Sashe 31
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ban hango.kowa ba hakane yasa na dawo d'akina da Sauri anan nagane Zahira ce ta fita waje
Ciikin tashin hankali nayi waje.
Ina dube dube Ina mamakin Ina Zahira ta fita daddare Nan
Sunanta na hau Kira da k'arfi
Zahira kuwa Ashe data fita gida gida ta ringa bi tana rokonsu abinci wasu kuwa har zaginta suke Akan me zata buga musu gida suna bacci
Wasu Kuma Haka zasu zageta ahaka ta cigaba da bin gida gida har ta iso wani gidan data ganshi a bud'e
Tana Shiga ta zub'e a kasa cikin kuka ta hau ce musu "Dan Allah ku taimaka Mana da abinci ummana yunwa takeji ta kasa bacci"
Daga Mai gidan har matar gidan tausayin Zahira ne ya rufesu duk da basu Santa ba.
Abincin da matar ta kawowa Mai gidan da shima Bai Dade da dawowa ba suna Dan tab'a hirane hakane yasa Bai ci abinci ba
Magana ya yiwa matar Akan ta Nemo Leda ta juye mata abinci shi Kuma zai Sha shayi da bredi
Matar mik'ewa tayi ta d'auko Leda ta juya tuwon dake da Dan yawa a bak'ar Leda ta juye miyar yauki shima a wani Leda ta hadasu a wani Leda ta mik'awa Zahira data mike da Sauri ta wafci ledar tana ta gode.
Ta fita a guje cikin murna duk da tsoronta da karnuka Haka ta ringa tikar gudu tana murna samo min abinci
Ni kuwa hankali a tashe na koma ciki na Sako hijabi na Dan na nemota sai dai jiri kawai ke d'ibana jikina na rawa kasa mik'ewa nayi Dana zub'e a tsakiyar dakina.
Kamar Wasa naji shigowrta tare da rufe k'ofar Gidan.
Kitchen naji ta shiga Ni kuwa na hau sauke ajiyar zuciya dawowa da tayi
Shigowa tayi da kwanu a hannunta daya hannun nata Kuma ledar tuwon ne.
Kamshin abinci yasa naji jikina ya Kara kwasar wani rawan
Ina kallonta ta juye tuwon ta zuba Miya a wani kwanun shima ta kawo shi gabana tana "Umma gashi na samo Miki abinci kici Bari na d'ebo Miki ruwa ta Kara yin waje.
Ni kuwa banyi wata wata ba na hau Danna tuwon a bakina Ina hawaye.
Dan inaganin tsaf Zan sume da ban samu tuwon nan ba fada nayi niyyar Mata Amma Ashe abinci taje Nemo min
Kafin ta kawo ruwan ma har na kusa cinye Rabin tuwon
Sai da tuwon ya kusa karewa naji hankalina ya dawo jikina jikina ya bar rawa.
Ruwan data ajiye a gabana na kafa kaina na Sha
Koshin da nayi yasa nayi hamdala a madadin nayiwa Zahira fada sai na hau shi Mata albarka Ashe dai yunwa masifa ce Dan sai yanzu na dawo daidai
Abinan da Zahira.tamin a matsayin ta na diyata Yana cikin Abubuwan da bana mantasu ahaka tana yarinya tasan tausayin iyaye inaga ta girma.
Amma Wai Zahiran Kuma su Umma ke San ganin Bayan ta Mai ta musu da zafi Haka
A dadafe na yi sallah asuba
Na tashi yarana sukayi Zahira kuwa ce Mata nayi kaina ke ciwo badan ta yarda ba ta hakura ta daina min tambayoyi.
Yanzu su suke min komai hakan yasa ban bar d'akina ba Suka had'a hannu Suka Gama aikin komai na gidan suka fara shigomin d'akin Akan sun shirya zasu tafi
Kansu na dafa daya Bayan daya Kamar yanda na Saba na musu addua suka ringa yin waje sai Dana Zo kan Zahira nace "Zahira kiringa addua kinji Allah ya kareki daga sharrin mutum Dana Aljann kiringa karanta ayatul kursiyyu Kafa bakwai idan Zaki bar gidan Nan idan kin dawo ma ki karanta ki kasance a cikin addua kullum Allah ya kareki da karewarsa karkiyi Wasa da Addu'a kinji Zahira Allah ya Miki albarka ban taba nufar Dan kowa da sharri ba insha Allahu ba Abunda zai sameki ki tsaya kiyi alwala sai ki tafi"
Kallona kawai take har na idda maganata amadadin tayi wajen sai ta tsugunna daidai k'afata tana "Umma ko dai wani abune zai sameni dazu da nake shara Naga kwai a cikin kwarya da sunayena"
Girgiza Mata Kai nayi da Sauri tare da mik'ewa.
Ina "ba Abunda zai sameki Zahira Kar ki Kara kallon Inda Kwaryar Nan yake Abbanku nake jira ya dawo maza jekiyi alwala ki tafi karku makara"
Na nufi wajen Dana ajiye Kwaryar da shima yake d'auke da Jan rubutu da sunan Zahira na d'aga katakon gadona na saka a karkashin gadon Dan so nake idan Naseer ya dawo na nuna Masa Yaga shaida wlh bazan d'auki a tabamin Yara ba"
Yanda nake Jin jikina ma kamar na Hana Zahira. Tafiya makaranta Dan sosai nake a tsorace gani nake zasu iya binta har makaranta su Mata wani Abu Amma ba yanda Zan hanata tunda Bai fi sati biyu su zanna jarrabawa Gama jnr secondary ba"
Har waje na rakasu Bayan tayi alwala yanda take Abu jiki ba kwari yasa na kwantar Mata da hankali har na daina hangosu gabadaya zuciyata ba dadi Haka na dawo gida
Ina kukan tashin hankali da nake ji a jikina Yana tunkaroni a da na dauka na samu kwanciyar hankali Ashe akwai wani masifar dake tunkaroni bansani ba
Masifar da nakeji zuciyata bazata iya dauka ba idan har su Umma suka ci Galaba Akan Zahira ga irin abinda nake gayawa Naseer Nan da har yake Jin haushina.
.
A ranar kasa komai nayi zuciyata na wajen su Zahira abincin rana ma ban iya Yi ba karshe dai waje na fita Dan sosai naji na kasa samun kwanciyar hankali sai Dana hangosu hankalina ya kwanta na koma ciki na daura alwala azahar.
Ina iddar da sallah na fito na Dora musu farar taliya Dan inada Miya
Sai a lokacin na daure na saka Abu a bakina shima Dan Kar Zahira ta zargi wani Abun Dan nasan halin ta
A takaice ahaka na ringa dari dari indai su Zahira suka tafi makaranta sai sun dawo hankalina ke kwanciya
Bacci Kam bana Iya yin shi cikin nutsuwa Rabin Daren rayya shi nake Ina kaiwa Allah kukana haka ma nake tashin Zahira tayi duk da Bata iya jurewan tana Yi sai dai na juya naga tayi bacci
Ban iya larabci ba da hausa nake adduoina Dan nasan ba yaren da Allah baya ji Yana jina Yana Kuma ganin duk abinda ke faruwa Dani Allah yasan zuciyata tayi rauni bana Jin Zan iya jure ganin wani Abu ya Samu yarana da nake ganin su kadai ne farinciki na a gidan Duniya a lahira kuma Allah ya bani Aljanna.
Har wani irin Rama nayi Sabida tashin hankali Dan idan dare yyi Haka Zan ta sintiri daga d'akina zuwa kofar gida Wai ko zasu Kara aiko wani.
Duk da ban Kara ganin kowa ba sabida dadewar da akayi hakan bai saka na saki jikina ba
A ranar laraba da bazan manta ba na Kara sanin suwaye Umma Ina zaune a tsakar gida Ina tsince wanke da Zan Mana abinci dashi ba kowa a gidan Dan dukansu sun tafi makaranta Isihu ma ya tafi wajen Aunty matar Mallam zai Kai Mata sako
Sai dai idan anzo siyan Abu na Shiga ta tsakar gida na bada abinda aka zo siyan.
Sallama da naji da yazo daidai da bugun zuciyata yasa na Dago bakina d'auke da Addu'a na amsa Sallamar a daidai lokacin da Wata Saude da take makociyarmu ta shigo makociyata ce data takuramin da karbar kayana Bata bani kudi hakane yasa Dana gaji na daina Bata shima su Nadeeya ne suka cemin tana zuwa wani shagon siyan Abu da kudi shagona ne take aikowa karbar bashi ko a yanzu ma data shigo bazan iya tuna adadin kudina dake wajenta ba.
Cikin sakin fuska na Mata iso dana ga fuskarta a sake tana sanye da dogon hijabi hannayenta a ciki.
Tabarmar danake Kai na Kara bajewa Ina "Zauna Mana mmn maimuna"
Cire takalminta tayi ta hau Kan tabarma ta zauna tana "mmn Zahira Ina wuni"
"Lafiya Lau ya su maimuna"?
"Suna Nan kalau"
Tace tana cigaba da jujuya hannu a cikin hijabi Ni Kuma Haka kawai naji zuciyata na bugawa bansan dalili ba.
Adduoi kawai nake a Zuciyata ita kuwa tayi shiru Bata ce komai ba
Ni kuwa nace Mata lafiya Dan bata Saba shigomin ba balle nace shigowa tayi Dan mu gaisa
Murmushi tayi tana lafiya Lau shigowa kawai nayi mu gaisa
Ni kuwa da zuciyata ke cigaba da bugawa nace mata ta kyauta na mike na Shiga kitchen na debo Mata ruwa a Raina Kuma inata addua fad'uwar gaban da nakeji tunda ta shigo Ina Kuma mamakin dalilin zuwan nata da Sam ban ji na yarda da ita ba
Agabanta na ajiye ruwan Ina "Bismillah ga ruwa"
Girgiza min Kai tayi da Sauri tana ta koshi har lokacin hannunta na cikin hijabi tana Dan kalle kalle
"Ke kadai ce kenan a gidan banji Motsin su Zahira ba"?
Tace cikin murmushi Nima cikin murmushi nace Mata eee wlh Ni kadai ce.
Sallama ake ta rafkawa ana San siyan Abu Amma fir naki tashi Dan Sam ban yarda da Matar Nan da ta shigo min ba ita kuwa cewa take na tashi Mana na sallami customers Dina Ni kuwa na girgixa mata Kai Ina "ba wani abin arzkik zasu siya ba abinda ma suke nema babu"
Na karasa Ina karantar yanda tayi Jim Bata ji dadin magana ta ba Hakan kuwa yasa na Kara gasgata zargin ba alheri ne ya kawota gidana ba.
Zama na gyara sosai Ita kuwa ta cigaba da kame kame tana surutun ta ita kadai
Ni kuwa jinta kawai nake Ina mamakin abinda yasa ta saka hannayenta a hijabi Sanin Dana Mata ma ba ma'abociyar saka hijabi bace ban dai ce komai ba na cigaba da wayancewa kamar gyara waken nake Amma idona na kanta
Muryata daya doki kunnena da "Mmn Zahira wlh fitsari ne ya matseni Ina bandaki nayi Dan Allah"
Sosai naji kirjina ya tsananta Bugu jikina na kwasar rawa
Sai Dana dau mintina kafin na iya nuna mata band'akin Tsakar gidan
Mik'ewa tayi da Sauri har lokacin hannunta na cikin hijabi ni kuwa nace Mata "Ga buta Nan da ruwa a ciki babu ruwa a band'akin
Wajen band'akin ta nufa da Sauri tana ta mutsu mutsu da hannu
Ciikin tashin hankali nayi waje.
Ina dube dube Ina mamakin Ina Zahira ta fita daddare Nan
Sunanta na hau Kira da k'arfi
Zahira kuwa Ashe data fita gida gida ta ringa bi tana rokonsu abinci wasu kuwa har zaginta suke Akan me zata buga musu gida suna bacci
Wasu Kuma Haka zasu zageta ahaka ta cigaba da bin gida gida har ta iso wani gidan data ganshi a bud'e
Tana Shiga ta zub'e a kasa cikin kuka ta hau ce musu "Dan Allah ku taimaka Mana da abinci ummana yunwa takeji ta kasa bacci"
Daga Mai gidan har matar gidan tausayin Zahira ne ya rufesu duk da basu Santa ba.
Abincin da matar ta kawowa Mai gidan da shima Bai Dade da dawowa ba suna Dan tab'a hirane hakane yasa Bai ci abinci ba
Magana ya yiwa matar Akan ta Nemo Leda ta juye mata abinci shi Kuma zai Sha shayi da bredi
Matar mik'ewa tayi ta d'auko Leda ta juya tuwon dake da Dan yawa a bak'ar Leda ta juye miyar yauki shima a wani Leda ta hadasu a wani Leda ta mik'awa Zahira data mike da Sauri ta wafci ledar tana ta gode.
Ta fita a guje cikin murna duk da tsoronta da karnuka Haka ta ringa tikar gudu tana murna samo min abinci
Ni kuwa hankali a tashe na koma ciki na Sako hijabi na Dan na nemota sai dai jiri kawai ke d'ibana jikina na rawa kasa mik'ewa nayi Dana zub'e a tsakiyar dakina.
Kamar Wasa naji shigowrta tare da rufe k'ofar Gidan.
Kitchen naji ta shiga Ni kuwa na hau sauke ajiyar zuciya dawowa da tayi
Shigowa tayi da kwanu a hannunta daya hannun nata Kuma ledar tuwon ne.
Kamshin abinci yasa naji jikina ya Kara kwasar wani rawan
Ina kallonta ta juye tuwon ta zuba Miya a wani kwanun shima ta kawo shi gabana tana "Umma gashi na samo Miki abinci kici Bari na d'ebo Miki ruwa ta Kara yin waje.
Ni kuwa banyi wata wata ba na hau Danna tuwon a bakina Ina hawaye.
Dan inaganin tsaf Zan sume da ban samu tuwon nan ba fada nayi niyyar Mata Amma Ashe abinci taje Nemo min
Kafin ta kawo ruwan ma har na kusa cinye Rabin tuwon
Sai da tuwon ya kusa karewa naji hankalina ya dawo jikina jikina ya bar rawa.
Ruwan data ajiye a gabana na kafa kaina na Sha
Koshin da nayi yasa nayi hamdala a madadin nayiwa Zahira fada sai na hau shi Mata albarka Ashe dai yunwa masifa ce Dan sai yanzu na dawo daidai
Abinan da Zahira.tamin a matsayin ta na diyata Yana cikin Abubuwan da bana mantasu ahaka tana yarinya tasan tausayin iyaye inaga ta girma.
Amma Wai Zahiran Kuma su Umma ke San ganin Bayan ta Mai ta musu da zafi Haka
A dadafe na yi sallah asuba
Na tashi yarana sukayi Zahira kuwa ce Mata nayi kaina ke ciwo badan ta yarda ba ta hakura ta daina min tambayoyi.
Yanzu su suke min komai hakan yasa ban bar d'akina ba Suka had'a hannu Suka Gama aikin komai na gidan suka fara shigomin d'akin Akan sun shirya zasu tafi
Kansu na dafa daya Bayan daya Kamar yanda na Saba na musu addua suka ringa yin waje sai Dana Zo kan Zahira nace "Zahira kiringa addua kinji Allah ya kareki daga sharrin mutum Dana Aljann kiringa karanta ayatul kursiyyu Kafa bakwai idan Zaki bar gidan Nan idan kin dawo ma ki karanta ki kasance a cikin addua kullum Allah ya kareki da karewarsa karkiyi Wasa da Addu'a kinji Zahira Allah ya Miki albarka ban taba nufar Dan kowa da sharri ba insha Allahu ba Abunda zai sameki ki tsaya kiyi alwala sai ki tafi"
Kallona kawai take har na idda maganata amadadin tayi wajen sai ta tsugunna daidai k'afata tana "Umma ko dai wani abune zai sameni dazu da nake shara Naga kwai a cikin kwarya da sunayena"
Girgiza Mata Kai nayi da Sauri tare da mik'ewa.
Ina "ba Abunda zai sameki Zahira Kar ki Kara kallon Inda Kwaryar Nan yake Abbanku nake jira ya dawo maza jekiyi alwala ki tafi karku makara"
Na nufi wajen Dana ajiye Kwaryar da shima yake d'auke da Jan rubutu da sunan Zahira na d'aga katakon gadona na saka a karkashin gadon Dan so nake idan Naseer ya dawo na nuna Masa Yaga shaida wlh bazan d'auki a tabamin Yara ba"
Yanda nake Jin jikina ma kamar na Hana Zahira. Tafiya makaranta Dan sosai nake a tsorace gani nake zasu iya binta har makaranta su Mata wani Abu Amma ba yanda Zan hanata tunda Bai fi sati biyu su zanna jarrabawa Gama jnr secondary ba"
Har waje na rakasu Bayan tayi alwala yanda take Abu jiki ba kwari yasa na kwantar Mata da hankali har na daina hangosu gabadaya zuciyata ba dadi Haka na dawo gida
Ina kukan tashin hankali da nake ji a jikina Yana tunkaroni a da na dauka na samu kwanciyar hankali Ashe akwai wani masifar dake tunkaroni bansani ba
Masifar da nakeji zuciyata bazata iya dauka ba idan har su Umma suka ci Galaba Akan Zahira ga irin abinda nake gayawa Naseer Nan da har yake Jin haushina.
.
A ranar kasa komai nayi zuciyata na wajen su Zahira abincin rana ma ban iya Yi ba karshe dai waje na fita Dan sosai naji na kasa samun kwanciyar hankali sai Dana hangosu hankalina ya kwanta na koma ciki na daura alwala azahar.
Ina iddar da sallah na fito na Dora musu farar taliya Dan inada Miya
Sai a lokacin na daure na saka Abu a bakina shima Dan Kar Zahira ta zargi wani Abun Dan nasan halin ta
A takaice ahaka na ringa dari dari indai su Zahira suka tafi makaranta sai sun dawo hankalina ke kwanciya
Bacci Kam bana Iya yin shi cikin nutsuwa Rabin Daren rayya shi nake Ina kaiwa Allah kukana haka ma nake tashin Zahira tayi duk da Bata iya jurewan tana Yi sai dai na juya naga tayi bacci
Ban iya larabci ba da hausa nake adduoina Dan nasan ba yaren da Allah baya ji Yana jina Yana Kuma ganin duk abinda ke faruwa Dani Allah yasan zuciyata tayi rauni bana Jin Zan iya jure ganin wani Abu ya Samu yarana da nake ganin su kadai ne farinciki na a gidan Duniya a lahira kuma Allah ya bani Aljanna.
Har wani irin Rama nayi Sabida tashin hankali Dan idan dare yyi Haka Zan ta sintiri daga d'akina zuwa kofar gida Wai ko zasu Kara aiko wani.
Duk da ban Kara ganin kowa ba sabida dadewar da akayi hakan bai saka na saki jikina ba
A ranar laraba da bazan manta ba na Kara sanin suwaye Umma Ina zaune a tsakar gida Ina tsince wanke da Zan Mana abinci dashi ba kowa a gidan Dan dukansu sun tafi makaranta Isihu ma ya tafi wajen Aunty matar Mallam zai Kai Mata sako
Sai dai idan anzo siyan Abu na Shiga ta tsakar gida na bada abinda aka zo siyan.
Sallama da naji da yazo daidai da bugun zuciyata yasa na Dago bakina d'auke da Addu'a na amsa Sallamar a daidai lokacin da Wata Saude da take makociyarmu ta shigo makociyata ce data takuramin da karbar kayana Bata bani kudi hakane yasa Dana gaji na daina Bata shima su Nadeeya ne suka cemin tana zuwa wani shagon siyan Abu da kudi shagona ne take aikowa karbar bashi ko a yanzu ma data shigo bazan iya tuna adadin kudina dake wajenta ba.
Cikin sakin fuska na Mata iso dana ga fuskarta a sake tana sanye da dogon hijabi hannayenta a ciki.
Tabarmar danake Kai na Kara bajewa Ina "Zauna Mana mmn maimuna"
Cire takalminta tayi ta hau Kan tabarma ta zauna tana "mmn Zahira Ina wuni"
"Lafiya Lau ya su maimuna"?
"Suna Nan kalau"
Tace tana cigaba da jujuya hannu a cikin hijabi Ni Kuma Haka kawai naji zuciyata na bugawa bansan dalili ba.
Adduoi kawai nake a Zuciyata ita kuwa tayi shiru Bata ce komai ba
Ni kuwa nace Mata lafiya Dan bata Saba shigomin ba balle nace shigowa tayi Dan mu gaisa
Murmushi tayi tana lafiya Lau shigowa kawai nayi mu gaisa
Ni kuwa da zuciyata ke cigaba da bugawa nace mata ta kyauta na mike na Shiga kitchen na debo Mata ruwa a Raina Kuma inata addua fad'uwar gaban da nakeji tunda ta shigo Ina Kuma mamakin dalilin zuwan nata da Sam ban ji na yarda da ita ba
Agabanta na ajiye ruwan Ina "Bismillah ga ruwa"
Girgiza min Kai tayi da Sauri tana ta koshi har lokacin hannunta na cikin hijabi tana Dan kalle kalle
"Ke kadai ce kenan a gidan banji Motsin su Zahira ba"?
Tace cikin murmushi Nima cikin murmushi nace Mata eee wlh Ni kadai ce.
Sallama ake ta rafkawa ana San siyan Abu Amma fir naki tashi Dan Sam ban yarda da Matar Nan da ta shigo min ba ita kuwa cewa take na tashi Mana na sallami customers Dina Ni kuwa na girgixa mata Kai Ina "ba wani abin arzkik zasu siya ba abinda ma suke nema babu"
Na karasa Ina karantar yanda tayi Jim Bata ji dadin magana ta ba Hakan kuwa yasa na Kara gasgata zargin ba alheri ne ya kawota gidana ba.
Zama na gyara sosai Ita kuwa ta cigaba da kame kame tana surutun ta ita kadai
Ni kuwa jinta kawai nake Ina mamakin abinda yasa ta saka hannayenta a hijabi Sanin Dana Mata ma ba ma'abociyar saka hijabi bace ban dai ce komai ba na cigaba da wayancewa kamar gyara waken nake Amma idona na kanta
Muryata daya doki kunnena da "Mmn Zahira wlh fitsari ne ya matseni Ina bandaki nayi Dan Allah"
Sosai naji kirjina ya tsananta Bugu jikina na kwasar rawa
Sai Dana dau mintina kafin na iya nuna mata band'akin Tsakar gidan
Mik'ewa tayi da Sauri har lokacin hannunta na cikin hijabi ni kuwa nace Mata "Ga buta Nan da ruwa a ciki babu ruwa a band'akin
Wajen band'akin ta nufa da Sauri tana ta mutsu mutsu da hannu