Sashe 5
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai Amma yarinya nan Allah sai ya tsine Mata muguwa idan ba mugunta ba ai ko Dan yaranta ta bar engine dinan sabida a samu na kula dasu Amma dayake bata da mutunci shine ta siyar da engine duka biyu idan ma tayi hakane Dan mugunta ai har da yayanta ta cuta wlh dadin abin ba iya markade akeyi a gidan ba Ana kulla zobo da ruwa Kuma a siyar Nima dai ba kuturwa bace inada hannun da Zan kula ruwa da zobon na samu na kaina wlh ko kallon yaranta bazan yi ba Kai Kuma zaman gida ai Bai kamaka ba tashi zaka Yi ka fita ka nemo kudi ba kazo ka shige daka ka kwanta Kai ga uwarka ta rabu da Kai ai Zama Bai kamaka ba ya zama dole kaje ka Nemo duk inda kudi yake ka nuna Mata Kai Dan halak ne insha Allahu sai kafi da arziki tashi Maza idan wanan shegen isihun yazo Zan aikeshi yamin cafenen zobon na hada ya kaimun"
"Ko na fita Umma bazan samu ko sisi ba ko na samu ma bazai Yi albarka ba Dan kin riga da kin tsinewa samuna Umma ko mantawa kikayi kin Kona duk dukiyata ta bakin naki kudi sai yamin wahalar samu yanzu gashi ai kingani kudi Yana min wahalar samu Umma kusan wata Takwas nayi a Abuja Ina neman kudi cikin tsananin wahala Umma Wanda ma na Dan samo sai da Yan fashi suka kwace a hanya ba abinda na taba yanzu dayake albarka"
"Duk ba Kai ka jawo ba sabida tsinanen taurin.kanka zuciya ya debeni nayi abinda nayi da Nima yazo ya shafeni Dan Haka batun ma Ni na jawo duk laifinka ne na saka albarka yanzu idan Allah ya yarda zaka samu kudi ka shirya kaje ka nemi kudi"
Daga Haka ta fito tana tsinewa Naeema akan ta siyar musu da engine.
Rai a bace Haka Suka zauna a tsakar gidan suna ta kwashewa Naeema albarka Dan canjin daya musu saura tasa Safiyya ta d'auko Suka lissafa abinda zasu kashe na hadin zobon suka zauna zaman jiran Isihu sai dai har karfe Sha biyu Basu ganshi ba ahaka Hajara ta lek'a da kanta Wai ko zata hango shi Nan ma Bata gan shi ba haka ta dawo ta Kara komawa d'akin Naeema ta tarar da Naseer a zaune a Kan Sallaya Dan tunda ya iddar da walha Bai bar Kan sallaya ba carbi kawai yake ja.
"Kaga shegen almajirin Nan Bai zo ba inata jiransa tundazu ko dashi ta tafi ne"?
Alama ya Mata da hannu alamar Bai Sani ba
Hajara kuwa ranta ya b'aci tana "Kai bana San iskanci Naga duk abinda ma shegiyar matar Nan tayi ba abinda ya dameka sai Abu kake Kamar wani maraya toh tunda Bai zo ba Kai Kuma ka k'i fita ka Nemo Mana kudi sai ka tashi kaje kayo min cafenan zobo idan zuciyarka ta mutu Ni tawa ba ta mutu ba idan tafiyar Naeema ne ma yasa kake wani nonok'ewa zaka ware me dalla tashi ka siyomin zobo da suga da farin Leda"
Ta karashe tana jefa mishi kudin hannunta.
Naseer ya d'ago da rinannun idonsa Yana "Ina Safiyya Umma da Ni zanje na siyo Umma Dan banida kudi Bai Kamata na zama kamar yaro da sai yanda akayi dashi wanan ma na iya janyo min raini a wajen Safiyya Ina gaba da ita ki wuceta kizo ki aikeni haba Umma"
"Kace kawai ban Isa dakai ba Naseer ai kafita sanin unguwar Nan sai ka fita sanin Inda ake siyar da kayan zobon shiyasa na kawo maka"
"Ki Bata idan ta fita tayi tambaya zaa nuna Mata"
"Nifa bazaka zauna a gida ni Kuma na ringa fafutukar neman kudi ba Dan Haka ko bazaka siyo ba ka zura rigarka ko dakone kaje kayi Dan Idan ma takamarka Kayan abinci da ake dashi a gidanan ne kwanan Nan zai Kare wlh Nima yanzu sama na da kasana iya kudin Nan ne Dani Dan Haka nemo kudi ya kamaka"
Daga Haka ta fice daga d'akin ta bawa Safiyya kudin ta lissafa mata abinda zata siyo Mata ta karbi kudin tayi waje tana zagin isihun da Bai zo ba
Naseer kuwa Yana fitowa
Kitchen ya Shiga ya fara k'ok'arin dorawa su Zahira abincin Rana Hajara kuwa tace ya fita idan Safiyya ta dawo zata Dora musu abincin.
Naseer Bai. Ce Mata komai ba ya cigaba da abinda yake Dan wasikar da Naeema ta bashi na ya rik'e amanar yayansa ya rik'e gam akansa bazai soma barin Safiyya ko mahaifiyarsa su dafawa yaransa abinci ba.
Haka Hajara tayi ta bambamin fad'a har Safiyya ta dawo.
Dayake taliya Naseer ya Dora musu Nan da Nan ya Gama Dan akwai Miya Mai yawa a freezer din dake d'akin Naeema Dan har freezer ta siya da ta samu kudi ta daina siyan kankara.
Haka take Miya Mai yawa sai dai su dafa shinkafa ko taliya Miya tuwo ma Haka take yinshi da yawa.
Yana gamawa ya zuba wa su Hajara a kularsu ya d'auki sauran ya Kai daki Kamar yanda yaga Naeema nayi
Ya daura alwala ya fice daga gidan Hajara da Safiyya dake kula zobo da ruwa suka bishi da kallo har ya fice.
A Kular da Naeema take zuba zobo da ruwan Suka zuba
Hajara ta nufi d'akin Naeema Dan ta dauko kankara sai dai tana zuwa taga k'ofar a kulle.
Masifa ta ringa surfawa akan me Naseer zai kulle k'ofar d'akin Mai ya mayar dasune.
Haka ta koma ganin Bata San lokacin da Naseer zai dawo ba yasa ta bawa Safiyya sauran kudin hannunta ta siyo musu kankara Suka zuba Suka zauna zaman jiran Isihu da sai daya Sha tsinuwa yafi cikin kwando Hajara har da Shan alwashin wanka Masa Mari idan yazo.
Naseer kuwa Yana fita a Massallacin dake kallon gidansa yayi zamansa bayan ya iddar da sallah Yana tunanin yanda zai fara fuskantar rayuwa batare da Naeema ba Bai San Mai yasa Bai tab'a koyawa kansa rayuwa batare da ita ba a yanzu da ta tafi a lokacin da Bai tab'a tunani ba sai yaji Kamar rayuwarsa ce ta tsaya Amma ba yanda zaiyi Haka zai rungume sabon Shafin kaddarar daya bud'e Masa.
Ganin biyu tayi yasa ya fito daga Massallacin a daidai lokacin daya hango su Zahira suna Shiga gidan.
Hakane yasa yabi bayansu.
Suka Shiga gidan kusan a tare.
Daga Safiyya har Hajaran ba Wanda ya amsa Sallamar da sukayi.
"Ka ajiye Mana abinci ba Miya ka Kama kanya ka fice tare da kullo k'ofar d'akin da bansani ba ko Gwal aka saka da zaa ringa rufewa sanan name idan an gama girki zaa wani shige dashi d'aki to daga Yau wlh idan anyi abinci Kar akara Shiga dashi d'aki idan uwarsu na Shiga dashi d'aki sabida Bata yarda Dani ba Kai ma yarda ne bakayi Dani ba shiyasa kake kaiwa daki kenan toh wlh Kar a sake idan ba Haka ba sai ranka ya b'aci"
"Ke maza ajiye jakar hannunki ki je Makarantar islamiyyarku ki kiramin wanan shegen almajirin tundazu na zauna Ina jiranshi yazo.ya kaimin zobo da ruwa har yanzu Bai zo ba narasa Mai ya Hana shi zuwa ko Uwarku ce ma ta zuga shi tace.kar yazo Dan ta tafi"
Hajara tace tana hararar Zahira data yi saurin ajiye Jakarta cikin rawar jiki zata yi waje
Naseer yayi saurin rike Mata hannu Yana "Bari ta fara cire uniform din jikinta taci abinci tayi Sallah kafin ta tafi yanzu Nan ta shigo gidan fa Bari ta Dan huta"
"Iyyeee Naseer Ni nake Aiken Yarka kake hanata akan sai ta huta kafin taje kana cikin hayyacinka kuwa ko Tafiyar Naeema yasa ka fara shaye shaye toh wlh sai taje Naga idan ma aka siyar da ruwa da zobon Kai ma zaka ci a kudin Dan Haka maza wuce ki kiramin shi kafin naci ubanki"
Da mugun gudu Zahira tayi waje.
Naseer kuwa idonsa ya kad'a yayi ja shi kam zuciyarsa na Dab da bugawa sabida tashin hankali da rashin nutsuwa sosai yake Jin gidan na Masa zafi kamar ya hada kayansa ya rik'e hannun yayansa ya gudu barwa Hajara gidan
Ahaka ya rik'e hanunsu Nadeeya suka Shiga karamin Palo ya cirewa Raheema uniform ita da Humaira ya saka musu wani kayan ya zubo musu abinci suka fara ci
Nadeeya kuwa cewa take Umma Bata dawo ba?
Bai kulata ba sabida gani yake magana ma wahala yake masa.
Muryar Zahira dayaji yasa ya mik'e ya fita
"Ance Baya Nan yayi tafiya"
Zahira tace da rawar.murya
"Maganata ta fito Ni nasan dashi ta tafi Dan da safe yake zuwa gidanan nan wanan abun da tayi ya tabbatar min da ita muguwa ce ta karshe wato shima isihun bazamu more shi ba toh ai shikenan kanta ta cuta wlh Dan ke Zaki kai min ruwa da zobon bazan dau asara ba wlh maza jeki cire Kaya kici abinci kizo ki dauka yanzu yanzu ki siyarmin"
"Aaaa Umma Zahira bazata taba talla ba
ba iya ita ba insha Allahu yarana baza suyi talla ba Haba Umma ko wani Kika ji Yana cewa zai Dora wa Zahira tala ai ke Mai hanawa ne Umma karki.manta yaran Nan ba iya Naeema ce ta haifesu ba yayana ne Kuma jikokinki Dan Haka Bai Kamata kiyayar da kikewa mahaifiyarsu ya shafesu ba da Raina bazan iya Bari yarana suyi Tallah ba Umma kiyi hakuri"
Sakin Baki Hajara kawai tayi tana kallon Naseer dake ta kwara bayani
"Yau Ina ganin ikon Allah toh iskanci nace taje tayi kake zabga min wanan Bayanin Naseer daga Kai har Naeema idonku ya rufe da San Yara bakwa so moresu ko ayi musu tarbiyya Naseer Naga idan ta siyar da ruwa da zobon kananun Abubuwan da babu Zan iya d'auke maka a gidanan tunda Kai zuciyarka ta mutu ka kasa fita ka nemo tundazu nake binka akan kaje ka Nemi kudi ka kasa sanann Dan nace Zahira ta Kai Mana tallan ruwa da zobo kace bazata je ba toh wlh sai taje idan dai har ka dage bazata je ba toh wlh sai dai Kai ka dauka ka kaimin da kanka tunda Ni na Haifeka na Kuma Isa dakai"
"Ko na fita Umma bazan samu ko sisi ba ko na samu ma bazai Yi albarka ba Dan kin riga da kin tsinewa samuna Umma ko mantawa kikayi kin Kona duk dukiyata ta bakin naki kudi sai yamin wahalar samu yanzu gashi ai kingani kudi Yana min wahalar samu Umma kusan wata Takwas nayi a Abuja Ina neman kudi cikin tsananin wahala Umma Wanda ma na Dan samo sai da Yan fashi suka kwace a hanya ba abinda na taba yanzu dayake albarka"
"Duk ba Kai ka jawo ba sabida tsinanen taurin.kanka zuciya ya debeni nayi abinda nayi da Nima yazo ya shafeni Dan Haka batun ma Ni na jawo duk laifinka ne na saka albarka yanzu idan Allah ya yarda zaka samu kudi ka shirya kaje ka nemi kudi"
Daga Haka ta fito tana tsinewa Naeema akan ta siyar musu da engine.
Rai a bace Haka Suka zauna a tsakar gidan suna ta kwashewa Naeema albarka Dan canjin daya musu saura tasa Safiyya ta d'auko Suka lissafa abinda zasu kashe na hadin zobon suka zauna zaman jiran Isihu sai dai har karfe Sha biyu Basu ganshi ba ahaka Hajara ta lek'a da kanta Wai ko zata hango shi Nan ma Bata gan shi ba haka ta dawo ta Kara komawa d'akin Naeema ta tarar da Naseer a zaune a Kan Sallaya Dan tunda ya iddar da walha Bai bar Kan sallaya ba carbi kawai yake ja.
"Kaga shegen almajirin Nan Bai zo ba inata jiransa tundazu ko dashi ta tafi ne"?
Alama ya Mata da hannu alamar Bai Sani ba
Hajara kuwa ranta ya b'aci tana "Kai bana San iskanci Naga duk abinda ma shegiyar matar Nan tayi ba abinda ya dameka sai Abu kake Kamar wani maraya toh tunda Bai zo ba Kai Kuma ka k'i fita ka Nemo Mana kudi sai ka tashi kaje kayo min cafenan zobo idan zuciyarka ta mutu Ni tawa ba ta mutu ba idan tafiyar Naeema ne ma yasa kake wani nonok'ewa zaka ware me dalla tashi ka siyomin zobo da suga da farin Leda"
Ta karashe tana jefa mishi kudin hannunta.
Naseer ya d'ago da rinannun idonsa Yana "Ina Safiyya Umma da Ni zanje na siyo Umma Dan banida kudi Bai Kamata na zama kamar yaro da sai yanda akayi dashi wanan ma na iya janyo min raini a wajen Safiyya Ina gaba da ita ki wuceta kizo ki aikeni haba Umma"
"Kace kawai ban Isa dakai ba Naseer ai kafita sanin unguwar Nan sai ka fita sanin Inda ake siyar da kayan zobon shiyasa na kawo maka"
"Ki Bata idan ta fita tayi tambaya zaa nuna Mata"
"Nifa bazaka zauna a gida ni Kuma na ringa fafutukar neman kudi ba Dan Haka ko bazaka siyo ba ka zura rigarka ko dakone kaje kayi Dan Idan ma takamarka Kayan abinci da ake dashi a gidanan ne kwanan Nan zai Kare wlh Nima yanzu sama na da kasana iya kudin Nan ne Dani Dan Haka nemo kudi ya kamaka"
Daga Haka ta fice daga d'akin ta bawa Safiyya kudin ta lissafa mata abinda zata siyo Mata ta karbi kudin tayi waje tana zagin isihun da Bai zo ba
Naseer kuwa Yana fitowa
Kitchen ya Shiga ya fara k'ok'arin dorawa su Zahira abincin Rana Hajara kuwa tace ya fita idan Safiyya ta dawo zata Dora musu abincin.
Naseer Bai. Ce Mata komai ba ya cigaba da abinda yake Dan wasikar da Naeema ta bashi na ya rik'e amanar yayansa ya rik'e gam akansa bazai soma barin Safiyya ko mahaifiyarsa su dafawa yaransa abinci ba.
Haka Hajara tayi ta bambamin fad'a har Safiyya ta dawo.
Dayake taliya Naseer ya Dora musu Nan da Nan ya Gama Dan akwai Miya Mai yawa a freezer din dake d'akin Naeema Dan har freezer ta siya da ta samu kudi ta daina siyan kankara.
Haka take Miya Mai yawa sai dai su dafa shinkafa ko taliya Miya tuwo ma Haka take yinshi da yawa.
Yana gamawa ya zuba wa su Hajara a kularsu ya d'auki sauran ya Kai daki Kamar yanda yaga Naeema nayi
Ya daura alwala ya fice daga gidan Hajara da Safiyya dake kula zobo da ruwa suka bishi da kallo har ya fice.
A Kular da Naeema take zuba zobo da ruwan Suka zuba
Hajara ta nufi d'akin Naeema Dan ta dauko kankara sai dai tana zuwa taga k'ofar a kulle.
Masifa ta ringa surfawa akan me Naseer zai kulle k'ofar d'akin Mai ya mayar dasune.
Haka ta koma ganin Bata San lokacin da Naseer zai dawo ba yasa ta bawa Safiyya sauran kudin hannunta ta siyo musu kankara Suka zuba Suka zauna zaman jiran Isihu da sai daya Sha tsinuwa yafi cikin kwando Hajara har da Shan alwashin wanka Masa Mari idan yazo.
Naseer kuwa Yana fita a Massallacin dake kallon gidansa yayi zamansa bayan ya iddar da sallah Yana tunanin yanda zai fara fuskantar rayuwa batare da Naeema ba Bai San Mai yasa Bai tab'a koyawa kansa rayuwa batare da ita ba a yanzu da ta tafi a lokacin da Bai tab'a tunani ba sai yaji Kamar rayuwarsa ce ta tsaya Amma ba yanda zaiyi Haka zai rungume sabon Shafin kaddarar daya bud'e Masa.
Ganin biyu tayi yasa ya fito daga Massallacin a daidai lokacin daya hango su Zahira suna Shiga gidan.
Hakane yasa yabi bayansu.
Suka Shiga gidan kusan a tare.
Daga Safiyya har Hajaran ba Wanda ya amsa Sallamar da sukayi.
"Ka ajiye Mana abinci ba Miya ka Kama kanya ka fice tare da kullo k'ofar d'akin da bansani ba ko Gwal aka saka da zaa ringa rufewa sanan name idan an gama girki zaa wani shige dashi d'aki to daga Yau wlh idan anyi abinci Kar akara Shiga dashi d'aki idan uwarsu na Shiga dashi d'aki sabida Bata yarda Dani ba Kai ma yarda ne bakayi Dani ba shiyasa kake kaiwa daki kenan toh wlh Kar a sake idan ba Haka ba sai ranka ya b'aci"
"Ke maza ajiye jakar hannunki ki je Makarantar islamiyyarku ki kiramin wanan shegen almajirin tundazu na zauna Ina jiranshi yazo.ya kaimin zobo da ruwa har yanzu Bai zo ba narasa Mai ya Hana shi zuwa ko Uwarku ce ma ta zuga shi tace.kar yazo Dan ta tafi"
Hajara tace tana hararar Zahira data yi saurin ajiye Jakarta cikin rawar jiki zata yi waje
Naseer yayi saurin rike Mata hannu Yana "Bari ta fara cire uniform din jikinta taci abinci tayi Sallah kafin ta tafi yanzu Nan ta shigo gidan fa Bari ta Dan huta"
"Iyyeee Naseer Ni nake Aiken Yarka kake hanata akan sai ta huta kafin taje kana cikin hayyacinka kuwa ko Tafiyar Naeema yasa ka fara shaye shaye toh wlh sai taje Naga idan ma aka siyar da ruwa da zobon Kai ma zaka ci a kudin Dan Haka maza wuce ki kiramin shi kafin naci ubanki"
Da mugun gudu Zahira tayi waje.
Naseer kuwa idonsa ya kad'a yayi ja shi kam zuciyarsa na Dab da bugawa sabida tashin hankali da rashin nutsuwa sosai yake Jin gidan na Masa zafi kamar ya hada kayansa ya rik'e hannun yayansa ya gudu barwa Hajara gidan
Ahaka ya rik'e hanunsu Nadeeya suka Shiga karamin Palo ya cirewa Raheema uniform ita da Humaira ya saka musu wani kayan ya zubo musu abinci suka fara ci
Nadeeya kuwa cewa take Umma Bata dawo ba?
Bai kulata ba sabida gani yake magana ma wahala yake masa.
Muryar Zahira dayaji yasa ya mik'e ya fita
"Ance Baya Nan yayi tafiya"
Zahira tace da rawar.murya
"Maganata ta fito Ni nasan dashi ta tafi Dan da safe yake zuwa gidanan nan wanan abun da tayi ya tabbatar min da ita muguwa ce ta karshe wato shima isihun bazamu more shi ba toh ai shikenan kanta ta cuta wlh Dan ke Zaki kai min ruwa da zobon bazan dau asara ba wlh maza jeki cire Kaya kici abinci kizo ki dauka yanzu yanzu ki siyarmin"
"Aaaa Umma Zahira bazata taba talla ba
ba iya ita ba insha Allahu yarana baza suyi talla ba Haba Umma ko wani Kika ji Yana cewa zai Dora wa Zahira tala ai ke Mai hanawa ne Umma karki.manta yaran Nan ba iya Naeema ce ta haifesu ba yayana ne Kuma jikokinki Dan Haka Bai Kamata kiyayar da kikewa mahaifiyarsu ya shafesu ba da Raina bazan iya Bari yarana suyi Tallah ba Umma kiyi hakuri"
Sakin Baki Hajara kawai tayi tana kallon Naseer dake ta kwara bayani
"Yau Ina ganin ikon Allah toh iskanci nace taje tayi kake zabga min wanan Bayanin Naseer daga Kai har Naeema idonku ya rufe da San Yara bakwa so moresu ko ayi musu tarbiyya Naseer Naga idan ta siyar da ruwa da zobon kananun Abubuwan da babu Zan iya d'auke maka a gidanan tunda Kai zuciyarka ta mutu ka kasa fita ka nemo tundazu nake binka akan kaje ka Nemi kudi ka kasa sanann Dan nace Zahira ta Kai Mana tallan ruwa da zobo kace bazata je ba toh wlh sai taje idan dai har ka dage bazata je ba toh wlh sai dai Kai ka dauka ka kaimin da kanka tunda Ni na Haifeka na Kuma Isa dakai"