawo kikamin wanan kalar tausayin gobe Yana fita sai na yanka ki kunji Mai nace ko bakuji ba"?
Gyada.mata Kai sukayi a tare Dan har ga Allah sun yarda zata yankasun sabida yaran da akwai tsoro ba Kamar na yanzu ba sai a lokacin ta barsu suka zauna a Palo.
Duk a tsorace Suka Kamar su zura da gudu
Ana Kiran Sallah magriba Tijjani ya dawo
Murja tayi sauri ta jawo Nadeeya ta kwantar da kanta a cinyarta
Ta hau shafawa tana "in cigaba da muku tsatsuniyar"?
A daidai lokacin da Tijjani ya shigo Niki Niki da ledoji
A hannunsa
Nadeeya kuwa sai mutsu mutsu take sabida danneta da Murjan tayi a cinyarta tana shafa Mata Kai
Tijjani kuwa washe baki yayi Yana "Uwar biyu keda yaran naki ne kuke Hira"?
Murmushi Murja tayi tana "wlh fa Wai tsatsuniya nake musu ai ba karamin dadi naji ba da zuwansu Dan wlh suna ta deb'emin kewa da sai dai nayi zuru Ni kadai kamar Mayya Nadeeya dai tafi yayarta wayewa Dan ita ta saki jikinta ita kuwa yayarta sai noke noke take Taki sakin jikinta"
Murja ta karashe a daidai lokacin da Tijjani ke amsa gaisuwar da Zahira take Masa kanta a sunkuye
Nadeeya itama gaishe shin tayi a lokacin da Murja ta daina shafa kanta ta mik'e zaune.
Shi kuwa Tijjani cikin Jin dadi ya amsa gaisuwarsu Yana "Ai Zahira Haka take tana da wuyan sabo ko gidansu Kikaje Bai zama lailai kiji maganarta ba har ki dawo
Nadeeya ce dai ba ruwanta.
Kuzo maza kuga kayan Dana siyo muku Tijjani yace Yana janyo katuwar ledar daya shigo dashi.
Murja kuwa kamar ya caka Mata wuka Haka taji a lokacin da ya jawo ledar ya bud'e
Nadeeya kuwa tuni ta Isa wajensa
Zahira kuwa ko dagowa batayi ba ballantana taje Inda yake zaune
Ki taso Mana Kika zauna.
Murja tacewa Zahira cikin murmushi yak'e dayafi kuka ciwo
Zahira kuwa jikinta na rawa ta Isa wajen Tijjani ta zauna a wajen kafarsa
Nadeeya kuwa a gefensa ta zauna
Tana murna da ganin kayan data ke kyautata zaton nasu.ne
Kaya ne masu Dan saukin kudi guda shida shidda iri daya
Sai takalma guda biyu brush biyu har da Mai da Dan turarensu.
Bai tsaya iya Nan ba har da yatsana ya siya musu.
Kamar an cinnawa Murja wuta haka ta ringa ji sai juye juye take ita kadai ita da take d'auke da ciki Tijjani ko pant Bai siya na jariri ba Amma ya laftowa su Zahira uban Kaya
Nadeeya kuwa tsalle tsalle kawai take akan kujeran tana murna yartsana da aka siyo musu shap tama manta da wata Murja a palon balle ta tuna dukan dataci.
Zahira ce ma ta kasa sakin jiki ta ringa satar kallon Murja dake musu wani Irin kallo
Manyan biscuit ya d'auko ya bud'e musu ya bawa kowace guda guda Yana maza suci
Nadeeya da Zahira kuwa sukayi ta mishi godiya
Har wani Dan hawayen bakin ciki ne ya Dan taru a idon Murja
Tana hada Ido da Tijjani ta kakalo murmushi tana "gaskiya ka kyauta Allah ya Kara budi dama dazu nake ta ce wa Basu zo da Kaya ba ko Mai zasu saka"
"Aikuwa gashi na samo musu Wanda zasu ringa Dan sawa Kafin na Karo musu idan na samu kudi.
Ga ayabar da kikace na siyo Miki ga Kuma balangu Nan Leda biyu ki dau babbar ki bani dayan
Murja Haka ta mik'a Masa ledar kamar ta kurma ihu
Tijjani kuwa ya bud'e ledar balangu ya Ajiye Agaban Zahira Nadeeya ta sauko ta hau CI
Zahira kuwa sai juye juye take tana satar kallon Murja a tsorace sai da Murja ta tafi dauko abincin ta iya Kai Naman bakinta.
Nadeeya kuwa ko kallon murjan batayi ba tayi ta Loma balangun
"Murja kuwa abincin ta d'auko ta zuba Masa faten wake da doya Dan Tijjani Yana balain san faten wake da doya
"Aaa Yau Mai dadin Kika Mana kenan"
Zahira maza ku tashi ku wanko hannun ku muci abinci"
Caraf Nadeeya tace "Ai bamu iya cin wake ba"
"Mun koshi Abba dazun Nan mukaci abinci"
Zahira tace cikin rawar murya
"Shaf na manta fa Baku iya cin Wake ba laifina ne da ban gayawa Auntynku ba"
"Ai sun gayamin Dama danake girkin hakane yasa na dafa musu taliya sukaci
Kallon da tayiwa Zahira ne yasa Tijjani na tambayarsu sukayi saurin cewa sunci.taliyar.
Nadeeya kuwa ta maida hankali ta cinye biscuit din da balangu Zahira kuwa tsatsakura tayi sabida tsoro.
Ahaka lokacin kwanciyarsu yayi sukayi shiga daki suka kwanta
Murja kuwa dak'yar tayi bacci sabida bakin ciki.
Washegari Tijjani na fita
Tayi wa Nadeeya mugun duka ta Kara saka su aiki kamar Jiya har dasu wanki Wanda a tunaninta wahala take basu Bata San sun Saba da aikin ba .
Kayan ma kwacewa tayi ta karya ita kadai batare da ta Basu komai ba
Zahira kuwa bredin da suka boye na jiya Suka ci a boye Dan guntun biscuit din ma ta kwace.
Sai data Kara turasu debo ruwa Dan duk a tunaninta a makabartar suka je jiya Nan kuwa Inda suka je jiya Nan suka debo ruwan
Jamilu kuwa Mai shago daya gansu Basu tambayeshi ba ya Basu kyautar biscuit da lemo suka boye a jikinsu
Suna zuwa suka ga ta d'ebo wake ko tsincewa batayi ba ta Dora waken Mai uban yawa ta daka attaruhu ta zabga a ciki
Sai daya dahu ta d'auko Sabulun Canoe data jika tun safe ya narke "(nasan mutanen da zasu Gane koren sabulu Canoe Zahira da wayonta lokacin ita ke bani wanan Labarin Nadeeya ma Bata manta komai ba)
Juye canoe din tayi a cikin waken ta gwamutsa ta d'auko wani farin roba Mai Dan Fadi ta juye a ciki ta saka a fridge ta kalli Zahira da Nadeeya tana "Daga yau wannan shine abinci ku Badai bakwa cin wake ba shegu tsinanu Zakuci ubanku ke Kuma na rantse da Allah idan kina wanan rawar Kan Agaban mijina kina surutu da wanna shegn bakin naki sai na yankaki ta karashe tana rankwashin Nadeeya
A takaice karfe shidda ta zubo musu waken
Akan suci
Zahira kuwa ta ki ci tace ta koshi
Nadeeya kuwa duk da Zahira nata Mata Ido Akan Kar taci
Nadeeya a Haka ta zauna taci waken Nan Yana d'ade Mata harshe tare da soya Mata zuciya
(Wani ikon Allah ba abinda ya samu Nadeeya tana Nan da ranta har yanzu har da yaranta ma )
A takaice sosai Murja ta bud'e babi babi na mugunta tana ganawa su Zahira Tijjani Bai taba Sani ba Dan idan ya kusa dawowa sawa take suyi wanka ta dauko musu kayan da ya siya musu da Yar tsana akan su ringa Wasa dashi shi kuwa Tijjani idan ya dawo Baya ganewa sam
Sosai take musu horar yunwa Zahira ta ringa wani irin Rama.
Indai ta saka wani abu a bakinta jamilu Mai shago ne ya Bata Nadeeya kuwa haka take dirkawa kanta faten wake Mai Sabulun Canoe tayi ta Kashi
Ga uban duka da take musu da sun danyi wani kuskure.
Kullum mak'ota sai sunji ihunsu Zahira.
Tana dirkarsu
A Haka har jamilu Mai shago da abin ya ishe shi sabida tausayinsu Zahiran.yaje har gidan ya kwada Sallama Murja na fitowa ya hau Mata masifa Yana "Kiji tsoron Allah ki daina zalintar yaran Nan idan babu idon iyayensu Allah daya hallicesu Yana kallonki Banda mugunta Mai yaran Nan suka tare Miki da kike musu irin Haka "
"Ina ruwanka Shugaban munafikai ko kashe su nayi Ina ruwanka ka Shiga uku da munafirci wlh ka ficemin daga k'ofar gida kafin na debbo ruwan zafi na watsa maka"
Murja tace cikin masifa
Jamilu zaginta ya cigaba da yi Yana rantsuwar akan sai.ya hadata da hukuma ya kaucewa ruwan data watso Masa ta rufe kofarta
Tana Shiga ciki tayi.kan Zahira da Nadiya ta hau duka Akan sun Kai kararta wajen Jamilu.
A ranar Kuma jamilu yayi ta jiran dawowar Tijjani Dan ya Gaya masa sai Tijjani Bai dawo da wuri ba har ya tashi
Washegari Kuma daya fito Tijjani ya fice.
Karfe takwas yaga Zahira ta fito ita da Nadeeya da bokitan ruwa Akansu
Shi kuwa ya kirasu
Suna zuwa yace "idan na Baku kudin mota zaku iya komawa gidanku"
Da Sauri Zahira ta gyada Masa Kai tana "a gadon Kaya gidanmu yake indai aka saukemu a junction xamu iya xuwa gidanmu a kafa Dan Allah ka taimaka Mana da kudin motar"
Naira Hamsin Jamilu ya d'auko ya bawa Zahira Yana ta ajiye bokitin ma yanzu ta rik'e hannun Nadeeya su gudu.
Ai Zahira da sauri suka dire bokitin ta rik'e hannun Nadeeya suka fara tikar gudu suna wuce gidan Murja ta bud'e kofa Dan ta siyo Madara aikuwa ta hango su Zahira na tikar gudu.
Itama binsu ta fara Yi agujen Taji kafarta ya rik'e.
A daidai lokacin da wani mai vespa yazo wucewa tayi saurin tsayar dashi Akan ya taimaka Mata subi bayan wadancan yaran guduwa zasuyi
Da Sauri ta haye vespan Zahira kuwa Tana ganin Haka ta Kara rike hannun Nadeeya suka cigaba da tikar mugun gudu suna zuwa titi wani bus na k'ok'arin tafiya Zahira.kuwa ta daga hannu biyu ta hau tsyaar da kwandastan
A Haka suka Shiga palon suna rab'e rab'e sai data Kara daka musu tsawa Suka zub'e a gaban ta jikinsu na rawa.
Wukan data ajiye a gaban ta ta Dago musu tana "Mai wanan"?
Hade jikinsu sukayi waje daya jkinssu na balain rawar tsoro Zahira har wani fitsari ne ya matseta
"Dan ubanku nace me wanan"
"Wukane Aunty Dan Allah kiyi hakuri karki yanka mu"
Zahira tace tana fashewa da kuka.
"Toh wlh idan Tijjani ya dawo kuka ce na muku wani Abu kukace na Hana ku abinci na rantse da Allah sai na cire muku Ido kunji na rantse muku idan ya dawo kuce Masa kunci abinci Kun koshi ke Kuma da ganinki kin iya munafirci Abu kad'an sai ki hau hawaye wlh ya dawo kikamin wanan kalar tausayin gobe Yana fita sai na yanka ki kunji Mai nace ko bakuji ba"?
Gyada.mata Kai sukayi a tare Dan har ga Allah sun yarda zata yankasun sabida yaran da akwai tsoro ba Kamar na yanzu ba sai a lokacin ta barsu suka zauna a Palo.
Duk a tsorace Suka Kamar su zura da gudu
Ana Kiran Sallah magriba Tijjani ya dawo
Murja tayi sauri ta jawo Nadeeya ta kwantar da kanta a cinyarta
Ta hau shafawa tana "in cigaba da muku tsatsuniyar"?
A daidai lokacin da Tijjani ya shigo Niki Niki da ledoji
A hannunsa
Nadeeya kuwa sai mutsu mutsu take sabida danneta da Murjan tayi a cinyarta tana shafa Mata Kai
Tijjani kuwa washe baki yayi Yana "Uwar biyu keda yaran naki ne kuke Hira"?
Murmushi Murja tayi tana "wlh fa Wai tsatsuniya nake musu ai ba karamin dadi naji ba da zuwansu Dan wlh suna ta deb'emin kewa da sai dai nayi zuru Ni kadai kamar Mayya Nadeeya dai tafi yayarta wayewa Dan ita ta saki jikinta ita kuwa yayarta sai noke noke take Taki sakin jikinta"
Murja ta karashe a daidai lokacin da Tijjani ke amsa gaisuwar da Zahira take Masa kanta a sunkuye
Nadeeya itama gaishe shin tayi a lokacin da Murja ta daina shafa kanta ta mik'e zaune.
Shi kuwa Tijjani cikin Jin dadi ya amsa gaisuwarsu Yana "Ai Zahira Haka take tana da wuyan sabo ko gidansu Kikaje Bai zama lailai kiji maganarta ba har ki dawo
Nadeeya ce dai ba ruwanta.
Kuzo maza kuga kayan Dana siyo muku Tijjani yace Yana janyo katuwar ledar daya shigo dashi.
Murja kuwa kamar ya caka Mata wuka Haka taji a lokacin da ya jawo ledar ya bud'e
Nadeeya kuwa tuni ta Isa wajensa
Zahira kuwa ko dagowa batayi ba ballantana taje Inda yake zaune
Ki taso Mana Kika zauna.
Murja tacewa Zahira cikin murmushi yak'e dayafi kuka ciwo
Zahira kuwa jikinta na rawa ta Isa wajen Tijjani ta zauna a wajen kafarsa
Nadeeya kuwa a gefensa ta zauna
Tana murna da ganin kayan data ke kyautata zaton nasu.ne
Kaya ne masu Dan saukin kudi guda shida shidda iri daya
Sai takalma guda biyu brush biyu har da Mai da Dan turarensu.
Bai tsaya iya Nan ba har da yatsana ya siya musu.
Kamar an cinnawa Murja wuta haka ta ringa ji sai juye juye take ita kadai ita da take d'auke da ciki Tijjani ko pant Bai siya na jariri ba Amma ya laftowa su Zahira uban Kaya
Nadeeya kuwa tsalle tsalle kawai take akan kujeran tana murna yartsana da aka siyo musu shap tama manta da wata Murja a palon balle ta tuna dukan dataci.
Zahira ce ma ta kasa sakin jiki ta ringa satar kallon Murja dake musu wani Irin kallo
Manyan biscuit ya d'auko ya bud'e musu ya bawa kowace guda guda Yana maza suci
Nadeeya da Zahira kuwa sukayi ta mishi godiya
Har wani Dan hawayen bakin ciki ne ya Dan taru a idon Murja
Tana hada Ido da Tijjani ta kakalo murmushi tana "gaskiya ka kyauta Allah ya Kara budi dama dazu nake ta ce wa Basu zo da Kaya ba ko Mai zasu saka"
"Aikuwa gashi na samo musu Wanda zasu ringa Dan sawa Kafin na Karo musu idan na samu kudi.
Ga ayabar da kikace na siyo Miki ga Kuma balangu Nan Leda biyu ki dau babbar ki bani dayan
Murja Haka ta mik'a Masa ledar kamar ta kurma ihu
Tijjani kuwa ya bud'e ledar balangu ya Ajiye Agaban Zahira Nadeeya ta sauko ta hau CI
Zahira kuwa sai juye juye take tana satar kallon Murja a tsorace sai da Murja ta tafi dauko abincin ta iya Kai Naman bakinta.
Nadeeya kuwa ko kallon murjan batayi ba tayi ta Loma balangun
"Murja kuwa abincin ta d'auko ta zuba Masa faten wake da doya Dan Tijjani Yana balain san faten wake da doya
"Aaa Yau Mai dadin Kika Mana kenan"
Zahira maza ku tashi ku wanko hannun ku muci abinci"
Caraf Nadeeya tace "Ai bamu iya cin wake ba"
"Mun koshi Abba dazun Nan mukaci abinci"
Zahira tace cikin rawar murya
"Shaf na manta fa Baku iya cin Wake ba laifina ne da ban gayawa Auntynku ba"
"Ai sun gayamin Dama danake girkin hakane yasa na dafa musu taliya sukaci
Kallon da tayiwa Zahira ne yasa Tijjani na tambayarsu sukayi saurin cewa sunci.taliyar.
Nadeeya kuwa ta maida hankali ta cinye biscuit din da balangu Zahira kuwa tsatsakura tayi sabida tsoro.
Ahaka lokacin kwanciyarsu yayi sukayi shiga daki suka kwanta
Murja kuwa dak'yar tayi bacci sabida bakin ciki.
Washegari Tijjani na fita
Tayi wa Nadeeya mugun duka ta Kara saka su aiki kamar Jiya har dasu wanki Wanda a tunaninta wahala take basu Bata San sun Saba da aikin ba .
Kayan ma kwacewa tayi ta karya ita kadai batare da ta Basu komai ba
Zahira kuwa bredin da suka boye na jiya Suka ci a boye Dan guntun biscuit din ma ta kwace.
Sai data Kara turasu debo ruwa Dan duk a tunaninta a makabartar suka je jiya Nan kuwa Inda suka je jiya Nan suka debo ruwan
Jamilu kuwa Mai shago daya gansu Basu tambayeshi ba ya Basu kyautar biscuit da lemo suka boye a jikinsu
Suna zuwa suka ga ta d'ebo wake ko tsincewa batayi ba ta Dora waken Mai uban yawa ta daka attaruhu ta zabga a ciki
Sai daya dahu ta d'auko Sabulun Canoe data jika tun safe ya narke "(nasan mutanen da zasu Gane koren sabulu Canoe Zahira da wayonta lokacin ita ke bani wanan Labarin Nadeeya ma Bata manta komai ba)
Juye canoe din tayi a cikin waken ta gwamutsa ta d'auko wani farin roba Mai Dan Fadi ta juye a ciki ta saka a fridge ta kalli Zahira da Nadeeya tana "Daga yau wannan shine abinci ku Badai bakwa cin wake ba shegu tsinanu Zakuci ubanku ke Kuma na rantse da Allah idan kina wanan rawar Kan Agaban mijina kina surutu da wanna shegn bakin naki sai na yankaki ta karashe tana rankwashin Nadeeya
A takaice karfe shidda ta zubo musu waken
Akan suci
Zahira kuwa ta ki ci tace ta koshi
Nadeeya kuwa duk da Zahira nata Mata Ido Akan Kar taci
Nadeeya a Haka ta zauna taci waken Nan Yana d'ade Mata harshe tare da soya Mata zuciya
(Wani ikon Allah ba abinda ya samu Nadeeya tana Nan da ranta har yanzu har da yaranta ma )
A takaice sosai Murja ta bud'e babi babi na mugunta tana ganawa su Zahira Tijjani Bai taba Sani ba Dan idan ya kusa dawowa sawa take suyi wanka ta dauko musu kayan da ya siya musu da Yar tsana akan su ringa Wasa dashi shi kuwa Tijjani idan ya dawo Baya ganewa sam
Sosai take musu horar yunwa Zahira ta ringa wani irin Rama.
Indai ta saka wani abu a bakinta jamilu Mai shago ne ya Bata Nadeeya kuwa haka take dirkawa kanta faten wake Mai Sabulun Canoe tayi ta Kashi
Ga uban duka da take musu da sun danyi wani kuskure.
Kullum mak'ota sai sunji ihunsu Zahira.
Tana dirkarsu
A Haka har jamilu Mai shago da abin ya ishe shi sabida tausayinsu Zahiran.yaje har gidan ya kwada Sallama Murja na fitowa ya hau Mata masifa Yana "Kiji tsoron Allah ki daina zalintar yaran Nan idan babu idon iyayensu Allah daya hallicesu Yana kallonki Banda mugunta Mai yaran Nan suka tare Miki da kike musu irin Haka "
"Ina ruwanka Shugaban munafikai ko kashe su nayi Ina ruwanka ka Shiga uku da munafirci wlh ka ficemin daga k'ofar gida kafin na debbo ruwan zafi na watsa maka"
Murja tace cikin masifa
Jamilu zaginta ya cigaba da yi Yana rantsuwar akan sai.ya hadata da hukuma ya kaucewa ruwan data watso Masa ta rufe kofarta
Tana Shiga ciki tayi.kan Zahira da Nadiya ta hau duka Akan sun Kai kararta wajen Jamilu.
A ranar Kuma jamilu yayi ta jiran dawowar Tijjani Dan ya Gaya masa sai Tijjani Bai dawo da wuri ba har ya tashi
Washegari Kuma daya fito Tijjani ya fice.
Karfe takwas yaga Zahira ta fito ita da Nadeeya da bokitan ruwa Akansu
Shi kuwa ya kirasu
Suna zuwa yace "idan na Baku kudin mota zaku iya komawa gidanku"
Da Sauri Zahira ta gyada Masa Kai tana "a gadon Kaya gidanmu yake indai aka saukemu a junction xamu iya xuwa gidanmu a kafa Dan Allah ka taimaka Mana da kudin motar"
Naira Hamsin Jamilu ya d'auko ya bawa Zahira Yana ta ajiye bokitin ma yanzu ta rik'e hannun Nadeeya su gudu.
Ai Zahira da sauri suka dire bokitin ta rik'e hannun Nadeeya suka fara tikar gudu suna wuce gidan Murja ta bud'e kofa Dan ta siyo Madara aikuwa ta hango su Zahira na tikar gudu.
Itama binsu ta fara Yi agujen Taji kafarta ya rik'e.
A daidai lokacin da wani mai vespa yazo wucewa tayi saurin tsayar dashi Akan ya taimaka Mata subi bayan wadancan yaran guduwa zasuyi
Da Sauri ta haye vespan Zahira kuwa Tana ganin Haka ta Kara rike hannun Nadeeya suka cigaba da tikar mugun gudu suna zuwa titi wani bus na k'ok'arin tafiya Zahira.kuwa ta daga hannu biyu ta hau tsyaar da kwandastan