Sashe 52
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sana'ar ma da nakeyi Yan bashi sunfi yawa.
Da taimakon Allah da arzikin Yaya Mata da Allah yamin asirina ke rufe dan Nadeeya da Minal ba laifi ma nemansu suna iya k'ok'arinsu wajen kyautata musu Wanda a hasashena da biyu sukeyi tunda sunga halin da muke ciki.
Duk da mafarkin Ina rufe Ido zanyi hakan bai saka na girgiza da san fasa tafiyar ba.
Addu'a kawai nake da sadaka
Ana saura kwana biyu na tafi da yamma Ina zaune a tsakar gida.
Waleed ya shigo gidan ba Sallama bai Kuma gaisheni ba ya shige daki ya Tara uban gashi kamar mace yaron da bai wuce shekara Sha hud'u zuwa biyar ba Nan da Nan ya Ajiye saje da gemu.
A duk abinan abinda ke kwantar min da hankali bai wuce shaye shaye da ba yayi ba
Da Ido na bishi har ya shige daki.
A hankali na cigaba da sauke numfashin da naji Yana min wahala kirjina yamin nauyi
Daga ni sai Inna Amina ke gidan
Dan duk sun tafi islamiyya.
Mik'ewa nayi na Shiga d'akin da ya Shiga.
A Gefen gado nagan shi a zaune yana gyara wani Abu irin da ake Jin kida dashi da matasa ke yayi (Bluetooth)
Shigowana bai saka ya d'ago ya kalleni ba illa Yan kananan wukakensa daya ajiye a gefensa daya d'auke a mayarsu cikin gidansu ya saka a Aljihun wandonsa
Girgiza Kai na nayi na zauna a gefensa kirjina kamar ya Fado danaga yanda ya Tara farce cikin sanyin murya nace "Waleeed"
Sai dana Kira shi ya Kai sau uku kafin ya d'ago
Hada idon da nayi dashi yasa hawaye hau zubomin.
Waleed ya rame sosai yayi duhu duk da ba fari bane.
Cikin idonsa kawai in ka kalla zaka san Sam dabiun daya ke yi aransa yayi ba halinsa bane.
Yana Nan a yaro Mai hankali Mai tarbiyya canza shi kawai akayi.
Shima rashin Jin Rama yake saka shi.
"Allah ya shiryeka Waleed Allah ya dubeni da idon rahama yasa Kai da Zahira ku dawo yanda kuke a da Waleed nasan duk abinan da kakeyi ba yin kanka bane Waleed ka rage rashin ji kaji ka tausaya min Kar na mutu lokacina baiyi ba.
Dan Allah bani wuk'akk'en nan da ka sa a Aljihunka"?
Tunda na fara magana cikin hawaye naga Waleed jikinsa yayi sanyi Kamar ba shi ba
Cikin bin umarnina daya saka naji kamar na taka rawa ya mikomin wuk'ar
Ni kuwa na cigaba da Masa naseeha
Rabon da na zauna waje daya dashi haka har na manta.
Damar Dana samu yasa nace bari na dauko abin aski na aske Masa uban gashin daya tara da nake ganin kamar zai iya saka shi ciwon Kai.
Ganin bai wani motsa ba yasa cikin farinciki jin Kamar Dana ya fara warkewa nayi d'akina da Sauri dan na dauko.abin askin Dana siya musamman dan shi
dan ni ke masa aski.
Sai dai Ina dawowa naga baya Nan sai wani farin takarda da ya Ajiye
D'aukar takarda nayi Naga yasa "Ina yawan munanan mafarki akanki Umma ki dage da Addu'a"
A ranar nayi kukan da ban taba irinsa ba wato Dana duk da an juyar masa.da.kai yasan yamin magana Mai dadi
Kamar Wanda ya karamin karfin gwiwa nayi tafiya dan na samo musu lafiya.
Na kudunduna takarda na fito daga d'akin
A daidai lokacin da Inna Amina ta hau kwalla min Kira.
Da Sauri na Shiga d'akin Bayan na share hawayena
Ga mamakina ita ma sai cemin tayi "kwana biyu Ina munanan mafarki akanki mamana Ina yawan ganinki a mumunan hali dan Allah ki dage da Addu'a"
Kamar ta sassareni da guduma haka naji ya akayi Inna Amina da Waleed sukayi mafarki iri daya
Tuni na fara Jin tafiyar na ficemin a rai Amma kasan zuciyata kamar ingizani ake akan tafiyar da zanyi shine zai saka yarana su warke.
Ina fitowa itama Zahira ta fado gidan Kamar wacce aka jefo tana sanye da matsassun Kaya Muna hada Ido ta sauke ajiyar zuciya ta kad'a kanta tayi daki.
Itama bin bayanta nayi kamar yanda nabi bayan Waleed itama na hau Mata naseeha kamar yanda nayiwa Waleed ta nutsu kamar gaske duk da bata cemin komai ba
Itama kusanci Dana samu da ita da karantar ta da nayi ya kwantar min da hankali ba kadan ba.
Dan duk abinan tsorona ta wulakanta kanta a rabata da martabarta.
Dawowar su Nadeeya gidan yasa suka haura da Minal ta zuciya ta bar gidan.
Abinda ke ingizani nayi tafiyar tuni ya motsamin naji na matsu jibi tayi na tafi.
A ranar bacci yayi ta daukata Ina mafarkin Ina hauka tub'uran
Wajejan asuba nayi mafarki da mahaifiyata ranta a b'ace tana tamin gargadi Kar k'afata ta bar garin Kano Ina barin garin Kano an samu abinda akeso.
Ba iya Mahaifiyata ba har da mahaifina da ba kasafai nake mafarki dashi ba.
Kamar a gaske nayi mafarkin
Tashina da Nadeeya keyi akan na makara sallah asuba yasa na mike a firgice Ina gumi.
Kirjina na balain bugawa mafarkin da nake bai tab'a dagamin hankali Kamar wanan ba.
Karo na farko da naji bana san yi tafiyar Amma abinda ke tunzurani nayi tafiyar na Kara ingizani.
Nayi Sallah ne kawai amma ba'a nutse ba dan mafarkin da nayi ya tsayamin a rai sosai kwakwalwata ta kasa bani hadin Kai nayi tunani.
A haka yarana suka bar gidan
Jiki ba kwari na shiga d'akin Inna Amina.
Ido ta zuba min har na ajiye flask din kunun dasu Nadeeya suka Dama mata
Na gaisheta a madadin ta amsa min sai cewa tayi "Da kin d'aukeni tamkar Mahaifiyarki Kamar yanda kike fada da baki ringa min boye boye ba Naeema ni nasan akwai abinda kike boyemin da nake ji a jikina ba alheri bane a gareki Naeema sanin da na Miki ba haka kike ba kin kasance yarinya Mai balain hakuri da tunani duk abinda ya Sameki kina Imani cewar Allah ne ya rubuta a takardarki akan zai sameki ba mutum ba sai dai mutum ya zama sila tunda ga farkon haihuwarki har zuwa lokacin da zaki koma ga Allah Allah ya riga da ya tsara Miki rayuwarki babu dan Adam daya Isa ya canja shi
Idan Kika duba baya da Abubuwan da Suka faru dake da Imani da kikayi da Allah kin samu maganin matsalolinki batare da kin wahala ba
Amma akan abinda ya samu yaranki imaninki yayi rauni har kina tunanin sai kin je wajen wayanda muke hasashen sune silar shigar yaranki wanan halin kina nufin Allah baifi karfinsu ba sai har kinje kin rokesu su warware abinda sukayi.
Abaya su ne suke Miki maganin matsalarki?su Kika je Kika samu akan larurar Zahira?
Mai yasa bazaki dogara ga Allah ya isar Miki kamar yanda ya isar Miki a baya ba Naeema"?
Tamkar yata na d'aukeki idan Abu ya Samu bawa Allah yake gayawa ya magance Masa matsalarsa domin Allah Mai jine Mai Kuma gani duk halin da bawansa zai Shiga yana sane sai dai mu muyi gajeran hakuri kamar yanda kike yi yanzu
Karki ga muna ta ga yawa Allah har yanzu shiru wlh Yana sane zai amsa Mana a lokacin da bamu zata ba wuyanta muyi hakuri dan haka kiyi hakuri ki koma ga Allah ki cigaba da gaya Masa Yana sane dake zai amsa Miki insha Allahu.
Domin matsalarsu nayi azumin kwana bakwai da niyyar Allah ya warware duk abinda aka yiwa yaran nan ga ruwan zamzam nan kiyi kokari su biyun su Sha ki Kuma shafe musu jikinsu dashi zamu dace watarana insha Allahu"
Kuka na fashe dashi sosai dan tabbas duk abinda ta fada gaskiya ne imanina yayi rauni akan San yarana su warke.
Ni kaina nasan yanda nake dukufa da Addu'a a baya ba haka nakeyi ba yanzu.
Ina sallah Ina tunani karshe idan naga zuciyata baa nutse take ba sai na hakura da sallah.
Godiya na ringa mata a raina Ina Jin na hakura da tafiyar ba Inda zani Zan cigaba da gayawa Allah sai a lokacin tunanin Naseer ya fad'omin arai.
Har nayi tunanin ko ina yake yanzu na Kuma ringa Jin kamar ban kyauta korarsa da nayi daga gidana da bai kareni da komai bama sai asara dana tafka ta hanyar siyar da gidana
"(Duk.mafarkin hauka dinan da komai ba fiction haka tayi mafarki Allah ya tsallakar da ita)
Calabar
Safiyya
Tunda ta samu cikar burinta akan Zahira da Waleed take cikin tsananin farin ciki zuciyarta v
bata tab'a k'issa mata alheri ba sai sharri
A duk lokacin data bude ido taga hauwa yarta da ta siffantu da d'abba takan ji tsanar Naeema da duk ahalinta.
A idonta gani take ko ta samu nassarar kashe Naeema da yaranta har da Naseer da ya Zama babban makiyinta zuciyata bazata taba sanyi ba tunda duk a silarsu take Kan Shan wuya da hauwa da take Mata fatan mutuwa sabida wahala da take Sha akanta
Dakyar ta samu tayi abubuwan da tayi Bashir ya fito daga prison Wanda ta gwammaci har zamansa a can da sakinsa da akayi.
Mugun barawo ne dan d'abba mashayi.
Da cikin da ta Kara samu da baban Hauwa Bashir ke nada Mata mugun duka idan yayi shaye shayensa
Sata kuwa baa Kama hannun yaro
Halayen Bashir yasa mahafin hauwa sakinta saki uku bayan ya kwashe duka kayansa ya bar gidan
Dan kananan sanaoi da take shi ke sawa ta samu na abinci har yaranta su samu Suma da sun kawo girman da take fatan su fara samun Samarin da zasu na kashe musu kudi.
Kamar yanda taci buri akansu take fatan Yan biyun nata suyi farin jini irin na Zahira sai dai shiru.
Da tsohon cikinta Bashir ya Sha jawo mata a kulle ta dan amfana da Oban keyi da ita yasa yake siddabarun da ake sakinta.
A cikin wahala ta haihu da ita kanta batasan cikin na baban Hauwa bane ko Oban da baya iya Bata ko sisi amma duk wani Abu na mugunta Idan Tana so zai Mata akan bashi.
Rabi ta sawa yarta data haifa Dan kudaden data samo dan ta dan siyi abinci da zasu ci ita dasu Yan biyu
Haka Bashir yazo da wuka yace ta bashi.
Tana gardama ya rufeta da duka Kamar ba uwarsa ba ya dau wukarsa Mai kaifi ya tsage Mata fuska dashi..
Da taimakon Allah da arzikin Yaya Mata da Allah yamin asirina ke rufe dan Nadeeya da Minal ba laifi ma nemansu suna iya k'ok'arinsu wajen kyautata musu Wanda a hasashena da biyu sukeyi tunda sunga halin da muke ciki.
Duk da mafarkin Ina rufe Ido zanyi hakan bai saka na girgiza da san fasa tafiyar ba.
Addu'a kawai nake da sadaka
Ana saura kwana biyu na tafi da yamma Ina zaune a tsakar gida.
Waleed ya shigo gidan ba Sallama bai Kuma gaisheni ba ya shige daki ya Tara uban gashi kamar mace yaron da bai wuce shekara Sha hud'u zuwa biyar ba Nan da Nan ya Ajiye saje da gemu.
A duk abinan abinda ke kwantar min da hankali bai wuce shaye shaye da ba yayi ba
Da Ido na bishi har ya shige daki.
A hankali na cigaba da sauke numfashin da naji Yana min wahala kirjina yamin nauyi
Daga ni sai Inna Amina ke gidan
Dan duk sun tafi islamiyya.
Mik'ewa nayi na Shiga d'akin da ya Shiga.
A Gefen gado nagan shi a zaune yana gyara wani Abu irin da ake Jin kida dashi da matasa ke yayi (Bluetooth)
Shigowana bai saka ya d'ago ya kalleni ba illa Yan kananan wukakensa daya ajiye a gefensa daya d'auke a mayarsu cikin gidansu ya saka a Aljihun wandonsa
Girgiza Kai na nayi na zauna a gefensa kirjina kamar ya Fado danaga yanda ya Tara farce cikin sanyin murya nace "Waleeed"
Sai dana Kira shi ya Kai sau uku kafin ya d'ago
Hada idon da nayi dashi yasa hawaye hau zubomin.
Waleed ya rame sosai yayi duhu duk da ba fari bane.
Cikin idonsa kawai in ka kalla zaka san Sam dabiun daya ke yi aransa yayi ba halinsa bane.
Yana Nan a yaro Mai hankali Mai tarbiyya canza shi kawai akayi.
Shima rashin Jin Rama yake saka shi.
"Allah ya shiryeka Waleed Allah ya dubeni da idon rahama yasa Kai da Zahira ku dawo yanda kuke a da Waleed nasan duk abinan da kakeyi ba yin kanka bane Waleed ka rage rashin ji kaji ka tausaya min Kar na mutu lokacina baiyi ba.
Dan Allah bani wuk'akk'en nan da ka sa a Aljihunka"?
Tunda na fara magana cikin hawaye naga Waleed jikinsa yayi sanyi Kamar ba shi ba
Cikin bin umarnina daya saka naji kamar na taka rawa ya mikomin wuk'ar
Ni kuwa na cigaba da Masa naseeha
Rabon da na zauna waje daya dashi haka har na manta.
Damar Dana samu yasa nace bari na dauko abin aski na aske Masa uban gashin daya tara da nake ganin kamar zai iya saka shi ciwon Kai.
Ganin bai wani motsa ba yasa cikin farinciki jin Kamar Dana ya fara warkewa nayi d'akina da Sauri dan na dauko.abin askin Dana siya musamman dan shi
dan ni ke masa aski.
Sai dai Ina dawowa naga baya Nan sai wani farin takarda da ya Ajiye
D'aukar takarda nayi Naga yasa "Ina yawan munanan mafarki akanki Umma ki dage da Addu'a"
A ranar nayi kukan da ban taba irinsa ba wato Dana duk da an juyar masa.da.kai yasan yamin magana Mai dadi
Kamar Wanda ya karamin karfin gwiwa nayi tafiya dan na samo musu lafiya.
Na kudunduna takarda na fito daga d'akin
A daidai lokacin da Inna Amina ta hau kwalla min Kira.
Da Sauri na Shiga d'akin Bayan na share hawayena
Ga mamakina ita ma sai cemin tayi "kwana biyu Ina munanan mafarki akanki mamana Ina yawan ganinki a mumunan hali dan Allah ki dage da Addu'a"
Kamar ta sassareni da guduma haka naji ya akayi Inna Amina da Waleed sukayi mafarki iri daya
Tuni na fara Jin tafiyar na ficemin a rai Amma kasan zuciyata kamar ingizani ake akan tafiyar da zanyi shine zai saka yarana su warke.
Ina fitowa itama Zahira ta fado gidan Kamar wacce aka jefo tana sanye da matsassun Kaya Muna hada Ido ta sauke ajiyar zuciya ta kad'a kanta tayi daki.
Itama bin bayanta nayi kamar yanda nabi bayan Waleed itama na hau Mata naseeha kamar yanda nayiwa Waleed ta nutsu kamar gaske duk da bata cemin komai ba
Itama kusanci Dana samu da ita da karantar ta da nayi ya kwantar min da hankali ba kadan ba.
Dan duk abinan tsorona ta wulakanta kanta a rabata da martabarta.
Dawowar su Nadeeya gidan yasa suka haura da Minal ta zuciya ta bar gidan.
Abinda ke ingizani nayi tafiyar tuni ya motsamin naji na matsu jibi tayi na tafi.
A ranar bacci yayi ta daukata Ina mafarkin Ina hauka tub'uran
Wajejan asuba nayi mafarki da mahaifiyata ranta a b'ace tana tamin gargadi Kar k'afata ta bar garin Kano Ina barin garin Kano an samu abinda akeso.
Ba iya Mahaifiyata ba har da mahaifina da ba kasafai nake mafarki dashi ba.
Kamar a gaske nayi mafarkin
Tashina da Nadeeya keyi akan na makara sallah asuba yasa na mike a firgice Ina gumi.
Kirjina na balain bugawa mafarkin da nake bai tab'a dagamin hankali Kamar wanan ba.
Karo na farko da naji bana san yi tafiyar Amma abinda ke tunzurani nayi tafiyar na Kara ingizani.
Nayi Sallah ne kawai amma ba'a nutse ba dan mafarkin da nayi ya tsayamin a rai sosai kwakwalwata ta kasa bani hadin Kai nayi tunani.
A haka yarana suka bar gidan
Jiki ba kwari na shiga d'akin Inna Amina.
Ido ta zuba min har na ajiye flask din kunun dasu Nadeeya suka Dama mata
Na gaisheta a madadin ta amsa min sai cewa tayi "Da kin d'aukeni tamkar Mahaifiyarki Kamar yanda kike fada da baki ringa min boye boye ba Naeema ni nasan akwai abinda kike boyemin da nake ji a jikina ba alheri bane a gareki Naeema sanin da na Miki ba haka kike ba kin kasance yarinya Mai balain hakuri da tunani duk abinda ya Sameki kina Imani cewar Allah ne ya rubuta a takardarki akan zai sameki ba mutum ba sai dai mutum ya zama sila tunda ga farkon haihuwarki har zuwa lokacin da zaki koma ga Allah Allah ya riga da ya tsara Miki rayuwarki babu dan Adam daya Isa ya canja shi
Idan Kika duba baya da Abubuwan da Suka faru dake da Imani da kikayi da Allah kin samu maganin matsalolinki batare da kin wahala ba
Amma akan abinda ya samu yaranki imaninki yayi rauni har kina tunanin sai kin je wajen wayanda muke hasashen sune silar shigar yaranki wanan halin kina nufin Allah baifi karfinsu ba sai har kinje kin rokesu su warware abinda sukayi.
Abaya su ne suke Miki maganin matsalarki?su Kika je Kika samu akan larurar Zahira?
Mai yasa bazaki dogara ga Allah ya isar Miki kamar yanda ya isar Miki a baya ba Naeema"?
Tamkar yata na d'aukeki idan Abu ya Samu bawa Allah yake gayawa ya magance Masa matsalarsa domin Allah Mai jine Mai Kuma gani duk halin da bawansa zai Shiga yana sane sai dai mu muyi gajeran hakuri kamar yanda kike yi yanzu
Karki ga muna ta ga yawa Allah har yanzu shiru wlh Yana sane zai amsa Mana a lokacin da bamu zata ba wuyanta muyi hakuri dan haka kiyi hakuri ki koma ga Allah ki cigaba da gaya Masa Yana sane dake zai amsa Miki insha Allahu.
Domin matsalarsu nayi azumin kwana bakwai da niyyar Allah ya warware duk abinda aka yiwa yaran nan ga ruwan zamzam nan kiyi kokari su biyun su Sha ki Kuma shafe musu jikinsu dashi zamu dace watarana insha Allahu"
Kuka na fashe dashi sosai dan tabbas duk abinda ta fada gaskiya ne imanina yayi rauni akan San yarana su warke.
Ni kaina nasan yanda nake dukufa da Addu'a a baya ba haka nakeyi ba yanzu.
Ina sallah Ina tunani karshe idan naga zuciyata baa nutse take ba sai na hakura da sallah.
Godiya na ringa mata a raina Ina Jin na hakura da tafiyar ba Inda zani Zan cigaba da gayawa Allah sai a lokacin tunanin Naseer ya fad'omin arai.
Har nayi tunanin ko ina yake yanzu na Kuma ringa Jin kamar ban kyauta korarsa da nayi daga gidana da bai kareni da komai bama sai asara dana tafka ta hanyar siyar da gidana
"(Duk.mafarkin hauka dinan da komai ba fiction haka tayi mafarki Allah ya tsallakar da ita)
Calabar
Safiyya
Tunda ta samu cikar burinta akan Zahira da Waleed take cikin tsananin farin ciki zuciyarta v
bata tab'a k'issa mata alheri ba sai sharri
A duk lokacin data bude ido taga hauwa yarta da ta siffantu da d'abba takan ji tsanar Naeema da duk ahalinta.
A idonta gani take ko ta samu nassarar kashe Naeema da yaranta har da Naseer da ya Zama babban makiyinta zuciyata bazata taba sanyi ba tunda duk a silarsu take Kan Shan wuya da hauwa da take Mata fatan mutuwa sabida wahala da take Sha akanta
Dakyar ta samu tayi abubuwan da tayi Bashir ya fito daga prison Wanda ta gwammaci har zamansa a can da sakinsa da akayi.
Mugun barawo ne dan d'abba mashayi.
Da cikin da ta Kara samu da baban Hauwa Bashir ke nada Mata mugun duka idan yayi shaye shayensa
Sata kuwa baa Kama hannun yaro
Halayen Bashir yasa mahafin hauwa sakinta saki uku bayan ya kwashe duka kayansa ya bar gidan
Dan kananan sanaoi da take shi ke sawa ta samu na abinci har yaranta su samu Suma da sun kawo girman da take fatan su fara samun Samarin da zasu na kashe musu kudi.
Kamar yanda taci buri akansu take fatan Yan biyun nata suyi farin jini irin na Zahira sai dai shiru.
Da tsohon cikinta Bashir ya Sha jawo mata a kulle ta dan amfana da Oban keyi da ita yasa yake siddabarun da ake sakinta.
A cikin wahala ta haihu da ita kanta batasan cikin na baban Hauwa bane ko Oban da baya iya Bata ko sisi amma duk wani Abu na mugunta Idan Tana so zai Mata akan bashi.
Rabi ta sawa yarta data haifa Dan kudaden data samo dan ta dan siyi abinci da zasu ci ita dasu Yan biyu
Haka Bashir yazo da wuka yace ta bashi.
Tana gardama ya rufeta da duka Kamar ba uwarsa ba ya dau wukarsa Mai kaifi ya tsage Mata fuska dashi..